Showing 111001 words to 114000 words out of 223329 words
Hankali tashe Mammah tace, “Am so sorry baby na. Ai bazan jimaba zan dawo kodan saboda halin da ake ciki. dan yanzu hakama na kammala tura kaya Morocco. Na Nigeria suka rage kawai insha ALLAH. Amma mi kikajeyi gida? Wane kuma irin tashin hankali kike a ciki?”.
“Ƙannen Yah Abdull ne suka zo jiya, harda yarinyarnan mara kunya data jimin ciwo a ƙafa. Mammah duk bama wannan ba. Wlhy Yah Mutallab ya haifi yaro da wata a waje kokuma yayi aure a ɓoye bada saninmuba”. Ta ƙare maganar da fashewa da kuka.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Farah wane irin maganane wannan? Ya haifi ɗa da watafa? Ke waya faɗa miki? Wacece ita wadda ta haifi ɗan kuma?” Mammah ta faɗa itama cikin tashin hankali.
“Mammah wlhy nima ban sanba. Yanzun nan naga yarinyarnan tana waya da yaron da Moos'ab, shine Moos'ab ɗin ya sanarmin yaron na Abdul-Mutallab ne, kinga kuwa indai ba'a waje wata ta haifa masa shiba wlhy aure yayi a ɓoye bamu saniba. Indai hakan ta faru mutuwa zanyi Mammah
“Kai ina!! Duk rintsi bazan bari hakan ta faruba Farah, dan wlhy har abada bazanyi sakacin da Kabeer zai ƙwacemin Abdul-Mutallab ba. Nayi alƙawarin tarkon da suke ganin zasu ɗana masa ya faɗa bazan bari yayi tasiri ba, dan haihuwarki itace kawai raba gardama a tsakaninmu. Kinga kuwa hakan na nufin babu wata mace data isa zuwa ta haihu da Abdul-Mutallab a ɓoyema ban saniba. ki kwantar da hankalinki yau ɗin nan zan baro china kuwa, dan bani da wata nutsuwar zaman yin abinda nazo yi ɗin”. daga haka ta yanke wayar.
Faɗawa Farah tai saman gadonta tare da fashewa da kuka mai cin rai, ji take tamkar numfashinta zai rabu da gangar jikinta, dan inhar wannan ɗan ya tabbata na Abdul-Mutallab tasan ita kam rayuwarta tazo ƙarshe. Kenan bayan ita ya taɓa sanin wata mace a duniya? Ya taɓa dai-daita farin cikin da yake bata da wata mace? ‘Kai ina wlhy hakan bazai yuwuba’ ta faɗa a fili tana fashewa da matsanancin kuka ta miƙe ta fito daga ɗakin.
Ficewa tai daga gidan dan ta rantse bazata sake kwana ba sai Mammah ta dawo sunji daga ina aka samo little. Ko kallon su Zinneerah dake falo zaune Farah batayiba ta nufi hanyar fita abinta.
Da kallo suka bita a tsorace. Cikin damuwa Jamal yace, “Gaskiya Yah Moos'ab baiyi tunaniba, miyasa shima ya faɗi cewar ɗan Yayanmu ne bayan yasan halin Aunty Farah da kishi. Gashi nan wannan maganar dashi yake gani yayi akan wasa gashi tana neman zama babba”.
Wasu hawaye ne masu zafi suka sake silaloma Zinneerah, dan ita a yanzu damuwarta daban da tasu, bataga laifin Farah ba, dan ko ita data haifi little har yanzu ta kasa fita daga ruɗanin kamannin da yakeyi da Yah Adnan. Balle ita dataga komai sama taka yau, ai komi tayi bai kamata aga laifinta ba.
Tunda ta haifi little yau shine karon farko data tsinci kanta a matsanancin tashin hankali tun bayan barowarta Danya.
Acan kuwa wajen su Hajiya iya an kira Moos'ab dan yayma Farah bayani akan wasa yake mata, Hajiya iya da Khalipha sun fito dan a bata wayar amma suka samu ta fice. Cikin damuwa suka sake shiga, dan ba ita kaɗaiba harsu Hajiya iya ganin kamannin yaron da AK ɗin sukai sosai fiye da kullum a yau.
Hajiya iya ta dubi Khalipha daya yanke kiran tace, “Ina Moddibon yake harya bari ta fita?”.
