Showing 177001 words to 180000 words out of 223329 words

Chapter 60 - Makauniyar Kaddara Hausa Novel Complete

21 Nov 2024

1205

wayar kunnenta tai sallama murya a marairaice.
    Dariya Granny tayi daga can da cewar, “Inno irin wannan marairaicewa haka?”.
     “Granny nayi kewarki ne”.
“Nima haka Inno, shiyyasa nace Moddibo ya banike na karajin muryarki kafin na kwanta”.
      A take hawaye suka ziraro a kumatun Zinneerah, muryarta ta fara rawa alamun kuka. Kai kawai AK ya ɗan girgiza da mikewa tsaye, batare da yace komaiba ya zare wayar daka kunnenta....
     Da sauri ta kallesa dai-dai yana maida wayar kunnensa. Idanun nasa ya ɗan juya mata da faɗin, “Daga gaisuwa kuma sai ki samin ita kuka Granny? To an fasa gaisuwar dake sai da safe”.
      Da alama wata baƙar maganar ta faɗa masa daga can, dan janye wayar yay yana murmushi. Batare da yacema Zinneerah dake sharar ƙwalla uffanba ya raɓata ya wuce inda ta ajiye masa system ɗinsa daya bari a ɗakin jiya. Ɗauka yay tare da nufar ƙofa yana faɗin, “Ki kawomin lipton”.
        Baki ta kuma tunzurawa tana matso hawaye da bin bayansa da kallo harya fice, babu yanda ta iya dole bayan ta gama kukanta ta share hawayen da ɗaukar turare ta ƙara a jikinta, hardasu fesa much freshener kamar yanda Hajiya Falmata ta koya mata, ta ɗauka wani ɗan kwalban turare da batasan kona minene ba ta shafa a bayan kinnenta da wuyanta, kamar yanda Hajiya falmatan ta sanar mata ta ringa shafa shi duk dare idan tai wanka, ta kuma ƙara da khumra mai shegen daɗi da narkar da mai shaƙa.
     Daga haka ta ɗau hijjab mai hannu jaa ta saka sannan ta fito. Kitchen ta nufa ta ɗaura masa lipton ɗin da ganyen shayin da hajiya Falmata ta bata shima, rashin wayonta yasa batai tunanin ko ganyen shayin na wani abu baneba daban. A wani butar shayi mai azabar ƙyau daya ɗauka hankalinta ta juye tare da kananun kofunansa tasa biyu, sai ɗan bowl ɗin data zuba suger shima ta ɗora da tea spoon guda ɗaya ta ɗauka tray ɗin tana addu'ar ALLAH yasa tayi komai dai-dai.

