Showing 201001 words to 204000 words out of 223329 words

Chapter 68 - Makauniyar Kaddara Hausa Novel Complete

21 Nov 2024

1188

al'amari ka nutsu wajen kwatanta haƙuri dan zata iya yuwuwa wani tsanin zuwa ga nasara ne. Na yafe musu. ALLAH ya yafe mana baki ɗaya”.
     A take aka shiga amsawa da amin duk cikin farin ciki. Maman sadiq da batace komaiba tun zamanta a wajen, tace, “Tabbas abubuwa da yawa sun faru an maimaita wasu anan amma wasu bazasu maimaituba. Ni shaidace daga wahalhalun cikin nan da yarinyarnan tasha wanda da da ƙarar kwana ranar haihuwarsa da ta bar duniya. Amma Alhmdllh, nagodama UBANGIJIN daya rayata, ya kuma kaimu ga ganin wannan ranar tunda gata a ɗakin mijinta cikin mutinci, kuma gaskiya ta buɗe a garemu ALLAH ya wanketa tun anan dunuya. Da yaso sai ya barmu muyita kallonta da laifin har ranar tashin alƙiyama. Nima na yafe muku domin ALLAH da wasu dalilai da Gwaggo ce silarsu (Hajiya iya) ALLAH ya yafe mana baki ɗaya ya kuma kiyaye na gaba”.
      Itama godiya suka shiga mata da amsawa da amin. Kafin Hajiya iya ta fara magana.
    “Tabbas dolene nima nace a yafemin ɗin bisa wani dalili, dan ƙila daban matsama Moddibo da ƙara aure ba da tunaninsu bai karkata ga hakan ba. Ni kuma ba komaine ya sani damuwarba sai ganin yanda matarsa bata ɗaukemi da darajaba. Hakama Hindatu. dan duk da Kabeer ya fita ƙarfin faɗa aji akan yarannan tana nuna masa iko a kansu, ko zancen auren yarinyarnan bamusan komai ba saida yazo gab. Koda yake duk ta wani tone-tone ya wuce, Moddibo ka yafemin kai da matarka dan zan iya saka kaina matsayin silar faruwar komai”.
        “Bake bace sila Granny, dan koda kikace na ƙara aure baki tursasaniba, sannan tsarin da sukazo muku dashi ya sakaki wannan tunanin kema. Dan haka nikam kima daina neman gafarata bakimin komaiba why”. AK ne ya faɗa cikin dauriyar abinda yakeji game da jikinsa.
       Mammah ta karɓe da faɗin, “Tabbar Inna ba laifinki bane, nice da wannan laifin, dan daban zurfafa da yawaba akan yaran nan da Zakiyya bataci galaba a kainaba har nakai ga bata goyon bayaba, dan ALLAH Adnan ka yafe min kaji, ajizancine na ɗan adam da son zuciya da tsoron rasaku tamkar yanda gangancina ya kaini ga rasa kabeer. Kishi ba hauka bane, kuma halas ne. Amma irin namu yayi muni da yawa dan muna zafafawa, da nayi haƙuri da hukuncinsa a wancan lokacin da duk haka bata faruba na tabbata. Dan ALLAH ku gafarceni baki ɗaya. Ɗiyata Zinneerah kema dan ALLAH ki yafemin kinji, wlhy bazan ɓoye mukuba tun randa na diro ƙasarnan naga yaron nan da kika haifa ƙaunarki data yaron ta kamani, duk abinda kukaga inayi borin kunyane kawai, amma har cikin raina son ɗanki dake kanki ya shigeni, koda nake cewa kar Adnan ya taɓaki ya sakeki inason na gwada yanda yake sonkine kawai ba wani abuba, kuma koda ya gama tsarani bawai ban fahimci tsaranin yayba. Sarai na san bazai iya sakinkiba wlhy, nima kuma bama zan yarda yay wannan taɓargazarba. Ki yafemin na ƙara roƙonki......”
     Da sauri Zinneerah ta shiga girgiza mata kai, “Mammah dan ALLAH ki daina roƙona. Wlhy ni bakimin komaiba sai tarin alkairi kodan zama mahaifiya ga Yayanmu da kikayi. Kuma ni kallon uwa nake miki daman, har abada kuma zan cigaba da kallonki da wannan kimar da darajar. Dan haka ki ɗauka bakimin komaiba. Idanma kinmin na yafe miki wlhy”.
