Showing 210001 words to 213000 words out of 223329 words

Chapter 71 - Makauniyar Kaddara Hausa Novel Complete

21 Nov 2024

1158

a kanta yana kaiwa zaune kusa da ita little a jikinsa.
      “Jikin ne kuma?”.
  Fuska Zinneerah taɗan yamutse tana kamo hannun little ɗin. “Kawai dai banajin ƙarfi ne amma babu inda kemin ciwo, garama tashin zuciya daketa damuna tun cin kifin nan na jiya da naci”.
      Tausayintane ya sake kamashi, musamman daya tuna yanda taita damunsa da maganar kifin. harma ya dawo gida jiya da nufin bazai sake fitaba ta takura sai da ya fita kusan goma na dare ya nemo mata kifin, gashi kuma taci ta kasa zaman lafiya.
         “Sannu ALLAH yay miki albarka ya saukeki lafiya. Bara na taɓa Mahmud naji kozaki iya shan wani abu dazai baki nutsuwa”.
       “Yayanmu kama barshi zai bari dan kansa. Dan nayi waya da Yaya gajeje tace na samu ɗan kanwa kaɗan nasa a ruwa na sha zai faɗa min”.
        Kafin yace wani abu little da yay kamar ba saurarensu yakeba yace, “Aunty sorry, idan kika haifa mana babynmu zan kaiki makka”.
       Dariya zancen nasa ya basu, dan haka suka murmusa AK na shafa kansa. “ALLAH ya tabbatar ɗan albarka. Yanzu ka muje na maka wanka kaga aunty yau babu kanta”.
    Kansa ya ɗaga masa. Zinneerah tace, “Kama barshi zan iya masa. Bara kaima na haɗama ruwan wankan ga abinci nan na shirya”.
        “Kina fama da kanki kika wani kama abinci? Nace miki duk randa baƙyajin daɗi basai kinyi ba tunda ga gidan Granny sai a kawo daga can”.
    Murmushi ta ɗanyi da kama hannunsa dan ta tura little ɗaki ya kai kayan sa. Ta kwanto jikin hannunsa tana duban ƙyaƙyƙyawan fuskarsa. “Yayanmu nace makafa bawani ciwo nakejiba ALLAH. Kuma idan ban motsa jikin ai sai wani kuma ciwon ya taso”.
    Kanta ya shafa yana rungumota da ƙyau jikinsa. Ya sumbaci laɓɓanta da goshinta yana jera mata addu'a. Itama hannunsa ta sumbata ranta fes ƙaunarsa na ƙara shigarta jini da ɓargo.

        Kwana biyu dayin haka sai ga Mahma daga london. AK yaji matuƙar daɗin wannan zuwa nata, dan dama lokacin bikin su Adilah ta tabbatar masa da cikin Zinneerah ya shiga watanni bakwai insha ALLAH zatazo Nigeria. To shikam ya ƙudiri tunda tazo riƙeta zaiyi har sai matarsa ta haihu.
      Sosai Zinneerah ma ta nuna farin cikinta sosai na zuwan Mahma. Dan-danan ta gyara mata ɗayan ɗakinta na falon farko duk da dama fes yake. Bakuma wani amfani take da shiba garama da ƴan Danya sukazo tariyarar Yaya Sa'a sun kwana a ciki.
     Itama Mahma taji daɗin yanda suka tarbetan, tare da ɗunbin tausayin Zinneerah daketa fama, dan ga cikin nata yayi girma sosai Alhmdllh kamar ba ɗan wata bakwai ba. Kasama haƙuri tayi sai da tace, “Anya cikin nan ba ƴan biyu bane kuwa a cikinsa?”.
     Cike da kunya Zinneerah tai ƙasa da kai tana murmushi kawai. Sai AK dake saurarensune yace, “Ƴan biyu kuma Mahma?”.
       “Eh mana Abdul-Mutallab, ai girman cikin ne masha ALLAH kamar ba wata bakwai ba”.
       Kallon Zinneerah ɗin yayi shima da ƙyau zuciyarsa na fata da tabbatar wannan zance na Mahma. Yace, “To Mahma bamu saniba dai, amma ALLAH ya tabbatar”.
       “Amin to, amma baku dubaba kenan?”.
      “Wlhy Mahma banason wannan bin ƙwaƙwƙwafin, komai ya fito a cikin nan ina maraba dashi da so da ƙaunarsa”.
       “Alhmdllh aihaka akeso musulmi ya kasance Abdul-Mutallab, ALLAH ya rabasu lafiya”.
    Da “Amin” ya amsa mata. Zinneerah kuwa tayi a zuciyarta kawai.............✍


