Showing 57001 words to 60000 words out of 223329 words

Chapter 20 - Makauniyar Kaddara Hausa Novel Complete

21 Nov 2024

1212

yaƙi na gaske Ahmad yazo Nigeria. Inda a wannan zuwan nasane Hajiya Iya ta amshe Moddibo ko hakan zaisa Ahmad ya ringa tunawa dasu.
      Hakan kuwa yaso fara tasiri akan Ahmad ɗin, saboda tsananin so da sukema Moddibo daga shi har Hindatu. Sai dai kuma yana kammala secondary daga tafiya karatu ƙasar London aka sake samun matsala suka sake ƙwace abinsu. Ɗan dawowa da Ahmad ɗin ya farayi garesu ta ƙara lalacewa. Sai dai Alhmdllh duk hutun duniya a Nigeria Moddibo keyinsa. Wannan ne ya ɗan sanyaya ran Hajiya Iya. Amma duk da haka basu daina yaƙin son maido Ahmad jikinsu ba. A dalilin Adnan da shima rashin zuwan mahaifin nasa gida ke cin ransa suka sake dawo dashi cikinsu a shekarun nan, sai dai kuma suna murna an samu waraka shima sai Adnan ɗin ya ɗauke tasa ƙafar gaba ɗaya a dalilin aure da Hajiya iya ta matsa masayi.......
         Nannauyan numfashi Baffah ya sauke mai haɗe da ajiyar zuciya saboda fahimtar da yay tunaninsa yayi zurfi. A yanzu haka kuma ba tunanin abinda ya shuɗe bane mai muhimmanci garesa, a'a abinda zaizo shi ya kamata yay tunanin gyarawa kodan farin cikin mahaifiyarsa ma dasu kansu shi da ƴar uwarsa da zuri'arsu. Dan haka ya sake zurfafa a wani dogon tunanin da bai dawo hayyacinsaba sai a wani tsahon lokaci daya samo mafitar da yaji har a cikin ransa ya gamsu da ita sannan.

         ★★★★

   Washe gari daga sallar asuba ya zarto sashen Hajiya iya. Bayan ya zauna sun gaisa ya zayyane mata shawarar da ya yanke a wannan karon. Cikin jimami tace, “Amma Kabiru baka gani wannan shawarar tana kamanceceniya data baya kuwa?”.
        “Eh to Inna tana kama da ita. Sai dai akwai ɗan banbanci da waccan ɗin. Ki dai tayani addu'a, kuma ki ƙara nazari kema akan hakan mugani”.
      “To shilenan. Ai ba'aƙi ta mutumba inji masu iya magana. ALLAH ya shige mana gaba”.
      “Amin ya rabbi Inna nagode. Ina mutuniyar takine banji motsintaba?”.
      “Oh kana maganar Zinneerah ne? Tana ɗakin Moddibo tunda ba zuwa yakeba ita ai saita zauna. Dan nace ja'iran nan suzo su rinƙa tayata kwana harta saba wai tsoro sukeji sudai. taya zasu iya kwana ɗakin Yayansu bayan kowa yasan dokarsa ba'a shigar masa ɗaki sai da dalili mai ƙarfi”.
       Dariya Baffah yayi yana faɗin, “Inna sunsan halinsa ba wasa yake dasuba ai Babana. Itama Zinneerah ɗin dai gara a gyara mata wani karki haɗa rikici Inna”.
       “Oh to nima tsoron nasa nakeji kenanma ashe?. To yaci ƙaniyarsa shida dokar tasa babu inda zataje. Idan yazo ni basai ya dakeniba mai bauɗaɗɗen halin tsiya irin na uwarsa”.
      Dariya Baffah ya mike yanayi shidai da faɗin, “Ai kunfi kusa Innata.  Wazai yarda ya shiga tsakaninki da Adnan da Khalipha a gidan nan”.
       “Aikam ni yanzu bana yayin wani Moddibo can. Garama Khalipha ɗin duk da shima ja'irin kansane, daka ɗakko laifin takwaran nasa zai fara karewa da yayansu kaza-kaza, saikace akansa aka fara ɗan uwa”.
     Shi dai Baffah dariyarsa yaketa sha harya samu ya gudu domin zuwa yay shirin fita kasuwa.

