Showing 108001 words to 111000 words out of 223329 words
“Lafiya lau muke, dan ganima tare da Little Handsome tun safe na ɗakkosa daga wajen Gwaggo yau a gidanmu zai kwana insha ALLAH”.
Idanu ta ɗan waro na mamaki, “Baka tsorin yay muku kuka Ya Moos'ab?”.
Maimakon ya bata amsa sai ya karo mata fuskar little ɗin yana dariya. “Hy Gentleman kalla Aunty a waya tana maka magana”. Ya faɗa yana sunama little wayan. Ɗagowa kuwa Little dake kokawa da chocolate yayi ya duba wayar, sarai ya gane Zinneerah dan haka ya washe baki cike da ɗoki yake faɗin, “Aunty! Aunty”.
Dariya sosai ta kama Zinneerah cike da jin daɗin ganinsa mai tsanani, idonta na tara ƙwalla tace, “Uhm su malami an ƙara wayo ashe?”.
A dai-dai nan Farah ta shigo kitchen ɗin cike da tafiyarta ta ƙasaita da isa. Dama kuma hango Zinneerah a kitchen yasata shigowa dan tanason jamata winning akan shigo mata kitchen. Wani irin mahaukacin bugawa ƙirjinta yayi lokaci guda har takalmin ƙafarta na neman kadata a ƙasa. Tai azamar dafe kitchen cabinet jikinta na rawa.
Harga ALLAH da farko ta zata AK ne akan waya saboda yanda Moos'ab ya sakama little wayar kusa da fuska sosai, sai dai data ƙara matsowa taga wannan yarone. Amma duk da haka wani irin jiri-jiri taji yana neman kwasarta saboda ganin matsanancin kamannin. Babu wani neman excuse ta ɗauka wayar cikin hannunta tana faɗin, “Wannan yaron wanene haka?”.
A yanda tai maganar, da tsoratar da Zinneerah tayi dan batasan da shigowarta kitchen ɗinba yasa Moos'ab maido da wayar kansa yana ɗaukar little ɗin yasa bisa cinyarsa tana ganinsu su biyu. Batare da tunanin abinda zai faɗa zai iya zama matsalaba yace, “Hy Auntynmu yaronmu ne. Bakiga yana kama da Yayanmu ba, shi ya haifa muna baku sani ba”.
Harga ALLAH cike da barkwanci Moos'ab yay wannan furuci, sai dai ya zoma Farah a bahagon tunani, dan babu shiri ta nema sakin wayar a ƙasa sai da Zinneerah ta tarota ALLAH yasa bata kai ƙasaba. Itako a take takai ƙasan saboda santain tiles dana takalmin ƙafarta. Wata irin gigitacciyar ƙara ta saki wadda ta saka su Khalipha da sam hankalinsu baya kansu maido dubansu wajen, kusan a tare suka kwaso da gudu zuwa kitchen ɗin duk da su basajin mi suke faɗa. Ihun Fara ɗinma dan tayi da ƙarfi ne yasa sukajita, gashi kuma tana ta wajen saitin ƙofa ne ma.
Shigowarsu tayi dai-dai da kaiwar Zinneerah durƙushe kanta, a kuma dai-dai lokacin numfashin Farah ya bar gangar jikinta alamar dai suma tayi. Ƙara ruɗewa Zinneerah tayi ta shiga jijjiga ta tana shafa fuskarta da kiran sunanta. Suma su Meenal duk ƙasa suka kai durƙushe suka shiga taya Zinneerah jijjigata ta.
Khalipha da shi kansa yake a rikice duk da ya fahinci suma tayi yama rasa taimakon da zai bata, sai da Jamal yay hikimar ciro ruwa a fridge shima a ruɗe ya mika masa sannan.
Yana ƙoƙarin ɓalle murfin gorar ruwan Hajiya Iya da AK suka shigo. Kuka da ihun su Meenal ya sakasu nufo hanyar kitchen ɗin cike da sassarfa.
“Ya ilahi, kuko yaran nan miya faru kuka cika gida da ihu haka dan ALLAH?”. Hajiya iya ta faɗa tana isowa inda suke.
Khalipha ne dake ƙoƙarin ɓalle murfin goran ruwan har yanzu ya kasa dan tsabar ruɗewa yace, “Granny Aunty Farah ce ta suma wlhy”.
“Suma?”.
