Showing 90001 words to 93000 words out of 223329 words

Chapter 31 - Makauniyar Kaddara Hausa Novel Complete

21 Nov 2024

1189

Farah data farka da jan tsaki baiyiba.
     A rikice Zinneerah ta damƙo hannunsa jikinta na rawa ga hawaye na kwarara. “Yayanmu Granny, Granny Yayanmu, dan ALLAH kazo Granny karta mutu”.
      A take shima ya rikice. Ya shiga binta a baya tana riƙe da hannunsa har sannan tana jansa. Tunda suka shigo yaga halin da Hajiya Iyan ke a ciki sai hankalinsa yafi nata tashi, a take yay kanta yana kiran sunanta da ƙarfi.
      Zinneerah daketa yarfe hannu kukanta na ƙara tsananta ya duba cikin sarƙewar harshe yace, “Ɗakkomin waya a ɗakina, m....”
    Batama bari yakai ƙarsheba ta kwasa da gudu ta fice. A guje ta shigo ɗakin har tana bangaje Farah data sakko daga gadon tana mitar an tasheta tana barcinta. Wanwar Farah ta zube a ƙasan tiles ɗin amma ko kallonta Zinneerah bataiba ta nufi wayar data hango a drawer gefen gado duk da bata da tabbacin nasane. Sai dai tana kaiwa garesu ƙamshinsa dake manne dasu suma ya tabbatar mata nasanne. Duka ukun ta kwasa ta sake tsallake Farah dake nishi a ƙasa ta fito.
         Da ƙyar ya iya saita kansa ya lalubo Number Baffah, shima Baffah da yake ba wani barcin kirki yayiba akan idanunsa kiran ya shigo. Mamaki da tsoro ya sakashi ɗagawa ganin sunan Adnan.

     Cikin ƙanƙanin lokaci dukkan ƴan gidan suka gama taruwa sashen hajiya Iya dake cikin mawuyacin hali. Khalipha ne keta ƙoƙarin bata taimakon gaggawa kasancewar ɗalibin likitanci dake gab da kammalawa insha ALLAH. Da ƙyar ya samu yaɗan saita wasu abubuwa. sai dai ya basu tabbacin dolene a wuce asibiti da ita tunda nan gida ba kayan aikine da shi ba.

     Suna idar da sallar asubahi ko Shira Hospital suka wuce. A canne likitocin da sukai duty ɗin dare suka rufu kanta. Yayinda AK kuma ya shiga bige-bigen waya na shirin wucewa da Hajiya Iya London kamar yanda dama yaci buri tun da, sai dai tace bata zuwa Nigeria ma akwai likitoci ƙwararru. A yanzun kam tunda bata a hayyacinta yaci alwashin sai ya kaita insha ALLAH an duba wannan ciwon ƙafartata mai kama dana gado. Dan mafi yawan ƴan family ɗinsu na ɓangaren mahaifiyarta duk sanadin ciwon ƙafa suke barin duniya kamar dai Inno. Ga su duk ALLAH ya basu jikin ƙiba dama masha ALLAH............✍
       

*_Kuyi haƙuri naji kunata cewa bana bana yayinku naƙi muku surprise. Wannan karon abin ya haɗa da wasu uzurorine wlhy. Amma insha ALLAH zan baku mamaki indai pages ne, ina kuma sake baku haƙuri wannan karon akan tafiyar hawainiyarmu ta Typing gaba ɗaya. Ku ɗauki hakan matsayin yau da gobe sai ALLAH. Sannan wasunmu sunada lalurorin yau da kullum tattare da su, da kuma uzirorin rayuwa da duk sukazo mana tamkar an saita. Mukammu bama jin daɗin hakan, dan babban burinmu shine muga mun taru gaba ɗayanmu mun faranta muku tamkar yanda kuka faranta mana kuma kuke zuwa kuna sayen buks ɗinmu a koda yaushe. ZAFAFA TEAM na godiya gaba ɗayansu tare da fatan alkairi a gareku da ban haƙuri. da babban albishirɗin ganin gyara daga garemu baki ɗaya insha ALLAH_*

*_Masu karantawa a waje kuma dan ALLAH ku daure kuzo ku saya naku copy ɗin da halalinku kuma ALLAH zai sakama kasuwancinku albarka ta inda bakuyi zato ko tsammaniba insha ALLAHU. Dan duk wanda ya kare mutuncin wani da fita haƙƙinsa kaima ALLAH zai fita naka ya kuma kare mutuncinka da izininsa._*

*Muna godiya da zaɓin zafafa a koda yaushe😍😍😘😍😋🤗🙏🏻*.