       Lokacin da Hajiya iya kenan suna maganarsu da Baffah Zinneerah datai kwanan baƙunta a ɗakin data fahinci mai shi mutum ne mai matuƙar daraja da girma ga jama'ar gidan, dan su Meenal ƙiri-ƙiri sunƙi zaman ko mintuna goma a ciki, nacan ta shige cikin masu aikin Hajiya Iya tana tayasu aikin gyaran sashen. Lokacin da Baffah ya fito ya fice suna Kitchen domin haɗa breakfast kasancewar kullum anan Baffah ke karin kumallon safe tare da mahaifiyar tasa.
    Masu aikin sunso hanatayi amma taƙi. Dole suka barta saboda sunsan yaran gidan dama kan shiga ai aiki dasu suma bisa dokar Hajiya Iya. Amma da dan ta iyayensu matane kam da ba hakaba. Itako Hajiya Iya ta tsaya tsayin dakane domin taimakonsu tunda tasan gidan wani zasuje.
     Bayan sun kammala komai tsaf Baba Rahi tace taje tai wanka kafin Hajiya Iya ta fito dan batason ƙazanta ko kaɗan. Shiyyasa kosu kansu idan baka saniba bazaka taɓa ɗauka ƴan aiki bane a gidanma sai an faɗa.............✍

     
*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_

*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_

*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_

*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

*_TYPING📲_*


*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*


*Page 18*
____________________

*_INA MATA ƳAN ƘWALISA BA'ABOTA SON GYARA JIKI DA FATA SUYI ƘWANAS TAMKAR WATA ƊAN DAREN SHABIYAR?!_*

_Ku marmatso kusa maza na kaiku kantin sauƙi na UMMU DUFAIL gidan sauƙi da biyan buƙatar MATA SARAKAN ado harma da MAZA ƴan ƘWALISA._

*_MATA da yawa kanso su koma Taurari ababen kallo da burgewa ga ma'abota kallo sai dai basusan ina zasu sami sinadarin kankaro wannan ƙyawu da mutuncinba._*

_To maza kuzo kusa dan Bilyn Abdull ta lalubo muku kantin sauƙi na Umm Dufail dakeda kaya masu sauƙi da gamsar da maison afani dasu_.

*_UMMU DUFAIL nada kayan gyaran jiki masu rahusa da inganci da gamsar da mai saya cikin ƙanƙanin lokaci kamar haka👇🏻😁_*


*Customers price list By Ummu Dufail FACE AND BODY*

SCRUB=2500(300ml)
Face and body mango butter=3k (250ml)
Face cream= 1800
Corretor oil/vitamin C oil=2k
Fairness skin lotion= 2500
Hot chocolate skin lotion 2500
Serum (for Nuckles )2k
Nuckles cream (stubborn)3500
Mix fruits Arabian black =soap 1800
Mix fruit glycerine soap =1900
Beetroot=1900
Coconut, milk,egg..face soap=1200
Lavender mix fruit soap =1800
Body wash =1500
cleanser=1600
Hair spray =700
Hair oil =1500
Hair relaxer =700
Hair butter 1700
Shampoo =1500
Breast=oil 2k powder 2k
Strech marks cream= 2k
Beetroot pink lips =700
Baby care soap glycerine=1k
Baby care butter =1500
Shea butter baby soap =700
Tsumin tula =2200
Tsumin zinariya =1200
Sliming tea =1500
Amarya set =25k
Liquid Arabian black soap =1900
Cleansing water =1500

*_Zaku iya bibiyarta domin gani da ido ta Handle ɗinta na istagram da facebook kamar haka_*

Ummu Dufail @ Facebook
Ummu Dufail @ instagram
Phone no: 07067943479.

_Ƴammata harma da masu auren karku bari ayi babuku. Dan gyara shine mace a wannan ƙarnin😉👍🏻_.

