Showing 144001 words to 147000 words out of 223329 words

Chapter 49 - Makauniyar Kaddara Hausa Novel Complete

21 Nov 2024

1204

suka shigo mota ta haɗiye abinta tana musu sannu. Duk amsawa sukai yana tada motar, daga haka sai gidan mmn sadiq da Zinneerah taita mamakin tayaya ya sani?.

    ★★

  Tarba suka samu maiban mamaki daga mmn sadiq da maman halima. ashe hajiya iya ta sanar musu da zuwan nasu, shiyyasa mmn sadiq datai niyyar zuwa dubata yau dole ta haƙura. Zinneerah kam ai tuni ta faɗa jikin mmn sadig tana murnar ganinta ita da mmn halima. hakan datai har sai da ya bama AK mamaki dan baiyi zatonta hakaba. Kasancewar Abba na gida yana jiransu a falonsa aka sauke AK, su Hajiya iya kuwa da mmn sadiq keji kamar ta goya suna a sashenta.
        Duk yanda mmn sakina taso nuna halin nata garesu saita kasa. Dan wani cika mata ido sukai dole ta kama kanta harda zuwa ɗakin mmn sadiq gaishesu. Ai kam sun amsa mata da fara'a da mutuntawa, hakan da sukai kuma sai ya ƙara musu kima a idonta da shakka. Mmn halima ma cike da girmamawa tazo ta gaidasu, Hajiya iya nata sanya mata albarka dan bata manta da fuskartaba taje mata gaiauwar Inno.
        Saboda zuwa nan hajiya iya dama taƙi cin abinci, dan ta taho da shirin cin abincin gidan ɗiyar tata. Aiko taji daɗin samun masa da mmn sadiq tai musu, sai gashi daga ita har Mommy sunci sosai suna godiya. hakan yasa Mmn sadiq ƙara jin daɗi da nutsuwa. Dan koba komai ai sun bata kimarta. Zinneerah kam tuni tana sashen mmn halima ta barsu dan su sake da kuma kasancewarsu manya a gareta.
    Da wannan damar mmn sadiq da baƙinta sukai hirar zuminci da tattaunawa game da labarin da Zinneerah ta bama hajiya iya da kuma abinda ya faru akan zancen little da maganar ɗaurin aurenta. Harma da shirye-shiryen tariya da a take mommy ta tabatar musu ita ta gama shirya komai rana kawai suke jira insha ALLAHU.
    Hawaye sosai mmn sadiq keyi har sai da hajiya iya ta shiga lallashinta.
     Sai da akai sallar la'asar Abba ya shigo gaida su hajiya iya tare da AK da shima yaci masa sosai dan yana sonta, ya kuma sha zoɓo shima. Sun gaisa cikin mutunta juna, suka ɗan ƙara tattaunawa har zuwa kusan biyar da rabi sannan sukai haramar tafiya.
    Sai kuma ga Zinneerah tai ƙwalkwal da idanu na kewar hajiya iya da zatayi duk da dai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu zata koma. Sau biyu suna haɗa ido da AK da tuni ya shige mota ta mirror ɗin waje, daga ƙarshe dai ta matsa daga saitinsa tana ɗaga musu hannu.

    Tafiyarsu da mintuna basufi talatinba su Sadiq suka dawo gida. Ganin Zinneerah suka haukace da murna suna tambayarya ina little ɗinsu?, su dai sunyi kewarsa dan ALLAH a dawo musu da abinsu. Dariya kawai take musu dan ita dai wannan ba huruminta baneba ai. Tunda batasan yaje canba itama ganinsa tayi.
     Bata samu zama da mahaifiyartaba sai dare bayan yaran sunyi barci, kasancewar ɗakin mmn sadiq ɗin zata kwana suka sami damar yin hira, yayinda mmn sadiq ketama ƴar tata nasiha a kaikaice akan aure da muhimmancinsa da darajojinsa. Ita dai Zinneerah saurarenta kawai takeyi bawai fahimtar dalilin yinsuba. Sai dai suna shiga kwakwalwarta tana kuma ƙoƙarin adanawa da fatan yin aiki dasu a duk sanda ƙaddara ta tilasta mata yin aure dan bata kawosa a lissafinta sam. ita kullum lissafi da budget ɗinta akan karatune mai zurfi kawai.
     Washe gari ma bayan tafiyar su Abdul skull sake zaman hira tayi da mamanta. A yau ɗinma hirar ta kasance kusan duk nasiha da dabarun zaman gidan aure koda da kishiya. Harma dai takai abin ya fara bama Zinneerah mamaki amma saita danne a ranta kawai.

