Showing 42001 words to 45000 words out of 223329 words
bisa hanya da ƙyau”.
Murmushi maman Sadiq tayi har haƙoranta na bayyana. “Maganarka haka yake Yaya. Dan yanda ma zakaji tana faman shagali dasu Sadiq idan na barsu su kaɗai ya isa tabbatarwa. Idan kaji bakinta cauy-cauy baka taɓa cewa itace ke zuba zance”.
Dariya shima Abban ya sakeyi. “Ahaf kaɗanma kenan. Bayan takurar data taso a can harda cikin yaron nan ya sake dankwafe dukkannin kuzarinta da karsashi. Amma zata ware tsaf ta bama kowa mamaki. Naga alamar kuma tanason karatu ma sosai, dan jin daɗinsa ya sakata bamu labarin abinda bamu tambayetaba ma”.
Haka suka cigaba da hirarsu cike da fahimta dajin daɗi. Yayinda Zinneerah kecan tana tsallen murna zata koma makaranta. Harda ɗaukar Little dake barcinsa ta hau masa rawa. Aiko ya farka ya birkuce mata kuma. Da ƙyar ta lallashesa tana dungure kansa da goyasa wai karya tona mata asiri Mama tazo tai mata faɗa ta tada ɗan aljanu kuma.
Kwana uku dayin maganarnan aka saka Zinneerah islamiyyar safe zuwa 2 sun taso. Kusan dai-dai da yaran gidan kenan amma ƴammatan kawai dake shirin gama secondary. Su Sadiq kam sai shidda suke tasowa makarantarsu haɗe take da islamiyya.
Faɗa muku irin kalar farinciki da Zinneerah tayi ɓata lokacine. Sai da akaje makarantar kuma ta raina kanta dan batasan komaiba. Amma tayi alwashin nutsuwa sosai ta fahimci komai ɗin kodan ta ribantu a duniya da lahirarta
_________________★
A kwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI. Yau ga Abdul-Mutallaf (Little) da wattani bakwai a duniya. Yaro ƙyawunsa nata ƙara fitowa fili da lafiya ingantacciya. Bazaka taɓa cewa ba abincinsa yake samu daga mahaifiyarsa ba. Dan ma zazzaɓin haƙora kan girgiza kuzarin nasa wasu lokutan.
Amma da yake zuwa yanzun cin abubuwa yake sosai, dan su Aliyu komai suka yayo kimsa masa suke shiko ya cinye abunsa sai hakan ya ƙara taimaka masa aynun. Rarrafe yake ko ina ga ɓarna, inda yana waje kowa kaye-kayen kayansa yake inba hakaba yazo ya tarar an canja musu sabon tsari.
Babu ruwansa da Zinneerah, hasalima ƙyuya yake mata wani lokacin. ba komai ya jawo hakanba sai itama rashin kulashin da takeyi sosai. Dan komansa Maman Sadiq ce sai kace itace uwarsa. Shi da su Sadiq kuwa ai da kuka ake rabuwa idan zasu makaranta. Dasun dawo kuwa zakaga walwalarsa ta daɗu.
Zinneerah nata karatun islamiyyarta wanda a yanzu tayi matuƙar yin nisa dai-dai gwargwado, dan ko a Alkur'ani ta kusa kai izifi biyu, ta saka himma sosai. Hakama sauran littatafai bata wasa. Bokon dai ce ba'a kai ga sakataba har yanzu saboda wasu ƴan dalilai da suka riƙe Abba. Amma yanata shirin hakan batarema da sanintaba.
★★★★★★
Little nada shekara ɗaya cif a duniya da ƴan kwanaki ALLAH ya bashi ikon fara takawa. Ranar zokaga murna wajen su Aliyu. Zinneerah na zaune a falon ita da Mama suka dinga ihunsu na murna mama na tayasu da dariya. Zinneerah dai ta murmusa ta kauda kanta ga abinda takeyi, sai dai a kallo ɗaya zakai mata ka fahimci kawaicine kawai takema mahaifiyarta, amma har cikin ranta tanason ɗanta da jin daɗin duk cigaban da zaizo masa a rayuwa. Duk da kuwa har yanzu tunaninta na nan akan aljanu suka saka matashi a ciki ta haifa musu. Wataran kuma zasuzo su sace abinsu.