*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_

*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_

*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_

*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍



*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

*_TYPING📲_*


*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*


_______________________

*Page 67*

.............Alhmdllhi sosai zuwan Mahma ya taimakawa Zinneerah, dan tana ɗebe mata kewa da rage wasu abubuwan. Tana kwana na huɗu ma da zuwa sai ga wata dattijuwa Hajiya iya data sa aka kawo mata daga bauchi ta iso. Nanma ya haɗu ya ƙara taimakawa Zinneerah ɗin sosai. Dan Mama A'i mace ce mai ƙoƙari da haƙuri. Gashi bata da yawan hayaniya itama ga kuma tsafta. Hakan yasa tasu tazo ɗaya da AK. Duk da dai iyakacinta ɗan taya aikin gida Mahma ke musu girki, wani lokacin kuma Zinneerah ɗin kan shiga da kanta tayi. Hidimar Little kuwa dama ta koma hannun Mahma. Yanzu ma a ɗakinta yake kwana abinsa.
     Haka aka cigaba da turawa har ALLAH ya sauka Tinene lafiya daga danya. Ta samu ƴarta mace mai kama da ubanta sak. A randa ta haihu a ranar aka ɗaura aurenta da Lado. Bayan arba'in zata ta tare. Baba bai gayama Sa'a da Zinneerah ba sai kusan kwanaki biyar da haihuwar ma. Dukansu sun mata addu'a da fatan alkairi, suka kuma aika musu da abinda ALLAH ya hore musu tunda duk ba sana'a sukeba. Dan Sa'a ma makaranta ta koma Dr Mahmud nason ta haɗa kwalinta na secondary da shirirta da halin Inna yasata kasa haɗawa. Tunda koda ta koma bayan baro Zinneerah Danya bata kammalaba tunda komawa tai ta fara daga js1.
       Ranar tarewar ma da ƙyar AK ya yarda suka tafi ita da Sa'a. Amma ya tabbatar mata banda kwana ranar zasu dawo. dan ko little ma bai bitaba ita kaɗai ta tafi Haneef ya tafi kaisu ita da Sa'a dasu Bahijja.
       Sun sami tarba mai ƙyau, dan kowa sai ji dasu yake sun zama tamkar wasu taurari a dangi baki ɗaya. Kowa nata tausayin Zinneerah da fatan ALLAH ya sauketa kafiya. itama Sa'a ALLAH ya bata nata dan har yanzu dai babu ciki.
     Ganin yanda jikin Inna ya ƙara rincaɓewa yasa hankalin Zinneerah da Sa'a ƙara tashi, dan Karima dake gidan tana kula da ita tata ƙorafi kenan da mita. Wani lokacinma sai yaya Gajeje ta yunƙuro tazo ko matar baba tai mata wani abun Karimar na zaune taƙiyi. Kiran AK tai ta sanar masa. Bai wani ja zancenba yace ta haɗashi da Haneef dan tunma ɗazu yake nemansa ya gaza samu, itama ɗin ya nemetan yaji yaya suka sauka amma bai samuba sai yanzu data kirasa.
     Umarni ya bama Haneef ɗin akan su taho da Inna kano. Batare da Zinneerah tasani ba sai da aka idar da sallar la'asar Baba ya tunkaresu da zancen. Murmushi kawai tayi bata nuna bata saniba. A ranta kuwa tana mamakin Yayansu.
       Kowa yaji daɗin abinda AK ɗin yayi, dan haka ana gama shagali basu zauna akai amarya ɗakintaba suka tattaro zasu taho, wai kuma Karima zata biyosu Baba yace bata isa ba. Yaya gajeje zata bisu daga baya. Itako ta zauna Danya.
          Sa'a ma da nufin kwana tazo, amma jin Zinneerah bazata kwana ba kuma za'a tafi da Inna sai kawai ta shirya ta biyosu. A shira hospital suka sauke Inna, inda Dr Mahmud yasan da zuwan nasu dan sunyi nagana da AK. Anan suka bar masa Sa'a bayan sunga komai ya dai-daita na kula da Inna. Haneef ya wuce da Zinneerah gida ya fara ajiyeta sannan suka wuce gida suma dasu Meenal.
         Tun daga ranar jinyar Inna ya dawo ƙarƙashin kulawar su AK, amma Yaya Gajeje tazo daga danya tana tare da ita a asibitin. Kullum sai Zinneerah taje ta dubata kamar yanda Sa'a ma haka. Alhmdllh kuma jikin nata na ƙyau ba kamar sanda tana Danya ba. Dan magunguna masu ƙyau da tsada ake mata amfani dasu, ga kulawa ta musamman da take samu daga mazan ƴaƴan nata. Baba ma lokaci-lokaci yakanzo dubata shi da yan uwansa da amaryarsa da Karima.
        