     Tasowa Mammah tayi ta rungume zinneerah tana saka mata albarka. Kamar yanda zancen nata ya saka kowa dake falon murmushi, duk da ƙarancin shekarunta ALLAH ya bata baiwar shirya lafuza masu taushi ga nagaba da ita duk da kuwa ko ba'a faɗa da gaske an tauye mata haƙinta.
       Farah da Zakiyya dai babu wanda ya roƙa gafarar Zinneerah, babu kuma wanda yace dasu ƙala akan hakan, kai kowama basu roƙaba sai kuka da sukeyi kawai. Dan haka mai martaba ya umarci AK da mijin Aunty Zakiyya da shima yana a wajen akan su basu saki. Babu wanda yace komai a falon, sai AK ne ya miƙa hannu ya amshi takarda da biro daga hanun Baba Wambai. Haka shima mijin aunty Zakiyya.
     Gani kawai sukai Zinneerah ta tashi da sauri taje gaban AK ta durƙusa. Biron daya dasa akan takardar ta riƙe da fashe masa da kuka tana girgiza kai. Jajayen idanunsa ya ɗago yana kallonta. “Yayanmu dan ALLAH karka aikata, na roƙeka karka saketa. Kuma koba hakaba ka tausaya mata ba laifinta bane itama tursata akayi”. Tai saurin juyawa ga mai martaba dake mata kallon mamaki hakama sauran jama'ar falon. “Abbah dan girmana ALLAH kayi haƙuri ka janye wannan hukuncin naka koda kuwa sauran zasu tabbata. Gara komi za'a musu ai musu da igiyar aurensu kar'a rabasu da iyalansu na roƙeka Abbah. Dan ALLAH kodan maraicinsu ai musu afuwa, wlhy na tsani naga an saki mace inajin ciwo. Granny, Baffah, Mahma, Babana dan ALLAH kusa baki, Abba dan ALLAH ku bama Abbah haƙuri dasu Yayanmu karsu aikata”.
        Yanda take kuka kamar ranta zai fita sai duk hankulansu suka tashi. Dan har suƙewa takeyi, ƙoƙarin son fisge pen ɗin AK yayi yana harararta ta sake damƙesa da fashe masa da kuka. “Yayanmu dan ALLAH, kodan ƙyautar little da ALLAH ya azurtaka da shi ka taimaka karkayi, idan ka saketa ALLAH nima bazan zauna da kai ba, zan ɗauke little na tafi inda bazaka sake ganinmuba wlhy”.
        Kansa dake sara masa ya dafe, da wannan damar ta samu amshe takardar da biron, ta koma gaban Mai martaba ta gurfana tana cigaba da roƙonsa shi da su baba wambai da su waziri. Sosai ta basu tausayi ta kuma sake birge kowa. dan haka hajiya iya tai ɗan murmushi da duban mai martaba ɗin da shi kansa yakejin wani irin ƙaunar Zinneerah na shigarsa. Dan koda ƴaƴansa suka kasance masu laifi bazaiso mutuwar aurensuba ai. Sai dai kuma dolene ya yanke musu hukunci domin yin gargaɗi.
        “Inaga a amsa kukan Zinneerah dan ALLAH, za'a iyama su Farah hukunci bawai sai an katsa igiyoyin aurensu ba, dan koda abinda duk ya faru aka barsu ya ishesu tunawa da ishara har ƙarshen rayuwa. Ayi haƙuri dan ALLAH”.
     Ƙasa kawai mai martaba yayi da kansa dan yana ganin girman tsohuwar ainun, yanda yayi ɗin ne ya saka sauran ƴan falonma fara roƙonsa harma dasu AK kansu. Ganin sun masa taron dangi ya sashi jan numfashi da dafa kan Zinneerah ya shiga jera mata addu'oi masu daraja da ake jifan mutum mai daraja dasu. Sai da ya gama ana amsawa da amin sannan yace, “Shikenan zan janye maganar saki, amma kuma dolene sai sunje masarauta sunyi wancan zaman wlhy, sauran hukuncin kuma tsakanina da sune. ALLAH yay miki albarka ke kuma, daga yau kema kin zama cikin jerin ƴaƴana”.
      Kabbara aka ɗauka a take. Kowa na nuna jin daɗinsa da farin ciki. Daga haka Hajiya iya tai musu nasiha. Hakama baba wambai yayi musu sannan shima maimartaba ya ɗaura tashi, daga ƙarshe aka rufe taro da addu'a saboda lokacin sallar zuhur yayi.