         Yana zaune a doguwar kujera ƙafarsa a miƙe yasa filo da ɗaura lap-top ɗinsa saman filon. Koda tai sallama bai dagoba amma ya amsa mata a saman laɓɓa yana cigaba da aikinsa.
       Kallo ɗaya tai masa ta ɗauke idanunta, a centre table ɗin tsakkiyar falon ta ɗaura ƙaramin tray ɗin da jawosa kusa da shi tace, “Yayanmu gashi”.
     Ɗan ɗagowa yay yayi mata kallo ɗaya ya ɗauke kansa, a taƙaice yace, “Zuba”.
        Kanta ta jinjina masa kawai ta tsugunna gaban table ɗin tana ƙoƙarin fara zubawar, yanda hijjab ɗinta yay ɗan bula lokacin da take kaiwa tsugunne ya bama hancinsa damar shaƙo fitinannun ƙamshin turarurrukan data sakama jikinta, duk da tun shigowarta ya jisu, sai haka datai ya ƙara ƙarfinsu fiye da farko a cikin hancinsa.
     Wani irin harbawa zuciyarsa tayi, har baisan yatsunsa sun kauce wajen tafa saƙon shirme ba a system ɗin. Ya lumshe idanu ya sake buɗewa a kanta yana ɗan cizar lip dinsa na ƙasa.
     Zinneerah da batasan mi yake cikiba ta miƙo masa ɗan mitsilin tea cup ɗin irin na larabawa bayan tasa suga ɗaya dan tasan yanda yake so tunda yasha sata aikin sanda suna gida, tsaf ta gama haddace adadin da yake so.
       Idanunsa da suka canja launi lokaci guda ya zuba mata, dai-dai yana amsar shayin muryarsa a ƙasan maƙoshi yace, “Cire wannan hijjab ɗin banaso”.
       Mamakin maganar tasa yasata ware idanu sosai tana kallonsa. Sai dai yanda fuskarsa ke a ɗinke ya sata yin ƙasa da kanta ta hau ƙoƙarin cirewa tana haɗiye abinda ya tokare mata maƙoshi, dan duk da doguwar riga ce a jikinta tsananin kunyar zama take a gabansa a haka saboda santsin rigar yasa ta kwanta mata a jiki ta lafe, musamman da yazam ita da kanta ta rage faɗin rigar tun suna gida ita dasu Bahijja.
   Hannu ya miƙa mata alamar ta bashi, dole ta miƙa masa, kusa dashi ya ajiye hijjab ɗin dan son tabbatar da shike ƙamshin ko ita?.
      “Zauna”. Ya faɗa yana matsar da ƙafafunsa. Yanzun kam kasa haƙuri tayi sai da tace, “Yayanmu zanje na kwanta inajin barci”.
      “Nima ba gadin gidan zanyiba ai”. Ya bata amsa a daƙile.
     Tashi tai tsam ta zauna inda ya nuna matan har jikinta na neman hayemasa ƙafafu, tai saurin muskutawa kanta a ƙasa.
       Idanu ya tsira mata yana kurɓar shayin kaɗan-kaɗan saboda zafinsa. Amma dai haka yafi bukatarsa musamman wannan da yay masa matuƙar daɗi, ga wani irin ƙamshi mai daɗi dake fita a cikinsa.
       Ya fahimci ta matuƙar ƙwarewa da iya cuɗa hannunta cikin na juna idan tana waje a takure ko makamancin hakan. Ya danyi gyaran murya nason gusar da shirun nasu. Ɗagowa tai ta kallesa.
        Idanunsa a cikin nata yace, “Kin kira su baba ne? Kinji yanda su gwaggo sukaje gida lafiya”.
      Ya sosa mata inda ke mata ƙaiƙayi, atake idanunta suka ciko da ƙwalla ta girgiza masa kai. “A'a ai bani da waya ta ɓata”.
      “Ɓata fa? A ina kenan?”.
   Da damuwa sosai a fuskarta tace, “A can gida, tun lokacin da Granny bata da lafiya zaku wuce london”.
       Cikin ɗan taɓe baki yace, “Kin dai jefashi wani waje”.
     “A'a wlhy Yayanmu, nifa ina gama waya da Mama a ranar daga ajiyewa naje na tarosu na nemeta na rasa. har yanzu kuma ban ganshiba, kuma ko ina su Meenal sun tayani na duba”.
       “Uhm to wani ya sace kenan”.
Ya bata amsa cike da basarwa.
     Itako tace, “Amma kuma a gidan nan wazai saci waya?”.
            Wani ɗan murmushin daya bata mamaki taga yayi yana lunshe idanunsa. Cikin basar da maganar yace, “Ganyen shayin nan yanada daɗi waya baki?”.
      Badan taso barin waccan maganarba tace, “Hajiya Falmata”.
    “Wacece ita?”.
“Nima sai kwanan nan na santa suna mutuncine da Granny”.
       “Uhm! Itace ta baki wannan turaren mai ƙamshi haka?”. Ya faɗa murya a shaƙe dan shayin da yasha ya fara aikinsa.
     Rasa amsar da zata bashi tayi, sai ta ɗan jinjina kanta kawai.
    “Baki da baki ne?”.
“A'a kayi haƙuri itace ta haɗa, khumrah ne”.
       Komai bai sake faɗaba ya sauke lap-top ɗin dan aikin kam bazai iya cigabuwaba, ƙafafunsa ya zaro daga kusa da ita ya ajiye ɗaya a ƙasa ya tanƙwashe ɗayar, sake ɗaukar butan shayin yayi ya tsiyaya dasa suga ɗaya a ciki ya motsa. Cigaba da shan abinsa yayi da maida hankalinsa ga television. Itama gyara zamansa da yayi ya sakata jin ɗan sanyi ta koma kallon television ɗin da satar kallonsa. dan ya dage sai ɗora shayin yake hankali kwance. Daya shanye yake karawa, tanata lissafi sai da yasha kusa cups bakwai duk da dai ɗan mitsitsine kofin.
       Sai da aka kammala labaran da suke kallo ya miƙe, batare da yayi mata magana ba ya fice gaba ɗaya a sashen har tana mamakin ina zaije? Bata da mai bata amsa dan haka ta ƙudiri aniyar zaman jiransa ya dawo ita dai taje ta kwanta ta farajin barci.

