Showing 78001 words to 81000 words out of 223329 words
ki sanar musu kin iso su nema miki wajen zama. dan ba zaki zauna a gidan nan ba. Lokacin da nake lallaɓaki kizo domin gaishesu matsayinsu na iyayena kai tsaye kike cemin bakison zuwa inda suke. To suma yanzu basa buƙatarki”.
Ya ƙare maganar da miƙewa ya fice a ɗakin batare da ko waiwayenta ya sakeyiba.
Bayansa ta raka da kallo idanunta na wani ƙankancewar bacin rai, ta cije baki zuciyarta na mata zugi da sakejin zargin jiya na dawo mata a rai sabo. Tabbas huɗubar aunty data hauce taso jamata wannan wulaƙancin nasa. Duk da dama bata isa tanƙwarashi ko juyasa yanda takeso ba tunda shima bauɗaɗɗen ne, dan ya fita zafin kai da shegen taurin kai tamkar shine jinin mulkin ma ba itamba.
Tayi alƙawarin bazata ƙara kamanta irin kuskuren dataso tafkawa a yau ba nason kwatanta zubar da kimarta. Dan wani raɗaɗi takeji a zuciyarta idan ta tuna a yanda ta shogo gidan a dole ita wayayya. Bandama shirmen aunty data bata shawarar ba ita kuma ta hau ai ko ba'a faɗaba duk wanda ya ganta yasan wayayyace ita, bawai saita nunama duniyaba kodan jinin mulki dake yawo cikin jikinta da tarihinta.
Taja ƙaramin tsaki da ɗauka waya ta kira Mammah, labarta mata duk yanda sukai yanzun tayi. Faɗa sosai Mammah keyi kafin ta yanke wayar domin nemansa.
Itakuma sai ta juya akalar kiran ga auntynta. dan dama da ita suke waya ɗazun daya shigo, itama ta labarta mata komai daya faru da nuna mata gaskiya shawaran data bata na shigowa gidan a yanayin gatse-gatse baiyiba. Dan gashi hakan da tayi yaso taɓa mata kima har a idanunsa, balle ƙannensa da tasan suma kowa ya gumtsi gulma ne dan babu damar yi a gabanta ne ko shi Abdul-Mutallab ɗin dan tasan yanda suke shakkarsa a gidan.
Itama dai auntyn tata kamar Mammah faɗan ta kamayi kamar Adnan ɗin ne a gabanta. Ta kumace ita ai batace tayi gatse-gatse a gabansu kamar wata sashasha ba ko mara tarbiyya, tadaice ta nuna musu banbancin da da yanzun kawai, daga haka ta yanke wayar itama ta koma neman Yah Adnan ɗin.
Su dukansu daga can nemansa a waya suka shigayi, sai dai babu wanda ya iya samunsa dan cama ake musu switch off. Mammah tai ƙwafa dan tasan kashe wayar yayi tunda yasan tsiyar daya shuka.
A falo kam a yanda ya fito ɗakin a fusace ya fice abinsa yasa Khalipha dake zaune yana karyawa fahimtar babu lafiya. Duk da dama dai ba wannan ne karon farkon daya fara ganin rikicin yayan nasu da matarsa ba. Duk da shi yayan nasu kan kauce faruwar hakan a gaban idonsa, amma da yake Farah mace ce mai nacin masifa da mita saita kaisa ƙarshe ya yaɓa mata maganar da zata koma rusar kuka. Dama kuma da yawan faɗan nasu ana yinsane akan zamansa gidansu nacan london ɗin, dan kullum zancenta baya wuce sai ya barmata gidanta ya koma hostel da zama.
Hajiya iya na ɗaki tana gabatar da walha dan haka batasan wainar da ake toyawaba. Sai da ta idar ta fito ne ta iske shi da Khalipha ɗin duk basu a falon. Baba Rahi ma ta sake gyara falon tsaf sai tashin ƙamshi yake. A tunaninta yana ɗaki tare da matarsa yasa bata damuba ta koma ɗakin danta ɗan kwanta itama ta huta.
________________________
*_DANYA_*
Yau a lissafi kwanaki bakwai kenan da bizne aikin Malam da Inna tayi, hakan yasa tun a daren jiya take zuba ido akan dawowar baba. Sai dai har garin ALLAH ya waye babu shi babu labarinsa. Bata damuba dan tasan akwai yau.