*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_

*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_

*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_

*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

*_TYPING📲_*


*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

*Page 27*

_______________________


*_WANI KAYA SAI AMALE💃🏻💃🏻💃🏻._*

*_INA MATA ƳAN ƘWALISA MA'ABOTA SON KALOLIN GIRKE-GIRKEN ZAMANI. KU GARZAYO GA DAMA TA SAMU A TAFIN HANNUNKU CIKIN SAUƘI💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻😋😋😋😋_*

Nigeria @ 61
COOKING COMPETITION!!!
from lavender Catering ina masu son koyon girki ga dama zaku shiga gasarmu ta girki bayan kunyi register damu akan 10k,wanda yazo na 1zai shiga ajin mu free hade da wasu prize din na 2 da na 3 kuma zasu bayar da rabin kudine da wasu prize suma saura kuwa zasu ayi musu ragin 5% da wasu prize wannan gasa zamu yita ranar lahadi ne 3/10/21 zamu rufe registration na gasar ranar asabar.

Lavender catering school zamuyi practical class. zamuyi 30 dishes continental, snack & desserts, traditional dishes, drink. Fee din 40k phone number WhatsApp and call 09080299283 akwai discount na 5% ga mutum uku farko wadanda sukai register aranakun independence 1/10/2021 to 3/10/2021 Nigeria @ 61

Shi class zamu fara on 14/10/21.

*_KU GARZAYO KAR ACI KASUWAR SAMA BABUKU, DAN NAMU BA IRIN NASU BANE💃🏻💃🏻💃🏻😋😋_*

________________________


*Page 27*

...........Alhmdllh an samu daidaituwar jikin hajiya iya, amma bawai tana a cikin hayyacinta yanda ya kamata baneba. Shiyyasa shima AK ya kammala dukan shirinsa akan tafiyar da ita. A wannan karon Baffah baiyi yunƙurin hanashiba. Sai ma taimaka masa da yay da wasu abubuwan kasancewar tafiyar ta zama ta gaggawa.
        Duk wanda ya kalla shirawa a yinin yau yasan lallai an taɓa musu wani babban jigonsu, dan kowa idanu jajur. Daga masu kukan zuci har masuyin na zahiri irinsu Zinneerah. Dan ita dasu Bahijja haɗe kawuna sukai sukaita rusar uban kuka sai da Yah Haneef yayta lallashinsu da ƙyar da nuna musu sumata addu'a sannan suka ɗan nutsu.

        Haka suka kasance yau yini guda a asibiti likitoci nata ƙoƙarin su, yayinda AK keta shigi da fici na ganin sunbar Nigeria a yau insha ALLAH. Yau ko ƙwaƙwaran abinci babu wanda ya samu yaci a cikinsu, sai ruwa da ƴan kame-kame. Salla kawai ke tashinsu.
     Yah Adnan bai farga da babu matarsa a asibitinba sai da zasu koma gida domin shiryawa. Ransa ya ɓaci matuƙa amma ya daure ya shanye har suka isa gidan. Kamar yanda yay hasashe kuwa a gidan ya isketa wai taji ciwo a ƙafa saboda turewar da Zinneerah tai mata da asuba, ga kuma zazzaɓi tanaji. Duk da ya lura da yanda take alamar kuka ta zauna tasha baibi takantaba ya hau shirya musu kaya da kansa batare daya mata bayaniba. Yana gamawa kuma fiwowa yay zuwa ɗakin hajiya iya. Inda ya iske Zinneerah zaune tanashan sabon kuka.
     Tsaye yay kawai shiru yana kallonta batare dayayi maganaba tsahon lokaci. ita kuma batasan da shigowar tasaba kanta na a cikin ƙafafunta ne. Yaɗan furzar da huci da cije lip ɗinsa yana ƙarasa takawa cikin ɗakin da ƙyau. Gyaran muryar daya saka Zinneerah ɗagowa yayi. Kallon cikin ido sukaima juna sai kawai ta fashe masa da kuka. Idanunsa ya lumshe yana ɗan kauda kansa gefe.
         “Dan ALLAH Yayanmu kaje dani duk inda zaku kaita”. Ta faɗa kukanta na kuma tsananta. Baice mata komaiba ya nufi bathroom ɗin ɗakin dake gyare tsaf duk da yau babu wanda yabi takansa. Ruwa mai ɗumi ya tara a botiki ya fito, inda ya barta anan ya isketa tana cigaba da kukan nata. “Tashi kije kiyi wanka”. Ya faɗa yana nufar inda littatafan hajiya iya suke na addini batare daya sake kallontaba.
     Jin abinda yacene ya saka Zinneerah miƙewa da saurinta duk zatonta ƙorafinta ya karɓune. Littatafan ya gama ɗauka da wasu ƴan abubuwa na Hajiya Iyan yasa a ƙaramar jikka. a saman gado ya barta ya fice domin zuwa shima yayi wankan.