Maman Halima dake tsakar gida tana girki ta leƙo tana tambayar lafiya su Sadiq ke ihu haka?. Cike da murna Abdull yace, “Mama little ya fara tafiya”.
Dariyar itama tayi, tare da shigowa ɗakin sosai ta ɗauka Little tana juyi dashi. Dariya su Sadiq suka sake sakawa. Amma banda Little da kowa ya fahimci miskilancin yaron tunda ya fara wayo. Sam baida yawan fara'a, akan daɗe ba'aga yana dariya ba. Garama idan su Aliyu ke masa wasa zakaji har ƙyalƙyalewa yanayi abunsa. Zinneerah ma catai ita daya rainama ko dariyar yake idan ya ganta dainawa yakeyi.
Duk sanda ta faɗi haka mama kan girgiza kai kawai da faɗin, “ALLAH ya kaimu randa zakiyi hankali dai, harshi Abdul-Mutallaf ɗin miya sani da sai ya zaɓa wanda zaima dariyar? Kawai dai zuciya nason mai ƙyautata mata, keko ko wasa bayimasa kikeba”.
Idan mama ta faɗi hakan Zinneerah bata ƙara cewa komai kuma, dan dai kam da gaskiyar mama. Idan kaga tama yaron wasa sai inba idon Mama a wajen. To kafin hakan ta faru kuwa akan jima musamman daya kasance yanzu itama ta fara makarantar boko a sukul ɗin su Sakina.
Duk da Sakina nashan zubar mata da mutunci ga abokan karatunsu na cewar ai bazawarace ta taɓa aure harda ɗa. Da farko ƴan ajinsu kan ƙaryata ta sukeyi, dan a ganinsu nawa Zinneerah ɗin take da za'ace ta haihu, a yanzunefa suke shekaru sha biyar suna farkon shiga sha shida. Tsabar son ƙara wulaƙanta Zinneerah saita ƙirƙiri dinga gayyatarsu gidansu dan aga little. Wasu ko sunje sun gansa basa yarda, amma yau da gobe sai suka fara amincewa da Sakina ɗin har suna tsokanar Zinneerah.
A farko takansha kuka. Amma zuwa yanzu da take neman watanni kusan biyar a makarantar sai hakan ya bar ɓata mata rai. Tama sake ɗammarar maida hankali akan karatunta kamar yanda a kullum Mama ke jaddada mata ta dage wannan karatun sai ya zame mata ado mai ƙawata tarihinta watarana.
Ba fahimtar Mama takeba kai tsaye akan furucin, dan ita a shirmenta har yanzu Mama batasan yaya aka samu Little ba. Bayan sun gama darerakunsu akan fara tafiyar little ɗin Mama ta fice. Su kuma suka cigaba da hidimarsu a ɗakin kasancewar lahadice yau islamiyya kawai yaran zasuje da yamma.
Ganin Little ya ɓingire ƙasa alamar barci zaiyi yasa Zinneerah ajiye buk ɗin hannunta da take Assignment ta ɗaukesa ta goyashi, dan Mama ma ta shige ciki kanta na ciwo. Fita tai tsakar gida dan ta taya Maman Halima aiki kasancewar yau ranar girkintace.
Maman Sakina kawai ta samu zaune dasu Luba dake wanki a bakin rijiya. Ba wani shiga sabgarta suke a gidanba shiyyasa itama bata matsawa kanta na shiga tasu. Dan wasa-wasa Zinneerah ma akwai miskilanci da tsiwa idan taso. Sai dai yanayin rayuwar data tashi a cikine ya sakata komawa sanyi-sanyi.
Yanzu ɗinma Maman kawai ta gaida taja kujera ta zauna a bakin rijiyar itama inda aka tara wanke-wanke. Cikin neman tsokana Luba ta dubeta taɗan taɓe baki, sai kuma a bazata ta bushe da dariya. Kallonta Aliya tayi, hakama Mamansu. “Luba lafiyarki kuwa da wannan dariya kamar wata mara hankali?”.
Cikin dariyar tace, “Mama bazaki ganeba. Wlhy wannan agolance take bani dariya. Idan ta fita waje samarin anguwarnan suyita wani rawan kai a kanta su sun sami budurwa, shashashun basusan harda surƙumemen ɗa gareta a gidaba. Jiyafa Faisal ɗin gidan Alhaji Zubair bakiga yanda ya nacemin da tambaya akan wacece ita ba? Niko na ce masa bazawarar agolan gidanmuce”.