        A haka Zinneerah ta cigaba da turawa har aka shiga kwanakin jiran tsammani na haihuwarta. Zuwa yanzu kam sosai bata da lafiya tamkar cikin little, dan dolema aka koma da ita zaman asibiti. Kwanakinta shidda a asibitin a wata safiya ta wayi gari da naƙuda. Sai dai fa tamkar cikin little jini ya ɓalle mata ga haihuwar shiru. Hankalin AK da kowama ya tashi, hakan yasa Dr Mahmud ya bada shawarar kawai ai mata cs kafin ta jigata ƙarfinta ya ƙare.
    Babu wani jayayya AK ya amince. Zuciyarsa fal tausayin halin da take ciki. Yayinda yake rayawa a ransa ko wannan tashin hankali da ta shiga a wancan karon na haihuwar little ya isa hana su Farah zaman lafiya da jin daɗi. Shikam sai yanzuma yake ganin matsalar da sukaita fuskanta na rashin jin daɗin rayuwar aurensu kullum faɗa da fitina shi da Farah ko wannan halin da suka zama sanadin jefa yarinyarnan ya isa su rasa farin cikin rayuwar aurensu ai. Dan Dr Mahmud ya tabbatar masa da haka tasha irin wannan wahalar a wancan karon ma.
      Alhmdllh an yi mata cs aka ciro ƴaƴa biyu mace da namiji. Zokaga murna wajen kowa. Shikam AK duk da yana murna da samuwar tasu hankalinsa nakan matarsa. sai da yaji tabbacin kasancewarta cikin ƙoshin lafiya sannan hankalinsa ya ɗan kwanta harya amshi jariransa ƙyawawa masu lafiya yana mai jerama UBANGIJI godiya daya bashi ƙyautarsu ta silar da ALLAH ya halatta masa bayan ya cire tsammani daga hakan.
         Inna daketa samun sauƙi tana zaune dan yanzu takan ɗan motsa jikin aka sanar mata da haihuwar Zinneerah. Hawaye kawai su Sa'a sukaga tanayi amma batace komaiba. Hakan yasa suka gagara fahintar na minene? Na daɗine kona nadama? Kona baƙin cikin har yanzu?.
     Oho masu karfin ajin ma basusan tanai ba. Dan cikin ƙanƙanin lokaci Shirawa suka cika asibitin domin taya Yayansu murna da samun wannan ƙaruwa. Waɗanda basa kusa kam irinsu Khalipha da Adilah tuni hotunan babes ya isa ga wayoyunsu.
       Addu'a dai kam sun shata kamar yanda Zinneerah ma keshan tata na fatan samun lafiya. dan kowa bai gantaba itakam har AK ɗin sai da daddare. Shima ya samu tanata barci. Ya ƙureta da ido cike da tausayi da ƙauna dan dukta rame sosai fiyema da lokacin da cikin na jikinta. Sumbatar goshinta yayi da hannunta yana mai jera mata addu'ar samun lafiya.