Kansa ya girgiza mata alamar bai sani ba. Sai su Bahijja ne suka sanar mata sungafa kamar ya fita.
“Fita kuma? To lafiya?”.
Hajiya iya ta faɗa. Khalipha da zuciyarsa ta bashi inda Yayan nasu yake yace, “Granny ina zuwa. Inaga yana baya, kinsan shi idan ransa ya ɓaci yafi bukatar ya killace kansa inda babu hayaniyar komai.
Batare da ya jira amsartaba ya fita shima. Kamar yanda yayi hasashe acan bayan ya samesa yanata kaikawo hannayensa goye a baya.
Harya karaso gab dashi baisan da zuwan Khaliphan ba, dan harga ALLAH kamanin yaron da shi ƙara gigitashi sukeyi, zai iya rantsewa tunda yaga yaron nan bai ƙara barci mai daɗi babu mafarkinsa ba. Dauriya kawai yake aɗan tsakanin nan har Hajiya iya ta samu lafiya. Amma da tuni ya koma Nigeria dan kawai yaga asalin mahaifin yaron nan shikam. Sai dai kuma abinda ya faru a yau ya ƙara tada masa tsumin ƙwaɗayin son zuwa Nigeria. Ko ita Farah jin gaskiyar zancen ya sakashi yimata uziri, dan inhar shi da yaron ke kama dashi zai iya rikicewa dolene ita yaga fiye da haka a gareta. Musamman daya santa da shegen zafin kishin tsiya, a yanzu babuma abinda zuciyarta bazata hasaso mataba game da yaron kamar yanda shi kansa duk da ance yaron ɗan Gwaggonsu ne zuciyarsa taƙi samun nutsuwa.
“Yayanmu”.
Khalipha ya kirashi cike da damuwa. Juyowa yay ya kallesa sai dai baiyi magana ba. Khalipha ya ƙarasa takowa garesa, kansa ya ɗan risinar ƙasa saboda abinda zai faɗa.
“Yayanmu kayi haƙuri, kar abinda aunty Farah keyi ya dameka. Dan ALLAH kumata uziri dolone ta shiga ruɗani kamar yanda muma ɗin muke a cikinsa tun ganin yaron da mukai a Nigeria, kawai dai ita matsalarta bata da nutsuwar zama ta fahimci abune”.
Karon farko AK ya saki murmushin ƙarfin hali, hannunsa ya ɗora bisa kafaɗar Khalipha ɗin. “Hakane bestie, Farah ta cancanci uziri a wajenmu, sai dai minene dalilin Moos'ab na cewa yaron nawane?”.
“Wlhy tsokanarta kawai yake Yayanmu, kasanshi duk da baida yawan magana yanada son wasa. Kuma inaga ya manta bataga yaronba a waccan ranar”.
Kai AK ya shiga jinjinawa yana sauke nannauyan numfashi, ya sauke hannunsa daga kafaɗar Khalipha yana maidasu bayansa ya harɗe. Taku biyu yayi batare daya juyo ya kalli Khalipha ba yace, “Bestie mi zuciyarka ke baka akan kamannina da yaron nan?”.
Babu shiri Khalipha ya kalli bayan nasa da sauri, haka kawai yaji gabansa ya faɗi, dan inhar gaskiya zai fito ya faɗa to komaima zuciyarsa na bashi musamman idan tunanin Zinneerah ce mahaifiyar yaron yazo masa arai kamar yanda yake zargi. Baki ya buɗe da ƙyar zaiyi magana Hajiya iya data biyo bayansu ta katsesa.......
“Wai tsayuwar mi kukeyi anan? Yarinyarnan fa bata gidan nan”.
Atare suka juyo suna kallonta. Takowa AK yay cikin tafiyarsa da babu gareje zuwa inda take, bai kawo wa take nufi ba dan haka yace, “Wace yarinya Granny?”.
“Matarka mana”.
Ɓoyayyen numfashi yaɗan sauke, a ransa yace ‘da sauƙi’ tunda yasan dai Farah ƴar garice bazata je wani wajeba sai gidan Mammah.
“Karki damu Granny babu inda zataje sai wajen su Mammah. Ya kamata mujema kisha maganinki”.