     Sauri-sauri Zinneerah tahau shiri bayan fitowarta wanka kasancewar ba salla takeba. Tana gamawa ganin jikkar daya ajiye akan gado itama ta jawo akwati tahau haɗa nata kayan. Tana tsaka da neman wayarta da tun jiya bayan ta kira mmn sadiq bata sake ganin wayarba, har so tai ta kirata yau ma ta sanar mata halin da ake ciki amma sai bataga wayarba. 
      Shigowar AK ɗakin da sallama ciki-ciki, Baba Rahi biye da bayansa ɗauke da tire ya sata dakatawa da leƙe-leƙen neman wayar da takeyi.  Juyowa tai tana kallonsu, yanzu kam shima yayi wankan dan yana sanyane cikin ƙananun kaya sai uban ƙamshinsa ke tashi dan yama danne nata turaren data saka. Shiko kallo ɗaya yay mata ya ɗauke yana maidawa kan akwatin data haɗa kaya. Baiyi maganaba sai zama da yay  cikin sofa ya ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya yana sauraren Baba Rahi dake lallaɓata ta zauna taci abinci.
      “Baba Rahi na ƙoshi, ALLAH bana jin yunwa”.
       Manyan idanunsa da launinsu ya canja gaba ɗaya a yunin yau ya ɗago ya zuba mata cike da gargaɗi, babu shiri ta amshi kofin shayin da Baba Rahi ke miƙo mata tai ƙasa da kanta tana kaiwa baki badan yana mata daɗi ba, dan bakintama ji take yana wani ɗaci-ɗaci. Ɗauke idanun nasa yay ya jingina da kujerar yana mai lumshe su. Sai dai kuma yana kallonta ta ƙasan idon.
       Baba Rahi ce ta cigaba da lallashinta har taɗanci abincin shima kaɗan ta ture idanunta cike da kwalla tace ta ƙoshi, Batare da Baba Rahi tace komaiba tahau tattare kwanikan zata fita da su ya dakatar da ita. “Baba barsu anan jeki abinki”.
       Amsa masa Baba Rahi tai tana maido tiren ta ajiye, Zinneerah kuwa kallon inda yake ta ɗanyi kamar zatai magana sai kuma ta maida kanta ta duƙar. Shi kuma batare daya tashi koya buɗe idanunba yace, “Tashi ki ɗauka maganinki da abincin kizo nan”.
       Ita tama manta wai bata da lafiyane. Shakkarsa yasata miƙewa ta ɗakko din tayi yanda yace batare data musa bin umarninsa ba. Ɗagowa yay daga yanda yake a zaune ya buɗe abincin da kansa ya sake tura mata gabanta. “Na baki 10minutes kawai ki cinyesa”. Daga haka ya koma a yanda yake kamar ɗazun. Cika idanun Zinneerah sukai da ƙwalla. Taja abincin gabanta tana ƙoƙarin haɗiye ƙwallar tata dan bataga wajen yin wargi ba. ALLAH ma ya sota abincin ba wani mai yawan tsiya bane dan baba Rahi dama ta santa bawani cin abincin take sosai ba. Sai da ta gama tasha maganin sannan ya sauke ƙafarsa da gyara zamansa yana faɗin, “Zonan”.