     Shiko daya fita kai tsaye sashenta ya nufa, kitchen ya fara shiga ya kaso wutar can ya rufosa. ta Dining ma ya kashe tare da leƙa bedrooms ɗin dake a falon duk yaga akashe sannan ya nufi nacan ciki da take amfani da shi.
      Akwatin kayanta ya buɗe, duk da shi ba mutum bane mai buƙatar matarsa tasa kayan barci idan zasu kwanta tare ba, yafi buƙatar tazo masa a natural ɗinta, hakan bai hanashi ɗauka mata suba. Sai dai yau ba kamar jiyaba sai da ya zaɓo dai-dai da ra'ayinsa. Gaban Mirror ɗinta yaje nanma ya shiga shinshina turarurrukan wajen kamar mai neman wani daban. Sai dai abin mamaki ya kasa tantance wanda yake buƙatar jin, har takai ya fara buɗe kwalaben khumra dake wajen kusan kala shidda dan bama a kawo mata sauranba tukunna. Ya ɗan samu wasu a ciki, harya ɗauka biyu sai idonsa ya sauka akan kananun ƙwalabe dake cikin wani haɗaɗɗen kwandon saƙa na kaba da aka zubasu ciki kusan kala goma nanma. Murmushi ya danyi dan shi mutum ne mai son ƙamshi, ƙamshi yana ɗaya daga cikin abinda Farah tai galaba a kansa kenan dan itama gwanace wajen baza turare. Nanma shinshinawa ya ringayi ɗaya bayan ɗaya, sai dai ya kasa tantance wanda yafi daɗi da wanda yaji a jikinta. Sai ma neman rikita masa lissafi sukeyi. Nanma biyu ya zaɓa a ciki ya fice bayan ya kashe komai. falukanma duk kashe komai yayi ya rufe sashen baki ɗaya ya nufi nasa.

