Showing 183001 words to 186000 words out of 223329 words

Chapter 62 - Makauniyar Kaddara Hausa Novel Complete

21 Nov 2024

1208


    Kasancewar dama Haneef na tare da Mahma da  Gwaggo Maryama da duk hankalinsu ke tashe da wannan kira na AK ɗin sai ya matsa musu alamar su shiga. Shi kuma ya juya.
      
        Cikin girmamawa AK yay zaman gaishesu su duka. Cikin rashin haƙuri Hajiya Iya tace, “Mukam dai duk ka tada hankalinmu Moddibo, mike faruwa ne? Ina Inno kuma?”.
        Ɗan dubanta AK yay yana maida kansa gefe da faɗin, “Ku kwantar da hankalinku ba wani abu bane, na saku zuwa nanne domin ku zama na farko dazan fara tabbatarmawa kafin kowama ya sani”.
        Hajiya iya dake cikin jimamai tace, “To muna saurarenka, ALLAH ya jishemu alkairi”.
    Da amin Mahma da Gwaggo Maryama suka amsa. AK ya gyara zamansa kansa a ƙasa dan nauyin maganar da zaiyi. “Kuyi haƙuri duk da ba magana bace wadda ya kamata kusani, amma saboda wasu dalilai naga ya dace ku sani ku kuma zama hujja akan binciken da zan ƙarasa. Mu dukanmu nan munsan cewar Zinneerah ta haihu a shekarun baya, kuma koda yaushe maganarta shine batasan a inda ta samo ciki ba. Wasu kan ɗauketa mara hankali, wasu na ganin tana wasa da hankalin mutanene kawai ko rainin wayo da makamantan haka. Wasu kuma kan mata uziri da cewar ƙaddara ce ta afka mata. Tabbas ƙaddara ce, da a zahirance zamu iya kiranta *_MAKAUNIYAR ƘADDARA_*. ALLAH shine shaidata ban taɓa taɓa ƴar kowa ba da nufin fasiƙanci. hakkane ya tada hankalina matuƙa akan Zinneerah har takai bana iya barci, a ƴan kwanakin nan gaba ɗaya cikin shan maganin hawan jini nake saboda tashin hankali da tunanin ta hanyar da aka samar da Abdul-Mutallab, sai da Granny ta kawo wani zance da Khalipha yayi akan dashen ciki sannan ALLAH ya haskamin hanya. A dalilin haka na cigaba da bibiyar abubuwa da dama a ɓoye batare da sanin kowaba, har ALLAH ya tabbatar a yau nakai gaɓar da nine na farko da zan fara tabbatarma duniya lallai dashen cikin Abdul-Mutallab akaima Zinneerah bata hanyar banza ta samoshi ba. Dan bata taɓa tarayya da namiji ba sai daren jiya. Inaji a raina ALLAH ya keɓance tane daga haihuwa da kanta sai cs akai mata domin irin wannan ranar dazai wanketa ga kowa”.
       Kallon kallo aka shigayi tsakani Mahma da Granny da Gwaggo Maryama, shi dai AK tunda ya fara bayaninsa harya ƙare bai yarda ya kallesu ba idanunsa a ƙasa.
      Cikin karfin hali Mahma ta katse tararrabin su ta hanyar kallon AK da faɗin, “Abdul-Mutallab ka sakamu a duhu nikam, kenan tayaya aka dasama baiwar ALLAH nan gudan jininka?”.
       “Wannan ne nakeson sani yanzun, amma Mahma kiyi haƙuri, inaga wannan abin ba kowa bane ya ƙullasa sai Zakiyya, Farah da Mammah, dan naji wasu zantuka nasu da suka rikitani jiya da rana sanda nazo gidan nan, to kafin na shigo na fara samunsu a garden ne amma su basu san na jiba. Sannan idan kin lura duk sanda akai maganar dashen cikin nan sai sun razana. Dalilina na biyu Dr Mahmud ya tabbatar min shi baiga wani alamun mai ciki tattare da Farah ba. Sannan ni kaina idan zanyi aiki da hankalina ai ciki girma yakeyi a jikin mace, amma ace kusan 5months babu wani alamarsa a jikin Farah. Idan baki mantaba cikin farko data samu tun yana wata uku suka matsa sai da ta tafi Morocco, bata dawo London ba sai da tai ɓari kamar yanda suka faɗa. To wannan ma a ƙiyasina tun yana wattani ukun ta shiga damuna zataje, amma zuwan danai da Granny ya sani taka mata birki. Hujja ta biyu a labarin da Zinneerah ta bamu na zuwanta katsina aikatau yayi kama da wadda aka yaudara saboda ƙuruciyarta, bayan an cutar da itane ta gudo batare da saninsu ba. Abinda kawai ban fahimtaba anan shine Mammah tasan hakan kokuwa ita Zakiyya da Farah ne kawai suka sani ko itama Farah bata sani ba? Hujjata ta ƙarshe samun Zinneerah da martabarta ta ƴa mace”.