★★★

     Ana idar da sallar azhar aka gabatar da ɗaurin auren Huzaifa da Adilah bisa alƙawarin Baffah, dan dama sun gama magana da mahaifin Huzaifa tun daren jiya, ya kumace ya bashi wuƙa da nama dan zaman Huzaifa hakan ya ishesa dama. Shima dan baya Nigeria ne da dashi za'ai komai a yau.
   Koda suka dawo cikin gida tuni labari yaje kunen kowa. Zokaga murna wajen ango da amarya dan dama sun folama juna tuni. Daga haka sukai zaman cin abincin da matan Baffah suka shirya musu, suka kuma sake tattaunawa a tsakaninsu na maza. Kamar yanda anan cikin gida suma su Granny basu gaji da sake tattauna zantukanba a tsakaninsu. Mahma taja su Zakiyya gefe tana musu faɗa akan ƙin neman gafarar kowa da sukayi. Ta zazzagesu tas tai gaba ta barsu batare da kowa ya sani ba.
      AK kam bayajin daɗin jikinsa, dauriya kawai yakeyi, hakama Zinneerah tana gadon Granny ƙudunsune dan zazzaɓi na neman dawo mata sabo ga ciwon kai na kukan data sha. Tanason zuwa ta gaisa da Baba ma ta kasa.

   Zuwa la'asar su maimartaba suka fara tafiya bayan ya tasa su Farah dake faman kuka gaba ya wuce dasu masarauta, harda Baba dan yanason ya shiga har ƙauyen Danya yayma baba rakkiya ya kuma gana da dagacin garin danya ta silar baba. Hakan yama Zinneerah data fito suka gaisa da ƙyar daɗi, yau ga babanta ga maimartaba wata hikima sai UBANGIJI. Shima kansa AK hakan da maimartaba yayi ya masa daɗi sosai.
    Bayan wucewarsu suma su mmn sadiq suka wuce, suma hajji Lanti tafiya sukai bayan sun sake gurfana neman gafara ga Zinneerah da AK dama su Hajiya iya baki ɗaya.
        Da wannan damar Mammah ta samu suka sake zama ita da Mahma dasu Baffah ta ƙara neman gafararsu da sake tattauna duk abinda ya faru. AK dai bai zaunaba ɗakinsa ma ya shige yay kwanciyarsa dan bayajin daɗi, ya tabbatar yau jininsa yayi ƙololuwar hawa tabbas.
     Hajiya iya ce ta hana su Mammah komawa gidan mijin Zakiyya. Tace Khalipha zaije ya ɗakko musu kayansu suyi zamansu anan har randa za'aje ga yarinyar datake rainon cikin a Morocco.
    Zinneerah ma dai magani Granny ta bata tasha ta kwanta.

________________________

      *_DANYA_*

  Su baba sun iso danya da tawagar maimartaba. Inda tsabar ruɗewar da maigari yayi kai kace zai kife ƙasa. Maimartaba da kansa yau a ƙauyensa, bayan ko'a labari bai taɓa jin ko kusada wajen hakimi yaje ba sai dai ya aiko wakili idanma wani abune ya taso. Ai baima san ya gurfana yana kwasar gaisuwa ba. Hakama garin danya cikin ƙanƙanin lokaci labarin zuwan maimartaba da baba a tare ya shiga kunnen kowa harsu Inna da ke kwance rijib cikin ciwo. Dan tun zancen cikin Tinene dajin uwar sata da Karima ta kima na sarƙar zinarin wata hajiya da har yay silar Babawo yimata dukan mutuwa ya korota gida ta yanke jiki ta faɗi aketa fama har yanzun. Dan saki uku Babawo yayma Karima. Ga kuma aike daga kotu cewar Karima zata biya naira dubu ɗari huɗu na sarƙar mata bayan tara kuma da zaman kaso na wata shidda bayan ta yaye ɗiyarta. Ga zancen cikin Tinene ya baje ko ina na garin danya da kewaye har ƴammata sun dasa mata waƙar dandali. Matan aure kuwa da biyu suke zuwa barkar ƴan biyun amaryar baba dansu sake tabbatar da zancen ciki da halin da Inna ke ciki na samun ciwon ɓarin jiki a silar faɗuwar da tayi.
       Ga ƴan uwan amaryar baba sun cika gida daga jiya zuwa yau dan ana haihuwa baba ya kirasu ya sanar musu. A safiyar jiya saiga kusan mutane shidda sunzo, sauran kuwa sai daren suna. Duk abinda ke faruwa kuwa akan idonsune sai mamaki sukeyi kamar almara ko hikayoyin marubuta.
        