       Zinneerah da har ta gaji da jiran dawowarsa ta jingina da makarin kujera tana lumshe idanu ta buɗesu a hankali jin sallamarsa. Bataga mike hannunsaba dan kai tsaye bedroom ɗinsa ya nufa. Zamanta ta gyara da ɗaukar hijjab ɗinta ta riƙe a hannu gudun kar tai laifi.
    Babu jimawa kuwa sai gashi ya fito, batare da yay mata magana ba ya ɗauka remote ɗin tv ya kashe tare da nufar fridge, yana juyowa ɗauke da fura a hannu tana miƙewa. Fuskarta a marairaice tace, “Yayanmu zanje na kwanta barci nakeji”.
       Baiyi maganaba sai da ya karaso, ya ajiye roban furan da kamo hannunta ya zaunar. “Zauna kisha wannan sai kije ki kwanta”.
      Cikin langaɓe kai tace, “ALLAH yayanmu na ƙoshi barci nakeji kawai”.
        Harar daya zuba mata tasata ɗauka dan harya buɗe mata robar, cokalin dake haɗe da robar furan ta ɗauka ta fara sha a hankali tana lumshe ido dan barci takeji, sosai furan na mata dadi sai dai barci na neman kwafsa mata. Shiko lap-top ɗinsa ya ɗauka yana ƙarasa aikin nasa.
      “Yayanmu ALLAH ta isheni barci”.
Ɗan ɗagowa yay ya kalleta, yaɗan jinjina mata kai kawai yana ajiye lap-top din daya kashe gaba ɗaya. Miƙewa yay hannunsa ɗauke da remote na ac ya kashe. Sannan ya tattara wayoyinsa da nuna mata hanyar ɗakinsa.
      Sosai ta ɗan waro masa manyan idanunta dake cike da barci waje. Sai dai yanda ya tsuke fuska dole ta haɗiye abinda ke bakinta ta maida kanta ƙasa. Sum-sum ta fara tafiya hanyar ɗakin da bata taɓa shigaba. Kasancewar ya tsaya kashe fitila ta rigasa shiga ɗakin. Da wani ni'imtaccen ƙamshi tafara cin karo, ta ware idanunta sosai tanabin bedroom ɗin da kallo baki sake. Komai yaji masha ALLAH, white and golden kamar kaci dan ɗaukar idon mai kallo. Ga uban sanyin ac.
     Tana tsaye a wajen harya shigo bata saniba. Sai jitai kawai anyi sama da ita gaba dayanta. Sosai ta firgita sai dai babu damar yin magana. Bai direta ko inaba sai toilet ɗinsa da komai yake a tsare kuma a tsaftace. Dan shi kansa kamshi yake na musamman.
       “Kiyi alwala”. Ya faɗa kansa tsaye. Sabo da alwalar kwanciya barci yasa bataji komai a rantaba, gashi dama ko shafa'i da wutiri ma bataiba. Alwalar ta ɗaura yana kallonta cike da nazari, da alama yana tabbatar da ingancinta a fannin addinine ne. Sai da ta kammala shima ya ɗaura tasa suka fito tare kamar yanda yay mata alama da ido.
     Da kansa ya sa musu abin salla. Ganin yayi tsayuwar alamar jansu salla yasata kallonsa da mamaki. “Yayanmu nayi sallar isha'i”.
     “Nima nayi ai”.
Shiru tai bata ƙara maganaba harya tada sallar, itama tayarwar tayi dan bin umarni shine masalaha a gareta. Sunyi salla raka'a biyu suka ɗora da shafa'i da wutiri, sannan ya juyi ya dafa goshinta da ambaton.
*اَللَّهُمَّ  إِنِّي أَسْأَلُكَ خَيْرَهَا، وَخَيْرَ مَا جَبَلْتَهَا عَلَيْهِ، وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّهَا، وَشَرِّ مَا جَبَلْتَهَا عَلَيْهِ*
*_Allahumma innee as-aluka khayraha wakhayra ma jabaltaha 'alayh, wa-a'oothu bika min sharriha washarri ma jabaltaha 'alayh._*
        _Ya ALLAH ina rokon Ka laherinta da alhrin da Ka dabi'antar da ita a kansa, kuma ina neman sarinka daga sharrinta da shaarrin Da ka dabi'antar da ita a kansa._
      Lumshe idanunta tayi tana sauraren daddaɗan muryarsa mai cike da kamun kai da nutsuwa. Bayan ya kammala ya juya da ɗaga hannayensa sama ya cigaba da kwararo addu'oi kala-kala da harshen larabci.
       Sai da suka kammala addu'ar ya juyo yana fuskantarta da ƙyau. Tambayoyin ya fara mata a fannoni daban-daban daya shafi addini, wasu ta amsa wasu tace bata saniba dan a yanzu take kan neman ilimi, danma Alhmdllh batai wasaba akan hakan tunda ta dawo da zama kano.
     Ya gamsu da yanda tayi ɗin, ya kuma karba uzirinta, daga haka ya miƙe yana magana batare daya kalletaba. “Ga kayan barci nan ki canja”.
    Yana fa ɗaya yana nufi hanyar toilet. Kaɗan ya rage Zinneerah ta saki kuka amma ta dake ranta fal tsoro. Kenan anan zata kwana tare da shi yau ma?. Ta ayyana a ranta. Sanin bata da mafita kuma baya maimaita magana, gashi batason ya fito ya sameta batai abinda yaceba yasata ƙoƙarin canja kayan. Ganin turarrukanta tare da kayan ta mulke jikinta dasu duk da kuwa ƙamshin take dama. Tana gamawa yana fitowa ɗaure da towel jikinsa nata raɓar ruwa. Ƙasa tai saurin yi da kanta tana gyara zaman hijjab ɗinta data ɗora saman kayan barcin. Komai baice mataba ya hau tsane jikinsa da towel ɗin daya ratayo a wuya.
    Da wannan damar ta wuce toilet ɗin nasa sumi-sumi danyin brush tunda taga sabbi a toilet ɗin, dan ta tuna Hajiya Falmata tace duk rintsi karta kwanta batai brush ba, idan da dama ma ta haɗa da much freshener, sannan ta tabbatar duk sanda zata kwanta barci tayi tsarki da ruwan ɗumi koda ace ta yini amfani da shine.
      Brush ɗin ta farayi, sannan tai fitsari dayin tsarki da ruwan ɗumi. Much fresheners ɗinsa data gani ajiye a ɗan drawer ɗin glass ɗin toilet ɗin ta ɗauka, dan gasunan kala-kala, banana, cucumber, kai kala-kala ta fannin fruit duk gasu nan. Son da takema S...barry ya sata ɗaukarsa shi da banana ta saka sannan ta fito cikin sanɗa, a ranta tana addu'ar ALLAH yasa ya gama shiryawa dan shiyyasama ta daɗe danta bashi dama.
     Tsaye ta iskesa gaban mirror sanye da wando 3quarter iya cinya da riga mai buɗaɗen ƙirji farare tas. Yana fesa turare. Ta madubi yake kallonta harya kammala sannan ya juyo...........✍