Cewar AK da shima ya karaso inda suke. Ganinta kwance a jikin Zinneerah da har yau take jijjigata tana kuka ita dasu Bahijja ya sakashi tabbatar da e da gaske suman kuwa tayi, amsar ruwan hannun Khalipha ɗin yayi ya zuba a hannu ya ranƙwafo ta bayan Meenal ya shafa mata ruwan akan fuska har bisa hannun Zinneerah dake shafa fuskar tata.
A take ta kawo wani irin nannauyan numfashi. Ganinsu a kanta ta miƙe a zabure jikinta na rawa. Babu zato babu tsammani sukaga ta cakumi wuyan Zinneerah ta shaƙe. “Tsinanniya matsiyaciya. Dan ubanki yau sai kin faɗamin wacece ke? Ta gidan ubanwa wancan yaron ya zama ɗan mijina kuma?”.
Wani irin kakari Zinneerah ta shigayi dan ba ƙaramin shaƙa Farah tai mataba, ga Hajiya Iya na ƙoƙarin janye hannunta dasu Bahijja amma sun kasa. Cikin rufewar idanu AK ya sauke mata mari dan ganin tana neman masa kisan kai a gida, bayan yanzu ya gama ganin yarinyar na kuka iya iyawa saboda shigarta wani hali.
Azabar zafin mari ya saka Farah sakin Zinneerah babu shiri ta ƙwalla wata irin gigitacciyar ƙara da ta sakasu toshe kunnuwansu babu shiri. Banda Zinneerah datai baya ta zube riƙe da wuyanta tana ƙoƙarin jawo numfashi da ƙyar.
Saurin riƙota Khalipha yayi, yayinda Hajiya iya kuma ta riƙo Farah da take neman fita hayyacinta saboda gigitar mari da abinda kunnuwanta suka jiye mata yanzu a bakin Moos'ab.
“Wai nikam mike faruwane haka? Farah ki nutsu ki mana bayani, ya mun tafi mun barku lafiya kuma mu iskeku a wannan harmutsatstsen yanayin abin ban tsoro”.
Kasa magana Farah tayi, sai jikinta ke wani irin rawa ga hawaye na rige-rigen sauka, yanda ta tsire AK da kallo tana sake hango tsananin kamanninsa da yaron ya sake harmutsa tunaninta, sai kawai ganinta sukai a ƙasa ta sake sumewa.
Sake rikicewa sukai gaba ɗaya, dan shi kanshi yanzu al'amarin nata ya fara bashi tsoro. Duk da yasan halinta ta iya ɗaukar abu da girma amma na yau ɗin kamar yafi na kullum. Hajiya iya ce tace ya ɗauketa suje ɗaki kafin a ƙara saka mata wani ruwan. Baiyi musuba ya ɗauuta gaba ɗayanta zuwa bedroom ɗinta. Hajiya iya da Khalipha ne kawai sukabi bayansu, su kuma su Meenal suka kama Zinneerah suka tayar zuwa falo. Jamal kuma ya ɗauka mata ruwa a fridge yabi bayansu zuciyarsa fal mamakin miya kawo wannan tashin hankali haka?. Baida mai bashi amsa, bai kuma zaton samun amsar ga Zinneerah a halin yanzun ba.
A can ɗaki kuwa ruwa aka ƙara shafama Farah ta farfaɗo, sai dai tambayar duniya sunyi mata taƙi cewa komai sai uban kuka take dirza. Data kalli fuskar AK kuma ta hasaso ta little sai ta sake fashewa da wani kukan.
Sanin halin Farah da AK yayi ne ya sashi jan tsaki tare da daka matsa tsawar data sakata shanye gumjin kukan da take ɗin. “Ki nutsu karki maidamu wasu ƴan iska mana, ya ana taroki kina zillewa sai kace wata karamar yarinya?”.
“Wlhy bazanyi shiru ba, har sai an faɗamin ƴar iskar data haifi wancan shegen yaron da Moos'ab ya kira da naka, har wannan matsiyaciyar yarinyar ke magana dashi ta waya.....”
A fusace ya zuba mata wani shegen kallo daya sakata haɗiye maganarta babu shiri ta ƙanƙame hannun Hajiya iya dake riƙe da nata. duk da bai fahimci inda zancenta ya dosaba sai da gabansa ya faɗi, juyawa yay ya sauke idonsa akan Khalipha.