Aiko yau ɗinma dai tunda gari ya waye idanunta basu huta da kallon ƙofa ba. Da taji an motsa ƙyauren gidan sai ta hau washe baki, sai kuma taga bashi ya shigoba saita haɗe fuska dajan tsaki. Kamar wasa tana zaune a bishiyar tsakar gidan har aka kira azhar. Maimakon ta tashi tai sallar sai ta cigaba da zama wai idan ya shigo ta haɗa duka tayo ai.
Duk wannan zaman zuba ido da Inna keyi na dawowar Baba Tinene na a gidan tana wanki, ta ƙure waƙa a wayarta da inna bata taɓa tambayarta daga ina ta samotaba. Koda ta tambayi Innar zaman mi take ta sanar mata sai kawai ta hau dariyar shaƙiyanci tana faɗin, “Oh kice tsohon tsimin soyayya ne ya motsa Innarmu”.
Banza Inna tai mata tunda tasan ba kunyace da Tinenen ba, yanzu saita yaɓa mata wata maganar. Haka ta cigaba da zama a wajen har akai sallar la'asar. Tinene data gama wankinta har tayi wanka tana kwashe kayan da alama fita zatayi a gidan. Buga ƙyauren gidan da akai da masifar ƙarfi ya sakasu dubar hanyar zauren a firgice su duka.
A bazata Karima ta shigo gidan jaye da akwati buju-buju da ita tamkar wadda aka ƙwato daga bakin kura. Babu shiri Tinene ta watsar da kayan hannunta ƙasa. Innama ta zabura kan Karimar dake tafiya kamar ma da tangaɗi.
“Mi nake gani haka ni Asabe. Karima daga ina kike tahe da maraicen nan?”.
Ina babu bakin amsawa daga Karima, sai ma zubewa datai a ƙasa cikin hakki tace, “Innarmu ku bani abinci yunwa nakeji”.
Tinene dake tsaye tana kallonsu har yanzun tace, “Tab abu mai wahala anan gidan yanzu Yaya Karima, amma bara naga inada wazobia ko awarar gidan Rashida a samo miki idan bata ƙareba dan maraice yayi”.
“Nagode auta. Inna bani ruwa”.
Ta sake faɗa tana kaiwa kwance da zare hijjabin jikinta gaba ɗaya ta jefar. Ruwan Inna ta ɗebo mata da sauri ta kawo mata, ta ɗagota daga kwancen da take danta bata sai a lokacin idanunta suka sauka akan sayin duka dake a wuyan Karima da damtsen hannunta ruɗu-ruɗu ga tsohon ciki. Duk da kasancewarta baƙa hakan bai hana fitar sayinba da ƙyau.
“Na shiga uku ni Asabe waya maki wanga bugun haka ga ciki Karima? Badai sheɗanin yaron nanbane Babawo?”.
Karima ta sake zamewa ta kwanta cikin tirɓayar jar ƙasar batare data bama Inna amsaba. Ganin Innar zata takura mata tace, “Inna ki barni dan ALLAH, ku bani abinci nide karna matu”.
Kafin Inna ta samu bakin sake cewa wani abu Tinene ta shigo gidan ɗauke da farar leda da awara a ciki. Kwano ta dauka a wanke-wanke ta juye mata takai gabanta. Cikin rawar jiki Karima ta tashi zaune taja kwanon. Bibbiyu ta dinga haɗa awaran tana turawa a baki. Ganin tana neman shaƙewa Inna tai azamar bata ruwa ta sha. Koda ta cinye saita kuma zubewa tana sauke numfashi wani irin zufa na karyo mata ta ko ina duk da kuwa awaran bamai zafi baceba.