______________________

*Page 18*

...........Washe gari daga sallar asuba Baffah ya zarto sashen Hajiya iya. Bayan ya zauna sun gaisa ya zayyane mata shawarar da ya yanke a wannan karon. Cikin jimami tace, “Amma Kabiru baka gani wannan shawarar tana kamanceceniya data baya kuwa?”.
        “Eh to Inna tana kama da ita. Sai dai akwai ɗan banbanci da waccan ɗin. Ki dai tayani addu'a, kuma ki ƙara nazari kema akan hakan mugani”.
      “To shilenan. Ai ba'aƙi ta mutumba inji masu iya magana. ALLAH ya shige mana gaba”.
      “Amin ya rabbi Inna nagode. Ina mutuniyar takine banji motsintaba?”.
      “Oh kana maganar Zinneerah ne? Tana ɗakin Moddibo tunda ba zuwa yakeba ita ai saita zauna. Dan nace ja'iran nan suzo su rinƙa tayata kwana harta saba wai tsoro sukeji sudai. taya zasu iya kwana ɗakin Yayansu bayan kowa yasan dokarsa ba'a shigar masa ɗaki sai da dalili mai ƙarfi”.
       Dariya Baffah yayi yana faɗin, “Inna sunsan halinsa ba wasa yake dasuba ai. Itama Zinneerah ɗin dai gara a gyara mata wani karki haɗa rikici Inna”.
       “Oh to nima tsoron nasa nakeji kenanma ashe?. To yaci ƙaniyarsa shida dokar tasa babu inda zataje. Idan yazo ni basai ya dakeniba mai bauɗaɗɗen halin tsiya irin na uwarsa”.
      Dariya Baffah ya mike yanayi shidai da faɗin, “Ai kunfi kusa Innata.  Wazai yarda ya shiga tsakaninki da Adnan da Khalipha a gidan nan”.
       “Aikam ni yanzu bana yayin wani Moddibo can. Garama Khalipha ɗin duk da shima ja'irin kansane, daka ɗakko laifin takwaran nasa zai fara karewa da yayansu kaza-kaza, saikace akansa aka fara ɗan uwa”.
     Shi dai Baffah dariyarsa yaketa sha harya samu ya gudu domin zuwa yay shirin fita kasuwa.