Daga haka ya kama hannunta suka nufi ciki Khalipha biye dasu. Basu sami su Zinneerah a falonba, sai mai aikinsu dake ƙara gyarawa. Har ɗaki ya raka Hajiya iya, ganin Zinneerah kwance a gado su Bahijja zaune jigum-jigum yasa Hajiya iya tambayarsu ko lafiya?.............✍
*_Masha ALLAH. Guys asha hutun weekend lfy ko😋😉😘😍😘😍🤗._*
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
*Page 36*
_________________________
_*YERWA INCENSE & MORE**_
_(The scents with diff essence for YOU& your HOME)_
_(MASARAUTAR KAMSHI)_
_Ina masu neman kayayyakin kamshi yan nahiyar ketaran chadi da Senegal? Kai harma da ingataccen had’i yan bornu? To ku matso domin nesa tazo kusa..._
_YERWA INCENSE & MORE: Sun zo muku da kayayyakin turaruka kamar haka:_
_Khumra kowacce Iri._
_Turarukan Wuta_
_Mopping khumrah_
_Washing khumrah_
_Bathing khumrah_
_body mist_
_kullaccam_
_scented hair cream/spray_
_wardrobe balls_
_carpet spray_
_air-fresheners_
_scented pebbles_
_body sprays_
_oil perfumes_
_Perfumes_
_kabbasa_
_burners_
_coal igniter_
_tong_
_kasko_
_kujerar tsugunno_
_english coal_
_dilke&halwa set_
_scented body mist_
_kai dama sauran kayayyakin da bamu ambata ba, YERWA INCENSE AND MORE, Na tura kayayyakin su ko’ina a fadin Nigeria da ketare. Domin tuntubar su. Suna instagram: _@yerwaincense_and_more. Ko _Facebook site:YERWA _COLLECTIONs. Ko a duba su ta number su: ___08095215215/09044191709! _
_suna bada kayan su kan sari ko sayi dai-‘dai_
_________________________
*Page 36*
..............Meenal ce tai ƙarfin halin faɗin, “Granny zazzaɓi ne a jikin Zinneerah”.
“Ya salam, zazzaɓi kuma?”.
Granny ta faɗa tana zagayowa inda Zinneerah take. Hannu ta saka a goshinta da wuyanta da sukai zafi rau. “Kai aiko jikin da zafi Inno, sannu kinji”.
Zinneerah da bacci-bacci ya fara figa ta ɗaga mata kai tana maida idanunta ta lumshe.
AK na tsaye yana kallonsu kamar baiji mi Hajiya iyan ke faɗaba. Sai da ta dubesa ne ya ɗan tako inda suke shima, kanta ya ranƙwafo yasa hannu yana cire bargon data lulluɓa. “Tashi zaune”. Ya faɗa ciki-ciki.
Tun matsota da yayi ƙamshinsa ya cika mata hanci, daƙyar taja numfashi lokacin daya ranƙwafota, duk da yanda taji maganar tasa gab da ita bata miƙe zaunen ba sai idanunta data rumtse da sauri.
“Baƙyaji ne?”.
Ya sake faɗa kamar bayaso.
Idanunta ta buɗe a hankali tare daja baya kaɗan daga kusa dashi, kafin ta yunƙura da ƙyar ta tashi zaune. Shima tsaye ya miƙe da ƙyau idanunsa a kanta. “Mike damunki?”.
Wani irin haushi tambayar tasa ta bata. Sai kace ba'a gabansa matarsa ta shaƙeta zata kashe ba yake wani mata wannan tambayar. Batare data yarda ta kalli sashen da yakeba ta nuna masa wuyanta.
Ɗan luu yay da idanunsa da gaba ɗaya suka canja kalarsu yana ɗaukesu daga kallonta. Batare da yayi maganaba ya fice a ɗakin su Bahijja na binsa da kallo.
Zama Hajiya iya tayi kusa da Zinneerah ta kamota jikinta tana mata sannu da duba wuyan nata. Duk da bata kasance fara tas ba ana ganin shatin hannun Farah a wuyan, saboda ba shaƙar wasa tai mataba. Gashi wajan kiciniyar ƙwaceta kuma duk an jijji mata ciwo da farce.
Shigowarsa shi da Khalipha ta sakasu kallonsu, Khalipha ya ƙaraso inda suke ya zauna a bakin gadon shima yana mata sannu. “Tashi ga magani kisha zai saki insha ALLAH”.