Sudai suna tsaye shiru cirko-cirko kowanne da kalar tunaninsa akan wannan al'amari..........✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
*Page 24*
_________________________
_RANO NET! RANO NET! RANO NET!_
_WHO NO LIKE BETA AWUUF THINGS?_
_IDAN KAJI GANGAMI DA LABARI....! INA MASU ZUBIN ADASHEN DA BA RANAR DAUKA NA DATA?_
_TO KU MARMATSO KUJI, KU KUMA SHARE HAWAYEN KU, MUNZO MUKU DA SABBIN TSARE TSARE NA DATA, WADDA KOWA ZAI IYA SAYA DAI DAI KARFIN SA. A FARASHI MAI RAHUSA_
_RANO NET! RANO NET! RANO NET!__
_(Afford data at chikini price)_
_MALLAKI DATA A KUDI KALILAN DA RANO NET_
_TSAYA KUJI, A RANO NET ZAKA IYA ZAMA RESELLER KO WHOLESALER KAI MA, EH ZAKA/KI IYA ZAMA MA SAYAR DA DATA A FARASHIN SARI MUKE BAYARWA, KAI/KI KAFA KASUWANCIN KU KUMA. DA KUDI KALILAN._
_MUNA KUMA SAYARWA AKAN ‘DAI DAYA, KOWANE NETWORK MUNA SAYARDA DATA PLAN DINSA AKAN KUDI KALILAN, MASU FARASHIN SARA KUWA MA KU KUDIN BAI KAI HAKA BAMA_
_AIRTEL_
_9MOBILE/ETISALAT_
_MTN_
_GLO_
_DUK MUNA SAYARDA TSARIN DATA DINSU. KAMAR MISALI MTN MUNA SAYARDA 1GB.24MB AKAN FARASHIN NERA 300 KUMA YANA KAIWA WATA DAYA, GWARGWADON YADDA KAKE AMFANI DA DATA, 2GB 600, 3GB 900!!_
_DUKA WADANNAN TSARIN DATA DAMA NA SAURAN LAYIKA MUNA SAYRWA AKAN FARASHI MAI RAHUSA, WANDA KOWA ZAI IYA YIN TSARIN DAI DAI ALJIHUN SA_
_Ranonet.com.ng_
_GA SITE DINMU NAN DAKE YANAR GIZO, KAI TSAYE ZAKI/KA IYA SIYAN NAKA TA NAN. _
_KO A TUNTUBE MU TA NAMBAR TARHON MU: +234 803 081 1300/+234 808 540 5215_
_KYAU, INGANCI, RAHUSA, ADADE ANA YAWO A YANAR GIZO SAI RANO NET._
_RANO NET..!!!!_
________________________
*Page 24*
...........Koda Farah ta gama surutan haushinta gado ta faɗa daga ita sai towel ɗin da tai wanka tai kwanciyarta batare data tuna ya kamata taje ta gaida matan gidanba. Barcinta tasha sosai kafin ta miƙe saboda shigar kiran salla a kunnenta dan bata da sakaci da ibada. Ruwa ta ƙara watsowa tayo alwalar salla.
Koda ta fito ta gabatar da sallar kwalliya tayi dai-dai misali ta shirya cikin baƙar doguwar rigar jallabiya mai ƙyau, ɗan kwalin rigar ta naɗa a kanta yanda larabawa keyi dai.
Farah ƙyaƙyƙyawa ce kamar yanda mijinta ya faɗa. Tanada jiki mai ƙyau ga kuma ilimi, matsalarta kawai itaɗin ƴar gatace ta gani kasheni, ƴar shagwaɓace bugun farko kuma jinin mulki. Dan itace auta a gidansu shiyyasa kowa sonta yake. Sannan ta girmane a Morocco hanun kakarsu dan a wajen haihuwarta mahaifiyarta ta rasu, daga bayane bayan rasuwar kakar tasu itama riƙonta ya dawo hannun Mammah duk da babbar yayarsu taso ita ta zauna a hannunta. Tana da son girman tsiya da miskilanci, dan koshi kansa oga kwata-kwatan yimasa isarta da taƙama takeyi. Sai dai shima da yake gwanine wajen iyawa duk da baɗan masu mulkin bane sai sukeyin dai-dai da juna harma ya kaita ƙasa ta risina tana mitar ya cika baƙin hali.
Tana son Yah Abdull-Mutallab kamar yanda kowama yasan shima yana sonta. Sai dai tanada matsalar tsananin kishi, wanda da alama ta gadane wajen su Mammah. Dan ita kanta Mammah ɗin ta rabu da Baffah ne saboda kalmar ƙara auren nan daya furta gareta duk da ɗunbin son da take masa har yanzu. Dan ko aure taƙi sakeyi.