    Sauran ƴan uwa kuwa da abokan arziƙi basu sami ganintaba sai washe gari, zuwa sannan ta farka Alhmdllhi. Kuma tana gane kowa da amsama kowa gaisuwarsa.
     Lokacin da taga ƴan jinjirayenta da farin cikin dake shinfiɗe a fuskar AK murmushi ta dinga zubawa itama. a ranta tana musu addu'a. A fili kuwa sai ta dinga nuna alkunya su Hajiya iya na mata dariya. Sai dai har cikin ransu hakan da tai ya musu daɗi, dan yaran yanzu daba kawaici garemu akan ƴaƴaba koda na farine balle na biyu.
      Sai dai kuma wata sabuwa. wannan karonma tamkar haihuwar little ruwan nono ya zamarwa yaran damuwa. Dan da sun sha cikinsu duk sai yake kumbura suyita kuka. Ga namijin da son abinci tamkar ubansa. Hankalin AK ya tashi matuƙa da hakan. Amma da Dr Mahmud ya sanar masa haka dama sukasha fama akan little sai yaɗan sami nutsuwa. Yanzuma magunguna suka haɗa mata. Amma sai Mahma tace wanann al'amari kamar bana asibiti ba. Yanada nasaba da jinnu sai an dage sosai ma Zinneerah ɗin.
    Kowa yasha mamaki, amma sanin wacece ita a wannan fanin yasa duk suka amince. Itace da kanta ta fara harhaɗama Zinneerah magungunan gargajiya ta fara amfani dasu, tace insha ALLAH komai zai daidaita.

      Kwananta takwas a asibitin aka sallameta, Alhmdllhi zuwa yau kuma yara sunsha nono kuma babu wani matsala data biyo baya. Hakan ya saka kowa farin ciki dajin daɗi. AK yaga amfanin wannan sani na Mahma da yaketa ƙorafi akansa tunda gashi ta bama matarsa magani an kuma dace.
      A randa aka sallamesun ranar Mammah ta iso Nigeria, zokaga murna wajenta datai tozali da ƴan jikokinta. Su Adilah ma an iso daga Lagos suda tawagar Mommy. hakama Gwaggo Maryama. Inna ma da aka sallamota nan AK yace a kawo ta huta sosai kafin a maidata Danya.
     Kai tsaye gidan hajiya iya aka wuce da Zinneerah, za'ai suna acan sannan su koma gidansu su cigaba da jego kuma.
     Yara sunci sunayen Hajiya Iya da Baffah. *_Ameenatu & Kabeer_* za'ake kiransu (Amaan & Anam). AK ya zata Mammah zatai fushi, sai yaji batace komaiba. Yaji daɗin hakan, dan koba komai ya yarda ta dawo hankalinta yanzu kam.
      (An zinni sai muce ALLAH ya raya keda yayanmu angon jego).
        AK dai bason bidi'a yakeba. Dan haka aka shirya ƙwarya-ƙwaryar liyafa anan harabar gidan akaci akasha kowa ya godema ALLAH. Ƴan Danya, ƴan ɗanmusa ƴan bauchi sun cika gida dam domin taya murna. Hakama mai jego da jarirai sunsha ƙyau harsun gaji masha ALLAH.
    Kowa ka gani sai son barka. Amare ma da yawansu suna maƙale da cikkuna kanana sai fatan suma ALLAH ya saukesu lafiya.

        Kwana biyu da suna AK ya takura dole su Zinneerah suka tattaro suka dawo gidansu, aranar kuma ƴan danya da ƴan ɗanmusa suka koma. Suma ƴan bauchi washe gari suka kama gabansu sai kuna wata ta taso.
      Zinneerah tayi farin cikin kasancewar gidan cike da jama'a. Dan kuwa Ga mahma ga Mammah da suka koma sashen Farah suka zauna. Ga kuma Mama Ai, ga Yaya Gajeje da Inna. karima ma maƙalewa tai taƙi bin ƴan suna. Sai Tinene da Atine ne suka koma da amaryar baba.

      Ganin al'amura komai ya daidaita jikinta yayi sauƙi kamar ba yankata akaiba Alhmdllh yasata ƙudirin tunkarar AK da batun dawowar Farah gida. Dan itako tama fi son ta dawo hakanan tunda dai tasan zuwa yanzu ta horu. Dan su Meenal suna bata labari da sukaje da Granny kwanaki duba Farah ɗin abin gwanin ban tausayi. Duk sun fita hayyacinsu ita da Zakiyyan dan horo mai tsanani maimartaba yasa aketa musu batare da sanin kowa ba. Idan ka gansu bazaka taɓa ɗauka su din bane ƴan gayu ƴan ƙwalisa masuji da naira a bankuna.