Babu musu ta tashi zaune ta amshi ruwa da maganin hannun Khalipha ɗin tasha. Tana gama sha kwanciya ta koma tayi jikin Granny. Hakan yasa ɗakin ɗaukar shiru na wani lokaci kowa da abinda yake saƙawa da kwancewa a cikin ransa game da al'amarin.......
*_DANYA_*
Koda su Inna suka iso Danya mahaifiyar babawo ta buƙaci wucewa da Karima gidanta amma sai Inna taƙi fir. Acewarta sai sunsan miya faru tsakanin Karima da Babawo koda hakan zata kasance. Badan innar babawo tasoba dole ta haƙura aka wuce da Karima gidan su Inna. Ita kuma tace zataje gida taɗan kimtsa saboda kwanan asibiti da sukai zata samesu daga baya dan tana son taɗan haɗoma karimar kayan kunu kafin babawon ya gadama yazo.
Baki amare Inna ta amsa mata tana jan hannun Karima suka shige cikin gidan.
Tun'a farkon shigowa gidan idanun Inna suka sauka akan Hajja lanti. Sosai ta waro idanu waje tana kallon hajja lanti da itama ita take kallo.
“Ni Asabe mi nake gani haka kamar hajja lanti? Idan mahwalki nake karku tadani dan ALLAH jama'a”.
Cikin dariyar yaƙe hajja lanti tace, “Ba mahwalki kike ba Asabe. Ni ce dai aminiyarki a zahirance walle”.
Jikin Inna na ɓari ta kwanto jaririyar Karima dake goye a bayanta ta mikama Sa'a data fito daga ɗaki dan yau anan ta kwana. “Ku shiga ciki, Sa'a kizo ki haɗa murhu asama ƴar uwarki ruwan wanka”.
Cikin ɗokin ganin baby Sa'a ta amsa tana ƙwalama Tinene dake barci a ɗaki ko sallar asuba batayiba kira dan tazo taga Baby. Karima kuwa ko gaida hajja lanti bataiba ta shige ɗakin Inna dan burinta kawai ta kwanta ta hutama ranta.
“Hajja lanti dama rai kanga rai?”. Inna ta faɗa tana zama a kusa da ita cike da jimami.
A raunane Hajja lanti tace, “Ba lafiya bace ta ɓoyeni ai Asabe, bayan ALLAH ma ya ƙaddara da sauran shan ruwana a duniya da ba wannan zancen mukeba anan”.
“Munga boni, mikuma ya hwaru hajja lanti? Dan ko baki hiɗi ba duk wanda ya dubeki yasan akwai damuwa, duk ƙibarkin nan ta zube kinyi baƙi”.
Hannu Hajja lanti tasa ta sharce hawayen da suka cika mata ido. “Asabe ai tun tahiyar danai da ɗiyar gidan nan abin ƙaddara ina baro garin katsina ashe ƴan doka na biye dani wlhy sukai ram dani aka sake maidani cikin garin katsina. Ashe wata matace dana ɗauka ɗiyanta a carachi tai shune na garesu”.
“Kai mun ɓitire. Hajja lanti kice kin auna arziƙi ke kau”.
“Bama ƙaramiba asabe, dan nahi wata biyu a wajen ƴan doka kahin su gaji da zamana wajensu babu mai belina suka mikani gidan yari wai zasu kaini kotu. Zancen da nake miki daga ranar babu wanda ya sake bi ta kaina ina gidan yari duk tsahon zaman nan. Sai shekaran jiya wani bawan ALLAH yaje ya fiddamu mu ɗari biyu”.
Sosai Inna keta faman tafa hannu tana sallallami da jajantama Hajja lanti dake matsar hawayen tuna azabar datasha a gidan yari. Sai da ta gama ƴan hawayenta sannan ta sake duban Inna. “Asabe yanzu abinda ya kawoni garin nan akan yaran dana ɗiba ne a tahiyar da nayi, dan nasan iyayensu hankalinsu a tashe yake. Nafara zuwa nan wajenki dan naji ko yarinyar gidan nan ta dawo ita kafin naje sauran gidajen suma naji yaya ake ciki? Dan naje can gidan hajiyar da nake kaima yaran a katsina na iske wai ta tahi saudia shekara biyu kenan”.
Ɗan waige-waige Inna ta fara, ganin su Sa'a har yanzu suna ɗaki tare da Karima dan Tinene ma ta fito tuni ta samesu. Ƙasa-ƙasa ta maida muryarta tace, “Ta dawo tun bayan mako uku da tahiyarku ai”.