Bayan ta shirya ta feshe jikinta da turarenta masu shegen ƙamshi da ɗaukar hankalin mai shaƙa ta fito. A falo ta sami Khalipha daya shigo zaune yana lunch. Ta ƙarasa inda yake taja kujerar dining ɗin ta zauna itama. Duk da ya girmeta shine ya fara gaidata dan yasanta da son girman tsiya. Babuko kunya ta amsa masa kuwa tana buɗe kulolin dake dining ɗin.
Yanda take yatsina fuskarta ne ya tabbatarma Khalipha komai bai mataba a wajen. Dan haka yay ɗan murmushi da fadin, “Ki faɗa abinda kike son ci sai a sayo miki idan duk nanan basu mikiba”.
Kanta tsaye kuwa ta shiga zayyano masa duk abinda takeson ci ɗin. Batare da damuwar komaiba kuwa ya miƙe ya fita dan dama ya kammala nasa cin abincin.
Khalipha na fita babu jimawa su Zinneerah suka shigo gidan. Ita kaɗai ta shigo sashen na Granny cike da ƙarfin hali dan mararta ciwo take mata. Batare data lura da Farah dake zaune a dining tana latsa wayaba ta nufi ɗakin Hajiya iya.
Farah da tun shigowar Zinneerah ita idanunta suka sauka gareta ta wani bita da kallo a yatsine tanajin rashin son yarinyar a ranta haka kawai. Sai dai kuma mamaki take ita wacece a gidan ma? Dan bata santaba a tarihi da labari. (To anya kuwa ƴar gidan nan ce?) ta ayyana a ranta gabanta na faɗuwa. Yunƙurawa tai ta miƙe zata bita ɗakin Hajiya iyan dan yanda Zinneerah ta wuce bata gaidataba sai abin yay mata zafi taga kamar rainine dan ta lura da yarinyar itama akwaita da nuna isa tun kallon datai mata ɗazun, sai kuma mita tuna oho mata ta koma ta zauna tana yin ƙwafa.
Zinneerah kam da batasan tanayiba tana shiga suka gaisa da Hajiya Iya wanka ta shiga. Bayan fitowarta ta shirya cikin doguwar rigar boyal less da yay mata ƙyau ɗas a jiki, dan ɗinkin ya zauna da ƙyau masha ALLAH. Tayin abinci hajiya iya tai mata. Amma sai tace ta ƙoshi sai anjima. Basu jima da cin abinciba a makaranta. Daga haka ta kwanta a sofa sai barci.
Barci tayi sosai, dan bata farkaba sai bayan sallar la'asar da Hajiya Iya ta tadata. Toilet ta shiga ta ɗan gyara jikinta ta fita zuwa falo cin abinci. Yanzu kam mafi yawan yaran gidan sun dawo. duk suna ma a falo zaune suna hira har Granny. Sai matar yayansu baƙuwar ɗazun dake zaune gefe ta haɗe fuska tamau kamar tanajin warinsu.
Cikin ƙarfin hali tai mata barka da yamma. Batare da sauraren amsartaba ta gitta zata wuce saita dakatar da ita. Juyowa Zinneerah tai gareta fuskarta ɗauke daɗan murmushi. A ɗage sosai Farah dake ƙarema Zinneerah kallon sama da ƙasa tace, “Kema anan gidan kike?”.
Kai Zinneerah ta ɗan jinjina mata kawai batare datace kimaiba.
“Uhyim! Amma ban sankiba ni”.
Kallonta Zinneerah tai cikin ido kamar zatai magana sai kuma tai shiru fara'ar fuskarta na raguwa. Dan tsaf ta fahimci dizgata matar Yayan nasu da taji suna kira da Aunty Farah ke neman yi. Itama Farah ɗin da har yanzu ke mata kallon wulaƙanci da isa duk da kuwa babu wani abin kushewa tattare da Zinneerah ɗin, dan duk da take ƙyaƙyƙyawa babbar yarinya babu abinda zata nunama Zinneerah, itama idan dirin jikinne ALLAH ya bata, musamman ma yanzu da take a kan ganiyarta na kammaluwar sirrikan budurci, sannan jikinta a mulmule yake dan ba siririya bace bakamar Farah ɗin. Ga fatarta kalar ɗaukar hankali gamai kallo. ta buɗe baki zatai magana Hajiya iya ta katseta dan dama ta saka musu idone taga mi Farah ɗin zatayi.
“Tunda ba zuwa cikinmu kikeba ta yaya zakisan kowa. Ke Zinneerah wuce kici abinci”.