          Suna zaune a falonta na farko ita da Yaya Gajeje da Karima, Yaya Gajeje tana shirya ƴan biyu da akaima wankan safe. Zinneerah ma tayi nata dan tana cikin kwalliyarta tamkar ba jego takeba. Har Karima na tsokanarta da tacigaba da kashe ɗauri baban ƴan biyu ya lallaɓo a samo gambo kafin arba'i.
        “Ya ilahi, dan ALLAH Yaya Karima barmin baki, ina ni ina wani gambo ana zaune ƙalau”.
     Dariya suka sanya mata, suna cikin dariyarne Mama A'i ta shigo riƙe da hannun Little dake kuka wai ya faɗi. Dubansu duk suka maida garesu, Karima na kamo hannun little ɗin da faɗin, “Yaya akaine Abdul?”.
       “Faɗuwa yayi, ya shigo da gudu yaci karo da kujera”. Mama A'i ta bama Karima amsa.
       Baki Zinneerah ta taɓe tana miƙama Yaya Gajeje pampas da za'a sakama Anam. Tace, “Maganinsa kenan, shidai a rayuwarsa yayi gudu, bansan daɗin mi yakeji ba sai kace wani ɗan ƙwallo”.
      Yaya gajeje ta katseta da faɗin, “Ai tsautsayi dai baya wuce ranarsa, sannu kaji Abdul ka daina gudu wannan gidan naku dake cike da kayan santsinnan, ni kaina babba idan ina tafiya wlhy a hankali nakeyi dan ji nake kamar zan faɗi”.
     Dariya Karima da A'i sukayi, Zinneerah taɗan murmusa da zancen Yaya Gajejen tana maida hankalinta ga little. “To gudun mi kakeyi?”.
      Baki ya tura gaba yana makalewa bayan Karima. “Daddyna yace nakiraki zaije anguwa”.
       “Naji to, kace ina zuwa”.
  Sai da little ɗin ya fita ta duba Mama A'i. “Mama an gama haɗa abinda ya rage ɗinne?”.
       “Eh an gama maman Abdul, harma na miki karanbani na shirya a tray ”.
      “Kai aiko ngd aiba karanbani bane”. Zinneerah ta faɗa tana mikewa. Fita tayi domin kai masa kayan breakfast ɗinsa.

         A falo ta samesa zaune yaci gayu cikin ɗanyar shadda ash, yana zaune a dogon kujera little a kusa dashi yana duba masa ƙafarsa da yaji ciwo. Koda tai sallama bai ɗagoba har ta karaso inda suke ɗauke da tray ɗin. “Barka da hutawa”.
     “Barka” ya amsa mata yana ɗan dagowa ya dubeta. Duk yanda yaso maida idonsa ga ƙafar little ɗin kuma sai ya kasa. tai ɗan murmushi da ɗauke kanta ganin kallon da yake mata. “A ajiye nan ko dining?”.
      Lumshe idanun yayi ya ɗan buɗe a kanta, cikin kasalar data samesa yanzu yace, “Ajiye anan kawai”.
    Saman centre table ta ɗaura tray ɗin da duban ƙafar little dake cikin hannunsa. “Shi kuma wannan miya samu ƙafar tasa?”.
    Iska AK ya ɗan furzar. “Yace faɗuwa yayi ga waje harya fashe, taimakemu da man zafi ma a ɗaki”.
       Bedroom ɗin nasa ta nufa tana faɗin, “Maganin mai gudu kenan idan yana tafiya”.
      Murmushi kawai AK dake binta da kallo yayi, dan a kwankin nan data haihu duk ramar nan ta ciki da tayi nan ɓacewa take, sai wani irin buɗewama takeyi alamar lafiya ta samu. Miƙewa yay yabi bayanta yanama Little gargaɗin ya jirasa ya dawo.

      Zinneerah na ƙoƙarin fitowa sukaci karo, baya ta koma tana faɗin, “Ouch Yayanmu zaka fasamin kai”.
         “Kokuma ni zaki fasamin ba”. Ya faɗa yana matsota. Kallonsa take da mamaki, ganin dai da gaske kanta yayo tai saurin faɗin, “Yayanmu wani abu ya farune?”.
       “Faffaruwa ma madam” Yay maganar yana kamo hannunta da jawota jikinsa. Hancinsa ya cusa cikin wuyanta yana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login