      “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un” Mahma dasu Granny keta ambata, hawaye suka shiga sakkoma Mahma, tasa hannu ta sharesu da faɗin, “Lallai biri zai iyayin kama da mutum Abdul-Mutallab, dan nima kaina ina mamakin rashin tasawar cikin Farah. Sannan akwai wasu abubuwa na rashin gaskiya da zakaga suna shan aikatawa a wani lokaci kuma, lokacin cikin farko na taɓajin wata wayarta da Adilah lokacin tana hostel a makaranta, sai dai ina shiga ta yanke wayar. Indai kuwa hakane sun cutar da yarinyar nan matuƙa, sun ɓata mata suna, sun sakata wahala da ƙarancin shekaru. Wane irin son zuciya ne wannan? Kai kanka damu sun cutar ai”.
    Ta kare maganar tana kuka sosai. Gwaggo Maryama ma hawaye takeyi, Granny dai idanunta sunyi matuƙar yin jajur alamar shiga ƙololuwar ɓacin rai. taja numfashi mai zafi da faɗin, “Lallai kayi haƙuri Moddibo, idan har ta kasance wannan zancen ya zama gaskiya sai nayi shari'a da uwarka da matarka. Dan wlhy sai na bima inno kadin haƙƙinta. Yanzu abinda nakeso da kai kar kai musu maganar komai, kuma tabbas inaga Zakiyya itace hajiyar da aka kai Inno gidanta. To karka yarda su haɗu anan gidan yanzun, dan idan suka gane itace zasu iya bin wata hanyar suga sun rufe asirinsu. Abinda nakeso dakai yanzu daganan zuwa safiyar gobe idan ALLAH ya kaimu ka aika hukuma a kama matar data kai Zinneerah aikatau katsina, itace zata kaimu ga hajiyar farko, ita kuma ta kaimu wajen wadda Zinneerah ta faɗa mana tata jerangiya da ita asibiti, na tabbatar zamu kamo bakin zaren insha ALLAHU.”
         Duk da kalaman cewar sai tayi shari'a dasu Mammah ya bashi tsoro dan yasan Granny akan tsayawa wanda aka zalinta hakan bai hanashi ɗaga mata kai ba cikin girmamawa yace, “An gama insha ALLAH, dan yanzu hakama zancen da nake miki tana police station tare da Khalipha. Tun da safe yaje Dayan akanta, ya tatar tana katsina, shine ya zarce can har inda take bisa taimakon wani bawan ALLAH ɗan nan Danya ɗin. Dan da nace a fara kamamin matar baba sai Khalipha ya bani haƙuri akan a barta kodan darajarsa dan yama tarar itama bata da lafiya. Mu kama matar dai kawai tunda ta hanyartane kawai za'a iya bin diddigin abun”.
       Mahma tace, “Alhmdllh hakan da kukai shine dai-dai, yanzu yaya akai mi matar tace?”.
     “Mahma ba'akai ga tambayarta komai ba, dan inaga ko mintuna goma basuyi da isowaba ma, ina gama waya daku ya kirani yake sanarmin ya dawo harda matarma tana station yanzu haka”.
         Gwaggo Maryama dai ta kasa tofa komai, sai hawaye taketa faman zirararwa. Hajiya iya tace, “Kabeer ya san duk wannan?”.
      “A'a ban faɗa masa ba”.
“To ya kamata ya sani dagashi har Ahmad da Abubakar (Abba mijin maman sadiq) da baban ita Zinneerah, dan babbar maganace wannan data wuce yinta iya mu kaɗai”.
       “Babu damuwa Granny, dama ai dole zasu sani, dama munason mu kammala gano inda mutanen suke tukkuna sai na sanar dasu. Amma tunda kinga ya dace su sani tun yanzu shikenan”.