       Lokacin da Hajiya iya kenan suna maganarsu da Baffah Zinneerah datai kwanan baƙunta a ɗakin data fahinci mai shi mutum ne mai matuƙar daraja da girma ga jama'ar gidan, dan su Meenal ƙiri-ƙiri sunƙi zaman ko mintuna goma a ciki, tana can ta shige cikin masu aikin Hajiya Iya tana tayasu aikin gyaran sashen. Lokacin da Baffah ya fito ya fice suna Kitchen domin haɗa breakfast kasancewar kullum anan Baffah ke karin kumallon safe tare da mahaifiyar tasa, weekend ne kawai bayayi anan.
    Masu aikin sunso hanatayi amma taƙi. Dole suka barta saboda sunsan yaran gidan dama kan shiga ai aiki dasu suma bisa dokar Hajiya Iya. Amma da dan ta iyayensu matane kam da ba hakaba. Itako Hajiya Iya ta tsaya tsayin dakane domin taimakonsu tunda tasan gidan wani zasuje.
     Bayan sun kammala komai tsaf Baba Rahi tace taje tai wanka kafin Hajiya Iya ta fito dan batason ƙazanta ko kaɗan. Shiyyasa kosu kansu idan baka saniba bazaka taɓa ɗauka ƴan aiki bane a gidan ma, sai an faɗa.
         Babu musu ta nufi komawa ɗakin data kwana. Ɗakin da kallonsa kawai saka mata wani shakkar zama a cikinsa take shiga. Dan har cikin ranta tanaji cewar matsayinta bai kai na ta zauna wannan ɗakinba da take ƙyautata zaton na musamman ne.
       Kamar yanda ta kasance a ɗarare daren jiya yanzunma a ɗararen tai komai. ALLAH ya taimaketa ma hatta da soson wanka da kayan shafarta ta taho da abinta. Komai na ɗakin bata yarda tai amfani da shiba bayan ruwa, sai bargo data saka a ƙasa ta kwanta a daren jiya.
     Tsaf ta kammala shirinta cikin riga da skirt na atanfa ruwan bula da ratsin fari, sai ɗan baƙi-baƙi kaɗan. Hijjab ƙarami data taho dashi saboda zaman gida ta ɗauka ta saka sannan ta fita. karo suka kusanci da Jamal tai baya da sauri.
     “Oh sorry Sister, dama Granny tace ki fito ke kaɗai ake jira cin abinci”.  Kallonsa tai kamar zatai magana sai kuma tai shiru saboda tinawa da nasihar mahaifiyarta data tuno akan zaman gidan. Tai ɗan murmushi da faɗin, “Ina kwana”.
      Dariya yayi yana susan kai. “Uhm su Jamal an girma. Wai ni kike gaidawa ma kowa?”.
     Karon farko tai dariya da fara tafiya, har cikin rai yanda suke da barkwanci na birgeta. Shima sai ya biyota yana rawa wai an gaishesa, bayan kaf gidan shike gaida kowa. Koda suka iso ƙaton dining ɗin karaɗinsane ya saka kowa maido hankalinsa kansu. Ya ƙaraso garesu yana basu labarin yau an gaisheshi shima ya tashi daga autan gidan nan yanada ƙanwa.
        Babu wandama yaji miya faɗa dan duk hankalinsu nakan Zinneerah da duk ta daburce saboda idanunsu. Ƙasa takai tsugunne dai-dai tana isowa gabansu tace, “Hajiya ina kwana?”.
       Fuskar Hajiya Iya ɗauke da fara'a da kulawa ta amsa mata, tare da tambayarta baƙunta. Kan Zinneerah a ƙasa take amsawa. kafin ta juya ga Baffah shima ta gaidashi da girmamawa. Amsa mata yay shima cikin kulawa da faɗin, “Kinga taso ga abinci, ga kuma ƴan uwanki nan dake gida duka”.
       Kanta ta jinjina masa jikinta na ƙara saki saboda jin idanunsu duk a kanta. batare data miƙe ɗinba tace, “Ina kwanan ku?”.
     Moos'ab ne ya fara sauke numfashi da amsa mata. “Lafiya lau ƴar ƙyaƙyƙyawa, Granny ina kika samo mai kama da Inno haka?”.
      Kafin Hajiya Iya ta bashi amsa Haneef ya amshe da cewa, “Masha ALLAH ko itace ƙanwar tamune?”. Saifudden zaiyi magana shima Baffah da ke shirin fara cin abincin da Abidah ta haɗa masa yace, “Wai ni gidan nan halan duk ƴan jarida muka tarane? Indai kune yanzu sai kowa yace sai ya mata tambaya anan. Ɗiyata taso kinji”.
       Cikin jin kunya ta taso ta zauna kujerar da Ni'ima ta gyara mata. Kallonsu Baffah yayi su duka, danya fahimci har yanzu duk hankulansu naga Zinneerah musamman ƴan samarin ƴaƴan nasa. Yay ɗan murmushin manya yana lumshe ido da buɗewa. “Wannan itace Zinneerah ƙanwarku. Wadda tun kafin zuwanta an sanarma kowa dake gidan nan. Muna fatan zaku karɓeta da hannu biyu ku kuma ɗauke babu wani banbanci daku”.
      Insha ALLAHU Baffah.
Suka haɗa baki wajen faɗa su duka.
    Kansa ya jinjina cike da gamsuwa yana maida dubansa ga Zinneerah da kanta ke ƙasa. “Ɗiyata Zinneerah ɗago ki kalli kowa danki haddace fuskokinsu da sunayensu”.
       Duk da tana cikin yanayin jin nauyi bin umarnin Baffah dolene a gareta. Hakan yasa ta ɗago a hankali. Da wanda ke kusa da Hajiya Iya ya fara. “Wannan sunansa Mas'ood, ƴan biyu ne shi da Moos'ab gashinan. Wannan kuma Saifudden, wannan Haneef, wannan Abidah, wannan Safiyya, wannan Ni'ima. Sai Jamal, Meenal, Bahijja. Akwai yayunki kusan goma da babusu anan. Koda yake ba duka bane yayun naki a cikinsu dan kin girma wasu. Insha ALLAH duk zaki sansu su sanki suma a hankali. Waɗan nan dai sune yanzu tare dake anan gida, zaki kuma kasance da kusan dukansu yanzu a gida insha ALLAH”.
        Fuskarta daɗan murmushi tace, “Nagode Baffah”.
      Murmushin shima yay mata yana jinjina kansa. Yayinda su Haneef suka haɗa baki wajen, “Welcome to Shira's family ƙanwarmu”.
       “Na gode Yayuna”.
Ta faɗa ita cikin son aro jarumtar son sakewa da su. Dan taji daɗin yanda duk suka nuna jin daɗin kasancewarta a cikinsu.
    Ƴar gajeruwar nasiha Hajiya iya tai musu akan zuminci kafin su fara cin abincinsu a tsanake. Wajen yayi shiru bakajin ko ƙwaƙwƙwaran tarin wani saboda dokace a garesu ba'acin abinci ana magana musamman idan Hajiya Iya da Baffah na waje. Uwa uba kuma Babban Yaya mai gayya mai aiki dashi ko ƙara cokalinka ya cikayi sai kasha uwar harara.