     Cikin ƙanƙanin lokaci ƙofar gidan maigari ya cika taf da jama'ar gari saboda kiranye da aka saka sanƙira yayi musu. Ciki kuwa har dasu Sa'a a ƴan kallon zuwa ganin maimartaba. Sai da guri ya nutsa sannan maimartaba ya fito. A take waje ya ruɗe yau gasu ga maimartaba. Farin ciki duk ya bayyana a fuskokinsu kamar shima yanda yaji daɗin yanda suka amshesa duk da basu da wani cigaban kirki a garin, zaima iya cewa baisan da zamansuba saita wannan silar. Sai yaji zuciyarsa ta ƙara rauni da karaya akan nauyin al'umma dake kansa.
          Bayan Matawalle ya isar da saƙon gaisuwar sarki a garesu ya gabatar da hajji lanti a gabansu tai bayani akan silar ɗaukar Zinneerah zuwa birnin katsina. Itama Hajiya Haule tayi bayani kamar yanda tayi a kano. Kafin Zakiyya ma da takejin tamjar ranta zai fashe tai nata bayanin akan gaskiyar dasama Zinneerah ciki da sukai ba ta hanyar iskanci ta samosa ba.
        Take gurin ya ƙara ruɗewa da al'ajab da mamaki. Ɗunbin tausayi da nadamar cin kashin da suka dinga ma yarinya ya ringa dawo musu a rai harda masu kuka. Kafin wani dogon lokaci labari ya ƙara kaiwa ga mata dake cikin gida da jama'ar sauran ƙauyukan gefensu da duk sukasan da labarin cikin na Zinneerah. Abinka kuma da ƙananun gari babu wanda ya manta musamman daya kasance ba'a jima da zuwa akai bikin Zinneerah ɗin ba. Bakajin komai sai ALLAH wadarai ga Inna asabe dasu Zakiyya. Dan su maimartaba kan sun tafi sunbar abin faɗa ga mutane. Musamman daya kasance yanzu ALLAH ya bama Zinneerah cigaban rayuwa. Ga kuma samakon nan a jikin Tinene da ita kanta Innar dake kwance rijif ita ba gawaba ba kuma rayayya ba.
     Ita kanta da labarin yaje mata sai gata tana hawaye zuciyarta na ƙara hauhawar zafi. Daga ƙarshe jikintane ya ruɗe sai da aka kwasheta zuwa asibitin cikin kusada..............✍       

*_TYPING📲_*


*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

_________________________


*Page 65*

............Ganin dare ya fara yasa Hajiya Iya tada Zinneerah, shima AK taje ta tasoshi akan suzo su wuce gida haka nan. Badan Zinneerah taso hakanba ta miƙe, shima AK ɗin ya fito yana faman dafe kai. Kowa bai kallaba a falon yay ficewarsa duk da yasan akwai su Mammah zaune. A waje ya samu su Haneef da little a hannu, aiko ya maƙale masa. Amsarsa yay suka shiga motar da Khalipha zai jasu dan shi bazai iya tuƙinba. Zinneerah ma da Hajiya iya ta rakota dasu Meenal ta shiga baya.
           
         Koda suka iso Khalipha ne ya buɗe musu ƙofar falon, daga haka ya juya yana musu sai da safe. AK ya ɗauka Little suka wuce sashensa batare daya kula Zinneerah ba. Itama ɗin ba kulashi taiba ta shige nata sashen. (Faɗan masoya hutu😂😝).
        Ko wanka kasa zamanyi Zinneerah tayi, tana shiga gado ta faɗa tai kwanciyarta dan barcin tafi bukata. Musamman daya kasance maganin da Granny ta bata yana saka barci.
    Shima a ɓangaren AK kwantar da little dayay barci tun a mota yayi, ya samu yaɗan watsa ruwan yasha tea dan yanajin yunwa, duk yinin yau ya gagara sakama cikinsa abinci, basket ɗin abincin da suka bari a gidan tunna safe ya ɗauka ya bubbuɗe. jin babu abinda abincin yayi ya sashi ɗauka ya fita dashi ya kaima maigadi yace ya badashi kar ai asararsa. Daga haka ya dawo shima yay kwanciyarsa bayan yaɗan leƙa Zinneerah yaga harma ta kwanta.