         Mammah ta buɗe baki zatai magana kenan sai ga Zinneerah ta fito tana tafiya a hankali batare da tasan da zamansu a falonba. Ita cama take AK ɗin baya gidan, dan tun ɗazu ta tashi, cikin ƙarfin hali ta gyara masa ɗakin da wanke toilet, yanzuma ta fito ɗaukar kayan sharane.
       Tun fitowarta ƙamshin turarenta ya isar masa hanci, dan haka ya waiwayo domin tabbatarwa. sai dai yayi dai-dai da suma duk suka ganta ɗin.
     Sai dai babu wanda ya iya cewa komai a cikinsu harta iso kusan tsakkiyar falon, turus taja ta tsaya gabanta na faɗuwa ganin yanda suke mata kallon ƙurulla su duka. Sai duk ta daburce dan gani take kamar duk sun san miya faru da ita a daren jiya. Da sauri ta juya zata koma inda ta fito Hajiya Iya tace, “Inno ba gaisuwa?”.
      Matse idanunta tai da cije lips ɗinta waje guda tamkar zata nutse dan kunya. Musamman daya kasance cike da tsokana hajiya iya tai maganar.
      AK dake binta da kallo ƙasa-ƙasa yace, “Granny ke baki iya gani ki ƙyale?”.
         Dariya duk suka ɗanyi, dai-dai Zinneerah na isowa inda suken kanta a ƙasa. Can jikin kujera ta lafe tana gaishesu, saika rantse wasu baƙin tane da bata saniba ko take matuƙar jin kunyar haɗuwa dasu. Yanda tayi ɗin ya bama AK dariya matuƙa amma ya gimtse baiyiba.
      “Oh kajimin ja'ira wa kikema wannan lafe-lafen anan to? Koda yake sai dai idan surukarki Zaliha”. hajiya iya ta faɗa tana nuna Mahma dake kallon Zinneerah ɗin da murmushi a fuskarta tanajin tausayi da ƙaunar yarinyar har cikin bargonta. Itace ta tashi tsam ta kamo hannun Zinneerah data kasa tasowa duk da maganar da Granny tayi.
      “Haba ɗiyata minene najin kunya, mufa nan duk iyayenki ne, ga kuma kaka nan. ALLAH yay miki albarka kinji, ya sakanka miki da alkairi mai yawa ta inda bakiyi zatoba. ALLAH ya tsare gabanki da bayanki ya ƙara ɗaga darajarki a wajen mijinki”.
      Babu kunya AK yabi sahun ƴan amsawa da amin, sai dai shi a saman laɓɓa yayi saɓanin su hajiya iya da sukai a fili. Ita dai Zinneerah ta kasa kallonsu koda sau ɗaya dan jitake kamar ƙasa ta tsage ta shige ciki. Dama kuma ga miskilanci data ƙware kuma ta haddace duk da bataima Hajiya iya yau dai itama ta shafeta kam.
     Duk yanda sukaso ta sake hakan ya gagara, hakan yasa hajiya iya cewar, “Tunda yanzu baƙya yayina Inno tashi kije abinki, ai gobema rana ce”.
     Tsam ta mike a tunaninsu tafiyar zatai, sai sukaga ta nufi hajiya iya. Tana zuwa a jiki ta faɗa mata hawaye na gangaro mata.
      “Oh ashe moddibo ne ya fara koya miki gulmarsa ta basarwa kina yina”. Hajiya iya ta faɗa tana shafa kan Zinneerah ranta fes da so da kaunarta data kara ninkuwa a ranta, ga ɗunbin tausayinta kuma.
    Albarka suka dinga saka mata AK na tayata da amsawa. Daga ƙarshe hajiya iya ta sata sake basu labarin abinda ya faru a zuwanta katsina. Suka kuma dora mata da ƴan tambayoyin abinda ya shige musu duhu musamman Mahma da hausar tata ba cika yay ba.
         Sallamar Zinneerah sukai su kuma suka cigaba da tattarawa, da wannan damar ta samu kuɓuta ta koma ɗakinsa. Barin batun shara tai ta shige toilet tai wanka da sake gasa jikinta da ƙyau, yunwa takeji sosai ga jikinta da takeji fayau, sai bakinta dake ɗaci amma babu zazzaɓin. Sai dai illahirin gaɓɓanta babu inda baya mata ciwo. Taji daɗin ruwan zafin sosai. Dan sai da ta tabbatar ko wace gaɓa tata ta gamsu kafin tai wanka ta fito ɗaure da towel ɗinsa daya tsaya mata iya cinya. Batai tunanin samunsa a ɗakinba tunda tasan yana tare da baƙi, sai dai kuma tana fitowa tai turus saboda cin karo datai dashi zaune a bakin gado yana waya.