         Koda duk suka kammala duk ficewa sukai, dan dukansu karatu sukeyi a mabanbanta makarantu jami'oi. Wasunsu na gab da kammalawa, wasu kuma yanzu suka fara musamman ƴammatan. Wasu kuma na tsakkiya. Sai su Bahijja dake secondary sun wuce Zinneerah da aji daya, dan suna ss2. Sai dai yau bazasujeba dan suna wani ɗan hutun kwana biyu a gida.
      Bayan wucewar kowa ita dasu Meenal ɗin ne suka gyara dining ɗin. Hajiya Iya kuma ta nufi ɗaki gabatar da sallarta ta walha tana bar musu saƙon raka Zinneerah wajen iyayensu ta gaishesu.
     Suna kuwa kammala gyara wajen suka jata. Meenal ce taja birki lokacin da suke gab da kaiwa tsakkiyar ƙaton harabar gidan nasu. “Kunga ku tsaya a fara da nunama sister kowanne sashe first”.
       “To uwar tsari”. Cewar Jamal da shaƙiyanci.
     Hararsa Meenal tayi sai dai batace komaiba. Bahijja tace, “Da gaskiyar sister ai, a fara da waje”.
      “Naji karku cinyeni da baki malamai. Sister Zinneerah nan inda muka fito shine sashen Granny nasan kin sani ai?”.
    Jamal ya faɗa idonsa a kanta. Batare da jiran amsarta ba ya cigaba. “Wannan na kusa da shi shine sashen Daddy Ahmad ne. Sai dai basa nan suna ƙasar Turkey lokaci-lokaci suke zuwa. Yaransa biyar shima. Yah Ibrahim, Yah Sadiq, Yah Hafeez. Aunty Zuhrah. Sai Aneesa dan bazance mata Aunty ba, kwana tara kawai ta bani a duniya kamar wannan yarinyar”. Ya nuna Meenal.
      “Shashasha ai dai na girmekan ko?”.
        “Oho a banza dai tunda kammu ɗaya”. Ya bata amsa yana mata gwalo.
    Dariya abin nasu keba Zinneerah. Dan haka yanzuma tai murmushi mai faɗi.
       “Yauwa sai nan kuma Sashen Gwaggo Bilkisu ne idan tazo nan take sauka itama. Tana Lagos da yaranta huɗu itama, kada lissafin yay miki yawa zakisan sunayensu suma nan gaba. Sai nan shine sashen su Yah Saifudden. Nan kuma sashen baƙine. Wannan da zamu shiga shine sashenmu, iyalan Baffah kenan”.
    Murmushi Zinneerah tai cike da gamsuwa dajin birgewar tsarin nasu. Batare da tayi maganaba suka nufi sashen Baffah ɗin da yafi na kowa girma a gidan kasancewar yafi kowa yawan iyalai.
      Sun fara shiga katafaren falo da yaji kayan more rayuwa da ƙawa, wanda har suka fice daga cikinsa Zinneerah bata gama kammala kallon daular dake shimfiɗe a cikinsaba. Basu tsaya anan ba suka isa falo na biyu wanda shima ƙatone na gaske harma zai iya ɗara na farko kayan alatu. A tunaninta an gama kenan, sai taga sun shigo wani falon a hannunsu na dama, sai dai shikam madaidaicine bakai na baya girmaba amma ya fisu tsaruwa.
      Hamshaƙiyar mace ƙyaƙyƙyawa dake zaune da waya a kunne ta ɗago tana kallonsu. Fuskarta a sake take sai dai ba murmushi takeba. Zama su Bahijja sukai a kujera suna faɗin, “Barka da safiya Momie”.
      Kasancewar waya take bata amsa musu ba. Tadai ɗaga musu hannu kawai idonta akan Zinneerah data kai zaune ƙasa zuciyarta na harbawa da ganin kamanin matar da Khalipha sosai. Bayan ta kammala ta ajiye wayar tana faɗin, “Masha ALLAH ɗiyata sai yanzu muke ganinki?”.
       “Kuyi haƙuri Momie”. Zinneerah ta faɗa kamar yanda taji su Meenal na kiranta.
      Cikin ƴar dariya tace, “A'a aiba laifi kikaiba ƴata. muna miki maraba da shigowa cikinmu”.
       Gaba ɗaya kan Zinneerah a kulle yake. Tadai daure ta amsa mata da godiya tana gaisheta cikin girmamawa. Hakan yasaka Hajiya Nafisa jin daɗi har ranta dajin ƙaunar Zinneerah. Sun ɗanja lokaci a sashen Hajiya Nafisa da suke kira Momie nata mata ƴan tambayiyi jefi-jefi da janta da hira.
       Hajiya Nafisa itace Baffah ya aura bayan rabuwarsa da Hindatu. Itace mahaifiyar Khadija da a yanzu haka tayi aure itada ƴar uwarta Hafsat. Sai Khalifa, Saifudden, da auta Bahijja. Sunɗan jima Kafin su miƙe su fito dan itama wajen aiki zata fita.
    Daga nan sai sashen Hajiya Halima mahaifiyar su Meenal. Wadda suke kira Ummi. Itace ta haifi Mas'ood, Moos'ab, Ni'ima, Meenal

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login