Sum-sum Zinneerah ta wuce dining tana ƙoƙarin maida duk wani ɓacin ran Aunty Farah ɗin daya fara yunƙuro mata. Dan a rayuwa ta tsani wulaƙanci da raini da disgi a rayuwarta. Zata iya jure komai banda waɗannan abubuwan.
Sosai su Jamal sukaji daɗin abinda Hajiya tayi, itako Farah a fusace ta miƙe tabar falon zuwa ɗakin mijinta. Yi hajiya iya tai kamarma bata ganiba. Ta kuma haɗe fuska dan karma wani a cikin yaran yace wani abu. Daga hakama hirar ta watse. Dan barin falon itama Hajiya iya tayi.
Kusan 6 Zinneerah da tuni suka fice suna can harabar gidan anata hira ta shigo sashen hajiya iya saboda matsa mata da mararta tayi. Bedroom ta nufa inda ta iske hajiya iya na waya. Sai da ta kammala ta dubeta tana ajiye wayar data gama ɗin. “Fitinar Moddibo dabance wlhy. Inno dubamin ko su Rahi sun wuce?”.
“Lah Granny ai sun tafi, bakuyi sallama bane?”.
“Munyi sallama. Na zata basukai ga tafiyar banebam wannan fitinatunne yay kirana yanzu, wai ashe azumi yakeyi amma bai faɗaba tun ɗazu ba sai yanzu. Kuma wai abinci yakeson a haɗa masa. Gashi su Rahi ba tuwo sukaiba yau”.
Cikin ƙarfin hali Zinneerah tace, “Granny yaya za'ai yanzu to?”.
“Nima ban saniba to Zinneerah, sai dai ko ke zaki shiga kitchen ɗin ki haɗa masa tunda waccan malalaciyar matar tasa na tabbata ƙila ko shayi bata iya dafawaba balle wani tuwo”.
Idanu Zinneerah taɗan waro waje da faɗin, “Kai Granny nikuma? Ta ina zai iya cin jagwalgwalona”.
“Ci kuwa zaiyi harda santi Inno na. Kinga tashima kije kar ya dawo ya samu ba'ayiba ya fara baƙar zuciya danshi baya wasa da cikinsa. Tuwon zaki masa da ɗan wani abun mai sauƙi tunda azumi yakeyi”.
Zata ƙara magana Hajiya Iya ta girgiza mata kanta. “Kinga babu abinda zai faru, lafiya lau zakiyi insha ALLAH kinji ƴar albarka. nina ai dana idar da sallar magrib zanzo nama tayaki muyi tare”.
Jin abinda Hajiya Iyan ta faɗa ya sata miƙewa tana fadin to ta fice zuwa kitchen da kwarin gwiwarta. Sai da ta fara karanto addu'ar nasara kafin ta ɗauraye tukunya tasa ruwan tuwo dai-dai misali, dan itama dai tana ganin tuwon zataɗanci ko zataji sassaucin ciwon marar nan da taketa dannewa dan karta tadama hajiya Iya hankali.
Cikin ƙanƙanin lokaci ta kammala tuwon semo.. data bama nutsuwa sosai gudun yimasa kuskure, sai da ta kammala kwashewa zuciyarta keta ƙara ƙarfafata akan miyar da taketa tunanin masa tunda ta fara tuwon. Ɗanyen kifi ta cira ta gyara tasashi a wuta da kayan ƙamshi da albasa dan rage masa ƙarni. Kafin ta koma ta ɗiba kayan miya zallar attarigu da tattasai sai albasa da tumatur guda biyu kacal ta wankesu suma tasa a blender da ɗan ruwa bamai yawaba can tai musu markaɗe ɗaya da yay kamar jajjage amma yaɗara jajjagen laushi kaɗan. Kifin ta sauke ta tsamesa a ruwan ta buɗesa ta cire ƙayarsa duka ta farfasashi, ta ƙara ɗora tukunya tasa manja a wuta ta zuba wannan fasashshen kifin da albasa da magi ƙwara ɗaya ta rage wutar can ƙasa. Sallamar hajiya iyace ta sakata juyawa tana kallonta. Ta ƙaraso cikin kitchen ɗin tana magana cike da tsokana. “Wai wai, anya kuwa yau kunnen moddibo bazai kai ƙasaba Inno. Irin wannan ƙamshi haka da