       Da baya-baya ta dinga jan ƙafarta zata koma AK ya miƙe yana binta da wani shu'umin kallo daya nema harmutsa hanjin cikinta dan tsoro, dan ita dai harga ALLAH wani irin tsoronsane ya sake tasiri a ranta bayan matsananciyar kunyarsa da bata taɓa ji ga wani ba. Ganin ya taso ɗin ya sata kara sauri, sai dai babu nasara dan taku baifi huɗu yayba ya cafkota. Gaba ɗayanta ya jawo jikinsa yana faɗin, “Okay Baffah sai nazo gidan zuwa anjima ɗin”.
    Daga haka ya ajiye wayar a ƴar drawer ɗin wajen da suke gab da ita.
       “Anya wannan jikan na Granny zatai jarumta?”.
    Ya faɗa cikin wani irin kasalalliyar murya dai-dai yana sa kansa a wuyanta. Duk da wanka tayo hakan bai hana tasirin fitar kamshin mayun khurah ɗinta ba. Ya ƙara tura hancinsa cikin wuyan duk da laimar ruwan dake naso a jikinta. Tare da zagayo duka hannayensa akan cikinta.
      Cikin rawar murya kamar mai shirin fasa kuka tace, “Yayanmu su Granny”.
         “Su Granny mi? Ba suna falo ba muko muna nan abunmu a ɗakin sirrinmu”.
         “Amma zasu ce.....”
Ta kasa ƙarawa saboda nauyin maganar.
       Yana cigaba da shin-shinar wuyan nata dake tada mata tsigar jiki yace, “Zasuce ina lalube amaryana?. To ai suma sunsan tunda suka bani komaima zanyi baby girl”.
       Zinneerah da kunya ke neman kasheta da mamakinsa, tai saurin cewa “Nifa ba hakaba Yayanmu”.
      “To yaya ne?”. Ya faɗa yana ɗagowa da birkitota suna fuskantar juna. Kafafu ta shiga matsewa saboda kunyar cinyoyinta dake waje. Yanda take ɗinne ya sashi kallon cinyoyin, idanu ya ɗan lumshe da sake buɗesu a kansu, kafin ya cije lip ɗinsa muryarsa na canja amo yace, “Karfa kisa nai miki wani sabon aika-aikan ALLAH. Muje ki shirya ga abinci har 2 tana neman yi. Kinyi salla ko?”.
          Kanta a ƙasa ta daga masa kawai.
      “Magana da baki”.
Dole ta buɗe baki tace, “Eh nayi tunma dana tashi naga lokaci yayi”.
     “Good. kije ki shirya to, ko na shiryaki ne?”.
       Babu shiri ta waro masa idanunta da har yau ke a ɗan kumbure. Shima waro mata nasa yayi sosai. Hakan sai ya sata jin kunya tai saurin saka tafukan hannaunta ta rufe fuska murmushi na suɓuce mata.
        Wannan salon nata na nuna yawan jin kunya na kayatar dashi, dan haka ya rungumeta gaba ɗaya a jikinsa yana faɗin, “Ina son wannan salon naki baby. Da gaske fa kina neman shigama Farah hanci, idan kuma ta tashi fyatoki zakiji jiki”.
     Gaban Zinneerah ne ya faɗi dan itakam sai an amfaci sunan aunty Farah take tunawa da ita, tare da tuna cewa Yay Abdull-Mutallab bafa nata bane ita kaɗai, akwai wadda ta fita tsananin sonsa da kishinsa, komai kuma zata iya aikatawa akansa. lallai tana cikin lukutin yanayi duk randa aunty Farah tazo Nigeria (dan itafa batasan suna nan ba har Mammah).
      Ganin yanda ta koma saboda ambaton Farah da yayi sai ya ɗauketa cak domin gusar mata da tunanin, saman gadon ya ɗorata yana ƙoƙarin kwance towel ɗin jikin nata ta riƙe gam idanunta na firfitowa waje da jera masa roƙon haƙuri jikinta har rawa yake.
     Duk yanda yaso ya danne sai ya kasa sai da ya dara. Ya ɗan dungure mata kai da faɗin, “Matsoraciya kawai. Tashi ki shirya kici abinci inason fita”.
     Yana gama faɗa ya nufi hanyar fita dan ya bata damar da zata kimtsa tunda ya fahimci a takure take matuƙa.