     Babu musu ta miƙe zuwa garesa. Sai dai inda ya nuna matan ta zauna ne yasata jin shakku tatsaya tana duban gefen nasa. Harar daya balla mata ce ta sata zaman babu shiri daga can ƙarshen kujerar duk da tazarar ba wata mai tsaho bace a tsakaninsu.
        Ƙasa tai da kanta tana wasa da yatsun hannunta, ji take ba'a taɓa saka rayuwarta a takuraba irin ta yau ba, dan kwarjininsa da ƙamshinsa gaba ɗaya sun sakata jin ɗakin ya musu kaɗan. Shiko ko a jikainsa kallon hanunta da taketa faman cuɗawa a juna kawai yakeyi cike da nazari. Mikuma ya tuna oho masa sai yay saurin kauda kansa. Kusan mintuna uku suna a haka shiru kafin ya sake dubanta.
        “Kikace zaki bimu?”.
Ya faɗa ciki-ciki idanunsa ƙyam akan fuskarta.
     “Eh Yayanmu dan ALLAH”.
  Ta bashi amsa itama murya na rawa. Kwarjininsa na sake tsumata dan ta kasa ɗagowa ta dubesa. Tamkar bazai sake cewa komaiba sai kuma yaɗan girgiza kansa. “Idan kin bimu karatunki fa? Ko kin jinginesa kenan?”.
     Idanunta da suka ciko da ruwan hawaye ta ɗago a karo na farko ta kallesa, sai gasu a cikin nasa dan shima ita ɗin yake kallo. Yanda ya tsatstsareta dasu ne ya tilastata maida nata ƙasa hawayen cikinsu da batasan na miyeba na gangarowa. Sai dai tana danganta zubar tasu da takurar da tayi na kasancewar su zaune a waje ɗaya yanda mafalkinta bai taɓa kaiwaba.
    Ya sake maimaita mata cewar, “Nace karatunki fa idan kin bimu?”.
      Muryarta na rawar kuka tace, “Yayanmu nidai kaje dani dan ALLAH, idan na dawo naje makarantar, inason na kasance da Granny kawai”.
        “Saboda karatun baida muhimmanci a wajenki ko?”.
     Kasa cewa komai tayi a wannan gaɓar, hakan ne ya sakashi sauke murya ƙasa da alamun lallashi a ciki yace, “Bazaki bimu yanzuba, dan shi ilimi abune mai muhimmanci ga mai nemansa, adalci ɗaya zan miki shine idan kunyi hutu zakizo ki ganta ok”.
      Sharrr hawaye suka sake ɓalle mata. Ta ɗago zatai magana ya miƙe abinsa yana faɗin, “Na gama magana ki tashi ki saka mata kaya kala biyu a wancan jikkan dana ajiye, sai abubuwan da kika sani masu muhimmanci da take amfani dasu yau da kullum. Wannan kayan naki da kika haɗa kuma ki kaisu sashen Momie dan zaki koma da zama can wajenta”.
       Daga haka ya fice abinsa ko waiwayenta baiyiba duk da yaji kukan data fashe dashi. Kansa kawai ya girgiza yana ƙara jinjina ƙuruciyarta da shagwaɓa a ransa.