“Mike faruwa?”.
Kai Khalipha ya girgiza masa. kansa tsaye yace, “Wlhy ban saniba Yayanmu, nidai Moos'ab ya kirani ina ɗaki kwance yace na bama su Meenal waya su gaisa. na kawo musu ya gaisa dasu Jamal sai aka kaima Zinneerah wayar kitchen dan tana can kuma tare yake da little. Daga haka bamusan miya faruba sai ihun Aunty Farah mukaji kawai dan ko wucewarta kitchen ma ni wlhy ban ganiba”.
Batare da yace komaiba ya maida dubansa ga Farah dake kuka har yanzu kamar zata shiɗe. “Meya faru ke da kika shiga kitchen ɗin?”.
Wani irin kuka ta kuma fashewa da shi, tace, “Miya faru kuwa bayan ganin shegen ɗanka da nayi wanda kake ɓoyemin karna sani, a duk sanda nai maganar kanacin amanata da wasu matan a waje ka balbaleni da bala'in ina zarginka. Sai gashi ALLAH ya tona maku asiri ɗan uwanka yau ya fallasamin, ALLAH ya nunamin shege ɗan ƴar iskar yarinyarnan na waya dashi. Wlhy bansan haka kakeba Abdul-Mutallab, dana gwammaci dawwama banyi aure ba akan ganin wannan baƙar ranar........”
“Haba kekuwa ƴarnan wane irin kalaman rashin ɗa'a ne haka kike jefar mijinki dasu? Ni wlhy saima yanzu na fahimci daga ina matsalar take, halan yaron nan na wajen Hauwa'u ta gani?”.
Khalipha ne ya bata amsar cewa, “Eh shine kuwa Granny, dan Moos'ab ne yake can gidan ya ɗakkosa. To inaga sanda suke magana da Zinneerah ita kuma ta shiga kitchen ɗin ta gansu. Amma aunty Farah ya kamata kiyi haƙuri ai miki bayani, yaron nan baida wata alaƙa da Yayanmu sai ta zuminci, kamannine kawai da ga ALLAH b........”
“Ƙarya kakeyi munafukin ALLAH ta'ala, idan kai kaƙi faɗar gaskiya ai shi Moos'ab ɗin da bakinsa yace ɗansa ne”.
Hajiya iya da mamakin Farah ke neman kasheta tace, “Shi Moos'ab ɗin ya faɗa miki yaron na Moddibo ne?”.
A gadarance tace, “Ƙwarai kuwa”.
Yanda tai maganarne ya saka AK kaima bakinta bugu. sai dai da sauri Hajiya iya ta kare tana faɗin, “Kull da wannan ɗabi'ar, karka sake ka aro halin da ba nakaba kayi haƙuri abi komai a sannu harta fahimta. Kai Khalipha kiramin Moos'ab a waya yanzun nan”.
Amsa mata Khalipha yayi yana fita falo domin amso wayarsa a wajen su Zinneerah.
Dai-dai lokacin da Khalipha ke ƙoƙarin kiran Number Moos'ab kiran Baffah ya shigo wayar AK. Cike da ƙarfin hali ya ɗaga, sallama yay yana mai ƙoƙarin dai-daita muryarsa dake a cinkushe. Sai dai kuma yanda yaji muryan Baffah sai ya bashi mamaki.
“Kaga Babana haɗani da Inna”.
“Baffah lafiya kuwa?”.
“Karka damu lafiya lau, haɗani da ita”.
Cikin sanyin jiki ya mikama Hajiya iya wayar yana faɗin, “Baffah ne”. Amsar wayar tayi takai kunnenta. Batare da sunsan mi Baffah ya faɗa mataba ta miƙe ta fito daga ɗakin. Hakanne yasa AK miƙewa shima ya fito domin jin ko Khalipha ya samu Moos'ab. Dan shi kaɗai yasan irin hukunci dazai masa idan har yaji gaskiyar zancen.