     Karfe huɗu dai-dai sai ga Ni'ima da driver sunzo ɗaukarta, jitai kamar ta fasa kuka. Amma jin mmn sadiq tace zasuje taron biki Danya kuma harda ita nanda kwanaki tara yasa taɗanji daɗi a ranta har fuskarta ta nuna. Bayan ta gama matse-matsen hawayenta ta shirya suka wuce ɗauke da madaidaicin botikin gullisuwa da mmn sadiq ɗin tai musu.
          Koda suka iso gidan cike da murna suka tari juna dasu Bahijja daketa mata ƙorafin basusan zataje wajen mama ba da sun bita. dan sai da su Mommy suka dawo suka sani. Haƙuri ta basu kawai, daga haka suka shiga hidimar cin gwullisuwa kuma.

         Ana idar da sallar magrib hajiya iya tai baƙuwa. Bayan sun shiga ɗaki kusan awa ɗaya aka kira Zinneerah, kai tsaye hajiya iya tace mata ta shirya zasu tafi da baƙuwar gidanta. Mamaki ya kama Zinneerah, amma ganin yanda hajiya iya ta fiske dole itama ta shanye mamakin nata.
     Bayan ta shirya Hajiya iya ta jata gefe tai mata ƴar nasiha da gargaɗin duk abinda akai mata a inda zataje kartai jayayya, karkuma tai wasa wajen koyon komai ɗin. Ta amsama hajiya iya da girmamawa ita dai tana matsar ƙwalla, dan hankalinta ya tashi jin wai sati ɗaya zatai acan, a hakanma hajiya fadi take waje ya ƙure ba haka tasoba.

      Zinneerah naji na gani ta tafi tabar su Meenal tana hawaye suma sunayi tamkar masu rabuwa har abada. Hajiya iya kanta sai da taji kewarta, to amma wannan shine kawai gatan da zatai mata ta miƙata wajen kwararrun mata ta fannin sanin gyaran jiki da wasu sirrika irin su hajiya Falmata su gyara mata ƴar jikallen tata. Dan idan tai dubi da abinda ya faru da kuma kishiya irin Farah saita ƙara jin wannan shine gatan.

      Koda suka iso gidan hajiya falmata bata tsaya sanyaba saboda gargaɗi da sharuɗɗan hajiya iya akan irin salon gyaran da take buƙata aima Zinneerah ɗin, itako hajiya falmata dama aikinta kawai ta sani batasan wasaba. Musamman ma aiki irin wannan na manyan mutane kamar su hajiya iya da suke alaƙa tun zamanin ƙuruciya ba abinda zatai sanya bane. Dan haka tun a ranar ta fara gyara Zinneerah daga isowarsu gidan ko hutawa batama bari sunyi zaman yiba. Tun Zinneerah na kallon abin wani iri hardai ta fara jin yana shiga jikinta da sha'awarsa ganin yanda ta fara canjawa da ƙamshi mai kama jiki da gogewar fata a cikin kwana biyu.
       Babu abinda ke damunta sai kewarsu Jamal da hajiya iya dan ko abinci da ake bata na musamman ne. Hajiya Falmata kuwa nata aikinta da koya mata abubuwa kai tsaye har kunya na neman kashe Zinneerah da ganin hajiya falmata zata iskantar da ita shekarunta basu kai ba. A ranta kuma tana mamaki yanda ake mata magana mai kama da harshen damo akan aure da zamantakewarsa. Ta rasa wannan dalili itakam, takumayi alwashin bazata tambayaba zata cigaba dabi da ido da kuma saurare.

      A Ɓangaren su Hajiya iya kuwa Zinneerah na barin gidan aka ware fara tsare-tsaren biki da maganar invitations dan hajiya iya da Baffah fa shiri suke gagarumi kodan ƙular dasu Mammah dake can hotel suna jiran tsammani daga mai bincike, AK kuwa daketa ƙoƙari akan aikin shinkafarsa yana sane dasu, dan tuni yasa aka bincika masa inda suke, ya kuma shirya ɗaukar mataki akan Farah data bijirema maganarsa.
     Akan gyaran gidansa kuwa Dr Mahmud da Huzaifa ne tsaye akai duk da gidan bama taɓa zamansa Farah tayiba. Garamashi yankan zauna lokacin da yake shigowa ƙasar a munafunce.
     Ranar da Zinneerah ta cika kwanaki huɗu wajen Hajiya falmata lefen da Momie ta haɗa gudunmawarta ya iso, sai kuma ga Adilah da Mahma daga london suma sun iso da nasu kayan lefen, dan AK na sanar da ita komai bai ɓoyeba, takuma bashi goyon baya ɗari bisa ɗari.
     Zokaga yanda Adilah ke murna da farin cikin kasancewarta cikin ƴan uwa. mahma kuwa abinci kawai taci anan taɗan huta ta nema inda su Mammah suke, dan bata son ita kanta su san da maganar auren har sai ranar tariyar insha ALLAHU..............✍