       Karo ya kusanci da Farah wadda ke ƙoƙarin shigowa ɗakin alamar biyosa tayi, ya ɗan bita da kallon mamaki kamar zaiyi magana sai kuma ya ɗauke kansa da raɓata ya wuce abinsa. Har tayi kamar ta shiga ɗakin Hajiya iyar taga mi yayo a ciki tun ɗazun sai kuma ta fasa tabi bayansa da sauri. Yana shiga ɗakin itama tana shigowa. Zama yay cikin kujera ya hau haɗa shayin daya saka Baba Rahi dafa masa shima. Sai da ya kammala zai fara sha sannan ya kalli Farah data zauna kusa da shi ta wani tsatstsaresa da idanunta manya.
      “K kina ganin abinda kikayi yau shine dai-dai? Kowa yana asibiti ke kina gida kwance?”.
       Cike da isarta tace, “Amma dai kasan nima banda lafiya ne ai. Sannan wannan shegiyar yarinyar sanda ta shigo ɗakinan ta ɗauka wayoyinka turenifa tayi a ƙasa amma ko waiwayena batayiba. Jiba kaga yanda ƙafata ta kumbura”. Tai maganar tana nuna masa ƙafar da cigaba da faɗin, “Wlhy yanda ta sani jin azabarnan itama sai na sakata taji wadda ta fita dan saina karyata kafin nabar gidan nan”.
       Ɗauke idanunsa yayi daga kan ƙafar kamar baiji mita faɗaba. Duk da masifar data cigaba dayi akan Zinneerah ɗin bai tanka mataba harya gama shan tea ɗinsa sannan ya miƙe. Hakan da yay ya ƙona ran Farah, sai dai ganin ya ɗakko man zafi ya dawo ya zauna da kama ƙafar tata ya ɗora a jikinsa ya sakata sauke ajiyar zuciya.
     Duk da ya jita baice uffanba ya hau shafa mata maganin a wajen yana ɗan dannawa kaɗan-kaɗan itako tana zuba shagwaɓa. Sai da ya tabbatar maganin ya shigeta sannan ya ajiye ƙafar yana dubanta cikin ido. “Yau zamu wuce”.
     Mamaki ƙarara a fuskarta tace, “Ina?”.
       Kansa tsaye yace, “London, Granny zataga Doctor acan”.
     Jitai kamar an daɓa mata mashi a ƙirji. ta tattaro yawun takaici ta haɗiye muƙut tana dubansa, “Amma my Hero duk likitocin ƙasarnan har sai an kwashi kamar Granny dake fama da jikin tsufa an wahal da ita zuwa wani waje”.
       “Ke kika kallesa a fuskar wahala. mu neman sauƙi zamu insha ALLAH ”.
       Harara ta zuba masa a kaikaice zuciyarta nayi mata zafi, cikin ɗan rawan murya tace, “To sai dai kuje ni kasan dai babu inda naje. Bazai yuwu na shigo ƙasarnan ba kuma ban ziyarci kowaba”.
        Juyiwa yay ya kalleta cikin ido fuska a tsuke ainun, cike da gargaɗi da barazanarsa yace, “Da zaki taho ai nan aka turoki, dan haka iya nan ɗin zaki tsaya. Nan da awanni shida jirginmu zai tashi”.
       Yanda ya tsareta da idanun ya hanata iya cewa ƙala, dan tasan mi wannan kallon nasa ke nufi a gareta. Dole ta tsuke bakinta hawaye na rige-rigen sakko mata. Batare dayabi takantaba ya miƙe ya fice dan yanason yin magana da Baffah.
     Miƙewa tai a harmutse itama ganin ya fice tana masifar bazata yarda hajiya iya ta bisuba. Dan babu yanda za'ai a jajubar musu gayya a takurawa rayuwarsu. Khalipha ɗinma ta ɗauki alwashin wannan karon bazai koma mata da zama a gidaba. Sai dai ya koma hostel kamar yanda Mammah ta faɗa. Haka taita masifa tana kuka da neman wayar Mammah amma taƙi shiga. daga ƙarshe sai auntynta ta samu ta kira sukaita masifar tare, Auntyn ta ta katse wayar ta kirashi. Yana ganin kiran sanda yake tare da Baffah yaƙi ya ɗaga dan yasan zancen dai bai wuce mai hali tayi halin nataba...........✍

★★★

        
*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_

*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_

*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_

*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

*_TYPING📲_*


*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*

*Page 28*

___________________________


*MG’s SKIN CARE*
(With us, your skin is elegant..)

Are you guys  looking for where to buy ur skincare product @ mg's skincare is the best plug for you🤗
Do you wish to have that flawless skin that's free of all skin prblm
Do you wnt to achieve that milky skin that turn heads wherever you go😉
Try mg's product nd I assure you you'll never use any

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login