Kamar jira suna fita kira na shigowa wayar Farah. Kamar zata share sai kuma ta duba wayar tana sharce hawaye. Wani irin zabura tayi saboda cin karo da sunan Mammah akan fuskar wayar alamar ta dawo kenan..............✍
*_Hummmm, tofa masu karatu ga wuri fa ga waina. Yanzu aka fara wasan kumuje zuwa😉🐥🐥._*
_Kar kuma naji wani yacema aunty Farah wani abu, kokuma na rage mudu ehe_🤒🤕😒☹️😖
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
*Page 35*
________________________
*ZAUREN GIRKI*
Abinci na *gargajiya* ...Kuka,Taushe,Danbu, Sinasir,Waina
Abinci na *zamani* ...Afang,Edikaikong, Coconut Rice, Ofada Rice
*Garabasa* ...Salads,Pancakes, Plantain mosa, Gyaran nama/kifi kafin girki,Shirin/shinfida abinci kan table.
• A kowane sati,in shaa ALLAAH, za a koyi miya/abinci daya da kuma wani abu ta karkashin *Garabasa* .
• Duk ranar *Lahadi* za fito da sabobin *videos* guda biyu na miya/abinci da na wani abu daga karkashin *Garabasa* .
• Kowacce daga cikin masu koya zasu bibiya video su kwaykwaya su gwada yin abincin bisa ga umurnin *video*
• Kowane ranar *Asabar* za a yi *Q&A* a inda kowa zai samu yin tambayoyi akan *videos* din satin daya gabata, da inda suke neman karin bayani/gyara akan kokarinsu na gwada abincin *video* da kawunansu
• Ga wace taga dama,daga ranar *Talata* za a iya fara turowan *video* ta kokarin da aka yi na kwoyon abincin da aka kwoyar ta *video* na ranar *Lahadi* .
• Inda akwai me bukatan wani fanni na abinci,ana iya hada *aji(Special Personal Video Classes)* musamman domin wannan bukatan.Anan za a shirya live *video* sessions domin cimma wannan burin
• Za a biya dubu biyu *(#2,000)* na watan farko,sannan za dinga biyan dari biyar *(#500)* ta kowane sati ga masu bukatan shiga group dinnan namu mai albarka
• *Zen Commute,account number 0119343451 Union Bank* ,asusunmu
• Duka lokacin da aka biya sai a turomana da hoton teller ko bank confirmation akan wannan number ta *WhatsApp 0817-541-7533*
• Ana iya tuntubammu akan wannan number domin karin bayani; **0817-541-7533(WhatsApp kawai)*
ZA MU FARA ZAUREN GIRKI LAHADIN SATIN FARKO TA WATAR SEPTEMBER,IN SHAA ALLAAH!
*MU TSARE MUTUNCINMU,MU KARE MAZAJENMU...MU KOYI GIRKI!!!*
_______________________
*Page 35*
............“Babangida duk ka rikitar dani wlhy, gani na dawo ɗaki ni kaɗaice yanzu mike faruwa ne?”. Hajiya iya dake zama a bakin gado ta faɗa.
Numfashi Baffah ya furzar daga can. Cikin nutsuwa yace, “Inna yanzu muka rabu da mijin Hauwa'u, kamar yanda na sanar miki dama munyi dashi yau zaizo yanada muhimmiyar magana”.
“Eh ƙwarai anyi haka”.
“Yauwa to Inna, maganar zancen yaron nan ne dai daya tsayamin arai mukayi dashi, ashe yaron ɗan wajen Zinneerah ne”.
“Uhm ban fahimcekaba dai babangida. Wace Zinneerah kake magana? Inno wai?”.
“Tabbas ita kuwa”.
Sosai zancen ya daki zuciyar Inno. Har sai da ta janye wayar daga kunnenta ta kalla, ta dai tabbatar da ɗan nata take waya ba wani dabanba dan haka ta mayar. “Babangida tayaya hakan ta faru? Dama Zinneerah ta taɓa aure ne?”.
“Bata taɓaba Inna. Ƙaddarar rayuwa ce takaita ga haihuwarsa....... (Anutse ya shiga yimata bayani dalla-dalla kamar yanda Abba ya sanar masa). Sai ga hajiya iya na hawaye shaɓe-shaɓe na tausayi. Dan har cikin ranta tanaji Zinneerah bazata aikata hakan da ganganci ba, dole akwai abinda ya faru dai......
Baffah ya katse tunaninta da cewar, “Inna harga ALLAH ta ɓoye-ɓoye ya ƙare, shin baƙya wani tunani game da kamannin yaron nan da Adnan kuwa? Adnan ba kama yake da yaran gidannan ba mahaifiyarsa ya biyo komai a kamanni balle muce ƙarfin jini yakai yaron Zinneerah da ɗakko kamannin yaran gidan nan. Shin kodai akwai abinda Adnan ke ɓoye mana ne?. Dan kwanaki sau biyu ana sanarmin shigowarsa Nigeria baizo inda mukeba. Nayi shirune kawai na ƙyalesa dan karna tayar miki da hankali”.