*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_

*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_

*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_

*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍




*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

*_TYPING📲_*


*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*


*Page 48*

__________________________


Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗

Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali
Ina masu pimples
Tabo(spot)
Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance
Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba

Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki

Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu
Sannan munada beauty kit🤗duk me bukatan (flawless skin/perfect glow) toh yy kokari yamallaki set dinnan wn zncn baa mgn🧚🏻‍♀️cuz duk inda kayi se ankalleka😀
Buh gsky wnd besan yy haske karyayi using set din cuz gsky yn sa haske buh bn bleaching ne b zaidai murje fatane nd bring out that hidden beauty in you😍

Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself
100%tested nd trusted
Beauty kit:11k
Soap price:3k
Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free

Maiso kindly message 08062991549
Call 08064532391

Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏

Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝

Mg's skincare

_________________________

*Page 48*

...........Lefe kam yayi sai dai makiyi ya kushe, dan daga na Momie harna Mahma sai dai ace ALLAH ya saka musu da alkairi, da AK yace sunyi yawa akai ɗaya Baffah cayay duka za'a kai, idan yay wasama shima sai ya haɗa nashi dole an haɗa an kai. Dole AK yay gum da bakinsa dan yaga waɗanan iyayen amaryar sai da lallaɓa.
      

     Kamar yanda ake shiri gagarumi a shira's family da gayyatar dangi lungu da saƙo hakama su mmn sadiq suke nasu shirin, dan tuni Gwaggo Maryam ta iso kano sun ɗinke itada ƴar uwarta suna shawararsu, hakama Abba ba'a barsa a bayaba wajen gayyatar dangi da shirya yima Zinneerah kayan ɗaki duk da AK yace basai sunyi komaiba, dan koba shine ya auri zinneerah ba dole shine mai mata kayan ɗaki matsayinsa na babban yaya.
         Lokacin daya ambata hakan murmushi kawai Abba yay da sanya masa albarka, a zuciyarsa yana mai jin daɗi da taya Zinneerah samun miji irinsa.

   A danya ma baba shirinsa yake da ƴan uwansa batare da sanin Inna ba, dan Baffah da kansa ya kira Baban a waya ya sanar masa hukuncin da hajiya iya ta yanke akan tarewar, baba baiji komaiba yace ALLAH ya kaimu. Daga haka suka fara shirye-shirye.
     Akan zuwan su mmn sadiq can kuwa har agama biki sun gama magana da Abba. Dan ana gobe tariya can zataje, danginsu na ɗanmusa ma acan zasu sameta, idan za'a ɗakko amarya washe gari su biyota zuwa kano insha ALLAH.

     Zinneerah dai nacam nashan gyaran wajen hajiya falmata lungu da saƙo, ita kanta tasan ta gyaru sai dai Alhmdllh, har tsara yanda zataima su meenal yanga take a ranta tana murmushi. Sai dai kuma iya hasashenta ta rasa dalilin wannan gyara haka, duk da yanda hajiya falmata kan zauna tana mata lectures akan abinda ya shafi aure kan tsunduma zuciyarta a dogon tunani da nazari. Har takan tambayi kanta anya ba aure akai mataba kuwa?. Rashin samun amsa ke sakata jefar da tunanin ta kama wani daban.