     Koda ya fita ɗakinta ya nufa, babu jimawa sai gashi da kayanta ya ɗakko mata. Less ne zani da riga kalar milk da kwalliyar coffee. Sai B&F ɗinta daya tuno masa randa ya far ganinta a gidan Granny. Haka kawai ya shiga sakin murmushi shi kaɗai tun a ɗakinta. Tana gyar gashinta ya shigo, ganin duk ta daburce sai baiyi magana ba ya ajiye mata kayan kawai a gado ya fice abinsa zuwa falo.
        Ajiyar zuciya ta sauke tare da juyowa ta kalla kayan nata. Har cikin ranta tanajin daɗin wannan kulawar tasa na yimata hidima batare da duba cewar ya girme mataba. Sannan inda wani ya bata labarin zata iya samunsa haka da sauƙin kai bazata yardaba. Musamman idan tai dubi da halayyarsa da kowa ke kallonsa da ita na rashin sakewa da barazana da rashin ɗaukar raini. Shiyyasa akace karka yankema mutum hukunci har sai ka zauna da shi sannan. Dan wani ɗan adam ɗin ba'a taɓa karantar shi wanene sai an rayu da shi. Ashe wannan damar Farah ta samu daga garesa take yanda ta gadama. A binda kuma ta fahinta da shi adalcine kawai da sanin darajar mace da son mutuntata ya sashi zama mai sauƙi ga iyalansa badan anfi karginsa bane ko bazai iya motsa ƙwanji ba. Jitai wani natsuwa da kaunarsa na sake saukar mata a rai da bargo, har tana jerama UBANGIJI kalaman godiya da samunsa matsayin abokin rayuwarta batare da yayi shawara da itaba ko dubi da cewar AK ɗin ya ɗarata a komai na darajojin duniya, a lahiran kuma tana fata da addu'ar su kasance a muhalli ɗaya a gurbin gidan aljanna insha ALLAHU rabbi..
     Da wannan tunanin ta kammala shiryawa a gurgurguje duk tunaninta su Granny na'a gidan basu tafi ba.............✍



*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_

*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_

*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_

*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍





*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

*_TYPING📲_*


*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

*Page 60*
________________________


*_KAƊAN YA RAGE SU ƘARE_*


*_MATA ƴan ƙwalisa kuna ina za'aci kasuwar sama babu ku?. Mg's skincare ɗin fa na gab da ƙarewar kaya kuna nan sake da baki baku mallaki naku ba_*


_Mg's SKINCARE nagartattun kayan ne dake gyara jiki da fata cikin sauƙi, sunada inganci da rahusa dai-dai da aljihunku._

*Da kin fito a ringa ga tauraruwar taurarin nan mai fatar da babu kamarta tamkar dinare abin haske da walwali.*

*_Sabulunsu kawai kika ɗana sai kinsan kin kai kuɗinki inda babu asara balle dana sani_*

_A yanzu haka muna jerin kayayyaki da suka rage kamar haka_👇🏻

Available

_Akwai: herbal whitening black soap 3k_
Akwai: beauty kit 11k shi set ne yakunshi Abu 6
Soap
Body cream
Face cream
Body nd face scrub
Cleanser
Glow oil

Location
kaduna buh mn tura Kaya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login