Babu shiri Hajiya iya ta miƙe tsaye tana ambaton, “Shi Moddibon da kansa?”.
“Wlhy kuwa Inna, ko lokacin da Khalipha yazo hutu tare sukazo”.
A take kan hajiya iya ya sake kullewa. Kamar yanda shima Baffah kan nasa yake a kulle. Dan sudai sunyi imani da cewar yanda yaron ya shiga ran kowa a gidan akwai wata a ƙasa. Sannan kamannin kam sunyi yawa, sai dai idan acan kuma dangin hindatu tushen matsalar take ba abinda zukatansu ke karkatar dasu akai bane.
Hajiya iya da takardar wajen mmn sadiq ta faɗo mata a rai tai masa sallama akan zuwa anjima zasuyi waya bara ta kashe wata wutar.
Tana katse kiran takardar ta ɗakko a inda ta ɓoyeta, ta sake komawa inda take zaune da ta warware.
*_Assalamu alaiki_*
*Alkairin ALLAH da samuwar lafiya mai ɗorewa su tabbata a gareki Gwaggo. ALLAH ya dawo mana dake gida lafiya*
_Gwaggo zan fara da baki haƙuri akan wani abu da muka ɓoye miki game da Zinneerah, munyi hakanne saboda ba abune mai daɗi ba ko farin ciki. Duk da dama dai munyi niyyar sanar daku ɗin harga ALLAH. Akwai ƙaddarar data faɗama Zinneerah wadda itace tai sanadin dawowarta zama a wajena, dan da tana can wajen mahaifinta da muka rabu...................._ _(Ta bada labarin tun aurenta da baban Zinneerah har bayyanarta da ciki a garesu da haihuwarsa kaf bata rage komaiba. Daga karshe ta ɗora da faɗin___). Yaro da mukazo dashi ranar da yara sukace ƙaninsune shine yaron, sunansa Abdul-Mutallab. Dan ALLAH ku gafarcemu da rashin sanar muku wannan labarin tun farko, bamun ɓoye bane dan bamu yarda dakuba. ALLAH ya hukunta sai yanzune zaku sani kawai. ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsahon rai mai albarka da amfani._
Sosai Hajiya iya taja wani irin dogon numfashi mai tafiya a sarƙe. Ko kaɗan bataga laifin mmn sadiq akan ɓoyewarba. Domin ko itace zata iya ɓoyewar bisa dalilai masu yawan gaske. Abinda kawai yake neman jefa zuciyarta a ruɗani irin wanda Baffaah ya shiga anan uku ne zuwa biyu. Shigowar sunan Khalipha a labarin da taimakon da yay ma Zinneerah a Shira hospital, Kamanin yaron da Abdul-Mutallab, dan wannan kamanni yakai ai zaman dogon nazari akansa.
Sannan har cikin ranta kuma tausayin Zinneerah da ƙarajin ƙaunar yarinyar ya ƙara faɗi a zuciyarta. Yarinya ƙarama kamar wannan ta fuskanci irin waɗan nan manya-manyan jarabawoyi na rayuwa. Amma abin mamaki ko'a labari bata taɓa nunama waniba, hakan na nufin itaɗin yarinyace mai yawan kamun kai da riƙe sirri, insha ALLAH kuwa zatayi wani abu, sai ta ƙwato mata haƙƙinta, dan har cikin ranta son yarinyar takeyi tamkar nata jikokin........
★
Daga ɓangaren Farah da kiran Mammah ya shigoma a waya. Wani ɗan karan daɗine ya tsarga mata. Tai saurin ɗagawa tana kai wayar kunnenta, dan har cikin ranta tana son Mammah kamar yanda itama take nuna mata soyayya.
Tana ɗagawa ta fashe mata da kuka, a rikice Mammah tace. “Auta lafiya kuwa? Miya faru da kuka haka ni hindatu?”.
“Babu lafiya Mammah, ina cikin damuwa da tashin hankali. Naje gidan jiya kawai na tarar bakyanan sai Mahma kaɗai, yau kuma sai ga tashin hankalin da yafi na jiyan ya riskeni”.