    A randa Zinneerah ke cika kwanaki shidda gidan hajiya Falmata aka kwashi akwatinan lefenta zuwa gidan Abba. kasancewar ansan da zuwansu sun sami tarba mai ƙyau duk da dai daga nan Danya zasu wuce. Sai da aka buɗe kaya Abba dasu Mmn halima suka gani. Su mmn sakina ma dai sun shiga layin ƴan kallo suna haɗiyar zuciya, daga ƙarshe suna shiga ɗaki Sakina harda kukanta rurus. Ita kanta maman tasu kukan zucin take wanda yafi na fili ciwo dacin rai.
         Maƙwafta sun shishshigo suma suka sanya albarka kafin masu binsu Danya su kammala shiri su sake ɗunguma domin kaiwa can. Dole badan mmn sakina tasoba akai tafiyar da ita, itako mmn halima da yaranta biyu ai sune ƴan gaba-gaba, sai maƙwafta da ake gaisawar mutunci da matar Nazifi da suma za'aje dasu.
     A ƴan gidansu AK kuwa Mommy ce, sai Adilah data maƙale, sai Momie da Ummi, da su Aunty Khadija yaran Momie na farko su biyu. Sai matar Alhaji Yusif. Sai kuma mahaifiyar Dr Mahmud. Gaba ɗayansu dai mota huɗu sukayi harda ta kaya, suka tafi a jere gwanin sha'awa dan su Khalipha ne masu kaisun, karan farko da zaije tushen Zinneerah.
       Anan ɗinma dai ansan da zuwansu, dan sai da safe baba yake sanarma Inna, amaryarsa kuwa tasani kusan kwana biyu, da itama akai aikin abincin baƙin a gidan Gwaggo Laritu harda Yaya Gajeje ma.
     Ƙarfe ɗaya da wasu mintuna motocin su Khalipha suka shiga cikin garin Danya. Gidan maigari suka fara isa dan can su Haneef suka sani, daga can aka saka yaro musu rakkiya dan babu wanda yako fito a motama a cikin matan.
      Cike gidan yake da ƴan uwa domin amsar lefe, dawowar su Gwaggo Laritu gidan kenan su Mommy suka iso, an musu tarba ta mutuntawa da girmamawa, inna dai shigowar waɗan nan ƴan gayun matama neman birkitata yayi. dan duk iya jarabarta sai gata tai muƙus sai kallo da idanu.
        Gidan baba yasha gyara aƴan kwanakin nan, dan ɗakuna ya sake zubawa sabbi aka kuma siminte tsakar gidan tsaf, ga amaryar baba akwai tsafta dan tunda tazo gidan ya ƙara ɗaukar saiti. Musamman yau ma datai masa gyara na musamman ita da Sa'a. Dan jiya akai taron sunan Karima duk da dai baimayi wani armashiba. Sai uwar rigima da aka kwasa tsakanin dangin Babawo dana Inna. Saboda Babawo har yau baizoba yakumaƙi cewa komai, ita kuma idan an tambayeta sai tace bata masa komaiba.
       A ƙarƙashin bishiyar gidan aka shimfiɗa musu tabarmi dansu sha iska, aka kawo musu lemuka da ruwan leda da su baba suka tanada domin su kawai. Ba ƙaramin daɗi su Mommy sukaji ba a yanda aka tarbesu da girmamawa da mutunci. Bayan anyi gaisuwa da tanbayar iyalan juna aka shigo da akwatunan da suka saka ƴan uwa fara callara guɗe-guɗen da suka nema jefa Inna a hauka. Dan duk yanda taso ta daure ta kasa sai gata ta shiga zage-zage.
    Cikin mamaki da ɗaukarta mahaukaciya su Momie ke kallonta, yayinda su Gwaggo Laritu da sukasan hali basubi takantaba, sai maida hankali a murna da farin cikin Zinni tayi goshi da sukai, suna kuma yaddama Inna habaici akaikaice. Cikin ƙanƙanin lokaci gidan ya sake haukacewa da makwafta da yara ƴan kallo, dole aka maida su Mommy ɗaki dan suma su samu suyi salla. Su dai yanda mutan garin keta arerewa akan wannan lefe nasu sai abin ya ƙayatar dasu ainun, Adilah harda yin video dan ita kam wani ƙayatar da ita suke da sakata nishaɗi, sai washe baki take ranta fes.
      A waje ma dai yanda mata ke gudun shigowa gidan da yara sai abin ya dinga saka su Khalipha dariya, da birgesu. Dan suma suna zaune ne a ƙofar gidan a ƙarƙashin bishiya ni'imtacciyar iska na kaɗasu.
     Haka suka kasance a ƙauyen danya suna kallon yanda ake kai kawo akan ganin lefe. Sai da sukai sallar la'asar sukai haramar baro garin cike da alkairi da tukuyci, duk da sunƙi amsa Baba yace indai basu rainaba su amsa dan ALLAH. Jin furucinsa yasa dole suka amsa suna mai yaba ƙoƙarinsa da dattako. Daga haka akai musu rakkiya suka shiga motoci suka ɗauka hanyar tafiya kano akan sai kuma ranar juma'a sunzo ɗaukar amaryarsu da zata iso zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu itama.

         Koda suka taho a hanya labarin yanda al'amarin ya faru suketayi, dan sun baro Inna ta birkicema jama'a kamar sabuwar kamu a hauka. Duk da dai Yaya Gajeje da Karima na ƙoƙarin tausarta. Gida su mmn halima suka wuce, suma suka wuce nasu gidan inda suka kaima hajiya iya labarin farin ciki. AK na zaune a dining yana cin abinci shi da little yana jinsu, sai dai uffan bai tofaba bayan sannu da zuwa da yay musu.
    Adilah ce tazo inda yake bakinta a washe ta sumbaci little da tunda tazo take maƙalle da yaron, cikin sabawa daya farayi da ita ta bashi nata kumatun shima yay mata kiss suna dariya. AK dake kallonsu yay ɗan murmushi kawai batare da yace komaiba.
     Zama tayi tana fara bashi labari, tare da nuna masa video

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login