*_WASHE GARI_*

      Da safe sun tashi Alhmdllh, musamman Zinneerah batajin ciwon komai a jikinta. garama AK dai jikin nasa sam baya masa daɗi. dan ko sallar asuba a gida yayi abunsa ya koma ya kwanta. Sai kusan ƙarfe bakwai da little ya farka yana damunsa ya miƙe da ƙyar ya ɗakkosa gaba ɗaya yayo sashen Zinneerah da shi. A lokacin tana cikin saka turaren wuta dan ta gama gyaran ko ina.
      Sanye take cikin wando da riga na kayan barci farare tas, yanda suke da santsi yasa suka manne mata a jiki sosai, gashi ko bra babu a jikinta. Kallo ɗaya yay mata ya kauda idanunsa, itama cike dajin kunyar yanda ya sameta dan batai zaton shigowarsaba takai ƙasa tana gaidashi cikin girmamawa batare da ta yarda sun haɗa ido ba.
     Amsa mata yay a daƙile yana dire little kusa da ita dan haushinta yakeji, har itace zata buɗe baki tace zata barsa saboda wasu. Wannan magana tai masa ciwo, tanama cikin masa ciwon. Juyawarsa yay ya fice ta bishi da kallo zuciyarta na raya mata yana fushine saboda matarsa da aka wuce da ita. Haka kawai sai taji ranta ya sosu. Ta ɗan taɓe baki tana miƙewa da ɗaukar little ɗin dake mata ƙorafin shi tea zaisha.
      “Dalla yima mutane shiru abinda ka iya kenan sai cin tsiya kamar ubanka”.
        Kuka ya sanya mata saboda dungure kansa da tayi. “Malam yimin shiru ALLAH kona huce a kanka”. Daga haka ta ɗaukesa suka nufi ciki dan ta masa wanka sannan tazo tanadar musu abinda zasuci dan tacema Granny abar kawo musu abinci zata fara girki.

       Wanka tayi masa itama tayi sannan, tura little tayi wajen AK ya amso kayansa, ita kuma tai ƙoƙarin shiryawa a gurguje ta fito. Sai da ta haɗa ma little tea ta fara nema musu abinda zasuci yanda bazata takura ba. Harta gama bataji ɗuriyar little mai kukan yunwaba, hakan bai dametaba dan tasan wani abun ya samu acan.
      Kamarko ta sani dan AK na gama saka masa kaya tea ɗin ya haɗa masa da ruwan dispencer, ya haɗa masa da biscuits. Shima wankan yayi dan yanason yaje asibiti kar abin yay masa nisa. Koda ya fito wankan rashin ƙarfin jikin ya sakashi sake komawa ya kwanta har takai barcin ya sake figarsa.
       Lokacin da Zinneerah ta shigo falon da kayan abincin little kawai ta samu a falon ya barbaza filos ɗin kujera yayma falon kaca-kaca. “ALLAH ya shiryeka” kawai ta iya cewa ta ajiye abincin a dining. Kayan shara ta ɗakko ta fara a tunaninta AK yana wani abunne a ciki. Waje ɗaya ta saka little zama harta kammala kimtsa falon tasa turare. Ganin har lokacin shiru babu motsin dadynsa ga goma harta gota ya sata nufar bedroom ɗin a ɗarare danta sanar masa ga abinci. Kusan sau uku tai sallama babu amsa. hakan ya sata tura ƙofar ta ɗan leƙa kanta a tunaninta koma dai baya gidan ne.
       Zaune ta hangosa a bakin gado dan dai-dai ya tashi kenan saboda sallamarta. Hannunsa dafe da kansa dake masa tsananin ciwo. Jitai tamkar ta juya da baya dan da ga shi sai boxer ne, amma ganin yanda ya dafe kansa yasata tunanin ba lafiya ba. tunda jiya dai ga a yanda suka dawo su duka, kuma tanaji sanda yake sanarma Khalipha kansa na masa ciwo a jiyan.
     

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login