Cikin zumuɗin dajin daɗi Hajja lanti ta ce, “Kai ALLAH na gode maka”.
Baki Inna ta taɓe tana gyara zama. “To ai baki saniba da ɗan ƙunshi ta dawo mana, nikuma a sanadinsa na kaɗa kanta tabi duniya yanzu haka ance tana birnin ikko ta kama ɗaki”.
“Kina nihin ciki tazo dashi Asabe”.
“Ƙwarai da gaske hajja lanti, dan ciki ma ya giyata ya hito duniya ta sani kahin nasata barin garin nan bayan na rihe bakin tambaɗaɗɗiyar gudun karta tona mani asiri dan na hiɗima duniya cewar yawan tazubar dama ta tahi tunda dagani sai ke mukasan yanda akai”.
“Amma asabe.....”
“Karkice komai hajja Lanti, dan kema kinsan komai akan tsanar ɗiyar nan danai, kinga can wajen” tai nuni da ƙasan turminsu na daka. “Acan na binne tsiyar, kinsan malam kallamu, shine yay mani aikin nan na rihe bakin kowane shege har abada kuma babu maiji, kema na hiɗi maki ne dan nasan abikiyar cin mushe ce. Kema kuma baki rihemani komai na rayuwarki”.
“Hakane Asabe. Amma ni abinda yaban mamaki ma a ina yarinyarnan ta samu ciki to? Kodai dashi ta tahi daman? Dan inda na kaita bawata harkar banza akeba, inbadai bayan barina ta samu wajen aiki ba acan komai ya hwaru”.
“Sudai suka sani lanti, ni dai tunda na kaɗata kuma bakin kowa ya rihe miye damuwata. matsalata kawai tahiyar malam adalilin barinta gida, amma inaji a jikina shima ya kusa dawowa gareni”.
“Ban ganeba yimani karin. bayani”.
Babu musi Inna ta shiga bata labarin komai tana matsar hawaye, dan tana son baba so mai yawa da itama batasan adadi ba a rayuwarta.
Sa'a dake laɓe a bayansu tanajin komai ta sharce hawaye da fitowa kamar batajiba ta fara haɗa wutar ɗorama Karima ruwan wanka kamar yanda innar tace. tana ƙoƙarin aza garwar wankan maƙwafta suka fara shigowa ƴan barka da ganin ƙwaƙwaf dan sai yanzu labarin dawowar karima gidan ya fara zuwa kunnuwansu.
Daga haka hirarta da hajja lanti ta watse. tashi hajja Lantin tai ma ta tafi bayan taje taga baby itama. dan mutane sai kallonta suke tunda ita ba ɓoyayya bace a garin dama tayi dillanci kafin fara ɗaukar yara tana kaiwa aikatau birni.
Ta tafine ranta makale da zancen Inna akan cikin Zinneerah. Itakam wahalar da taci a rayuwa yasa tayi nadama. Ta nunama Inna tana tare da itane kawai danta samu bakin zaren da zata taimaki Zinneerah. dolene saita koma katsina ta binciko ainahin gaskiyar abinda ya faru da ƴar mutane kozata samu kwanciyar hankali da nutsuwar zuciya. Yanzu hakama zataje sauran ƙauyikan data ɗakko waɗancan yaran ne dan taji sukuma yaya suke ne? Ta kuma nema gafarar iyayensu.
Firar Inna da Hajja Lanti tasa Sa'a kuka sosai a yinin yau, saboda ƴan barka daketa shigowa yasa taketa ƙoƙarin dannewa har dare ya rufa. Saboda ƙudirin dake ranta yasa yau tai shirin kwana a gidan nasu. Bata kwantaba kuwa har wajen sha ɗaya da ƴan barka suka gama shigowa Tinene ta dawo gidan. Kallonta kawai Sa'a tai ta watsar, dan ko uffan batace mataba akan ina ta fito ko taje. Tunda dama zance nata yawo a gari Tinene na yawon dare, amma ko an faɗama Inna saita karyata tace anama Tinene sharrine dan ba'a ƙaunarta.
Sai da taga Tinene ta kwanta sannan ta fito kamar zata bayi, ta Window ta leƙa ɗakin Inna taga duk sunyi barci ita da Karima da jaririya.
Kanta tsaye wajen turmin sissikar hatsinsu da inna ta nunama hajja lanti ta