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_

*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_

*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_

*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍




*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

  *_TYPING📲_*


*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

*Page 58*
________________________


*_KAƊAN YA RAGE SU ƘARE_*


*_MATA ƴan ƙwalisa kuna ina za'aci kasuwar sama babu ku?. Mg's skincare ɗin fa na gab da ƙarewar kaya kuna nan sake da baki baku mallaki naku ba_*


_Mg's SKINCARE nagartattun kayan ne dake gyara jiki da fata cikin sauƙi, sunada inganci da rahusa dai-dai da aljihunku._

*Da kin fito a ringa ga tauraruwar taurarin nan mai fatar da babu kamarta tamkar dinare abin haske da walwali.*

*_Sabulunsu kawai kika ɗana sai kinsan kin kai kuɗinki inda babu asara balle dana sani_*

_A yanzu haka muna jerin kayayyaki da suka rage kamar haka_👇🏻

Available

_Akwai: herbal whitening black soap 3k_
Akwai: beauty kit 11k shi set ne yakunshi Abu 6
Soap
Body cream
Face cream
Body nd face scrub
Cleanser
Glow oil

Location
kaduna buh mn tura Kaya ko Ina saidai inmutum ya amshi kayanshi zebada kudin delivery

WhatsApp 08062991549
Call 08064532391

Instagram:glow_with_mgs

Facebook:mg's skincare

*_Karku bari ayi babu ku guys, siyan nagari maida kuɗi gida._*

________________________



*Page 58*

...........Gabanta ya tako a hankali, ya tsaya tamkar zai shige mata jiki. Baice komaiba sai kama hijjab ɗin jikin nata yay ya zare. Ganin yanda ta duƙar da kai ya sashi saka yatsunsa biyu ya ɗago haɓarta. Ba karamin firgita tai ba da ganin yanda ƙwayoyin idanunsa suka canja launi tamkar wani bugagge. Muryarsa a shaƙe matuƙa tamkar mai mura yace, “Turaren nan naki zai kashe ni kairunnisaa”.
       Sosai jikin Zinneerah ya hau rawa saboda kusanto da fuskarsa da yay gab da tata, ya ɗaura hannayensa duka a kafaɗarta ya fara tafiya dasu a hankali zuwa gaban gadon, gwiwar ƙafarsa ɗaya ya ɗaura a bakin gadon, hakan da yay ya daidaita tsahonsu. Ya cusa fuskarsa akan dokin wuyanta yana wani jan numfashi a fisge dan neman ƙwace masa yake.
       Yanda ƙamshin turaren ke neman zauta masa ƙwaƙwalwa baima san bakinsa ya suɓuce wajen fallasa asirin zuciyarsaba yace, “Ina ƙaunarki da komanki Neerat”.
    Yay maganar da in ina jikinsa na wani ɗan tsumar da shi kaɗai yake jinsa a jininsa. Dan ita Zinneerah ma ruɗewar datai da salon nasa batasan ta fashe masa da kuka ba. Babu alamar ya jita, dan luuuu yayi dasu suka faɗa saman gadon. Babu shiri ta kanƙamesa jikinta na ɗaukar rawa jin harshensa akan kunnenta.
      “Na shiga uku Yayanmu Please ”.
Ta faɗa cikin muryar kuka tana ƙoƙarin ture fuskarsa dan neman sakata yin fitsari yake.
    Al'amarinne yazo mata a bazata, gashi farko, gashi da mutum mai matukar girma da daraja a idonta, gashi ta sha gyara na musamman da ita kanta ko yaya akai mata wani salo sai jininta ya motsa.
       “Shiiiiii!!!”
Ya faɗa a cikin kunnen nata yana zagaya yatsansa saman bakinta. Tsit tai shiru tana haɗiyar zuciya. A nutse ya ɗago fuskarsa yana kallon tata cikin ɗan hasken fitilar ɗakin green.
      Kasancewar idanunta a lumshe suke batasan kallonta yakeba,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login