Dariya suka bushe dashi su duka har Maman. Maman Halima dake kicin ta fito a fusace tana kallon Luba mai zancen. “Haba Luba wane shirmene haka da girmanki. Zinneerah ba ƙanwarki bace amma kike wannan sakarcin?”.
Da kunƙunin rashin tarbiyya Luban tace, “A'a Umma nikam ba ƙanwata bace, dan bamu haɗa komaiba banda agolanci datazo gidanmu cin arziƙi”.
“To sannu mara kunya, yanda kikejin nan gidankune itama haka gidansu ne. Dakike aibantata wajen mutane cewar bazawara kuma agola kina tunanin hakan zai hana wanda ALLAH yasa ya zama mijinta zuwa har gidan nan neman aurenta. Kubar wannan banzan halin dan baida ƙyau, ku matane gidan wani zakuje wataran kuma.......”
A fusace Maman Sakina ta tare zancen. “A'a Maman Halima kinga, miye na wannan dogon alkaba'in bayan gaskiya yarinyar ta faɗa. Daga ni har ke kowa yasan ai ita agolarce a gidan. Kuma bazawara. Luban ai taimakonta takeyi wajan faɗar gaskiya dan kar bayin ALLAH suzo a rufesu a basu budurwa bayan gata harda ƙurmusheshen ɗa a baya”.
Maman halima zata sake magana Maman Sadiq da hayaniyarsu ta sakata fitowa dole tai saurin faɗin, “Yaya dan ALLAH abar maganar dan bata da amfani. K kuma Luba ki kwantar da hankalinki ko baki faɗa musu ba dama idan sunzo ɗin zasu sani ai. Cin arziƙi kuma da tazoyi gidanku naɗan lokacine insha ALLAH ”. Daga haka ta juya ta koma ɗaki idanunta na cika da ƙwallar tausayin ɗiyar tata da babu ranar da zata fito ta koma ga ALLAH Saude da ɗiyanta basu yadda habaici akanta ba a gidan. Sai dai suna musu shirune daga ita har Zinneerah ɗin saboda tana ƙwaɓarta akan karta kulasu komai mai wucewane. Sai dai na yau ya mata zafi har tanajin kamar tasa Zinneerah tabar gidan ko itama ta huta da wannan gorin.
Maganar Maman Sadiq sai gashi tabar baya da hazo. dan dama irin wannan damar Maman Sakina ke jira ta dirje Maman Sadiq ɗin akan haushin zaman Zinneerah da ɗanta a gidan. Aiko ta zauna ta fara zuba tijara har su Luba na iƙirarin dukan Zinneerah wai.
Shiru Zinneerah dai bata kulaba, tamkarma batasan anaiba tanata wanke-wankenta. Sai da cikin suɓutar baki Aliya ta zagi Maman Sadiq ne Zinneerah ta miƙe batare da kowa ya luraba. Sai saukar sautin mari kawai sukaji akan fuskar Aliya a bazata..........✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
*Page 14*
____________________
*_INA MATA ƳAN ƘWALISA BA'ABOTA SON GYARA JIKI DA FATA SUYI ƘWANAS TAMKAR WATA ƊAN DAREN SHABIYAR?!_*
_Ku marmatso kusa maza na kaiku kantin sauƙi na UMMU DUFAIL gidan sauƙi da biyan buƙatar MATA SARAKAN ado harma da MAZA ƴan ƘWALISA._
*_MATA da yawa kanso su koma Taurari ababen kallo da burgewa ga ma'abota kallo sai dai basusan ina zasu sami sinadarin kankaro wannan ƙyawu da mutuncinba._*
_To maza kuzo kusa dan Bilyn Abdull ta lalubo muku kantin sauƙi na Umm Dufail dakeda kaya masu sauƙi da gamsar da maison afani dasu_.
*_UMMU DUFAIL nada kayan gyaran jiki masu rahusa da inganci da gamsar da mai saya cikin ƙanƙanin lokaci kamar haka👇🏻😁_*
*Customers price list By Ummu Dufail FACE AND BODY*
SCRUB=2500(300ml)
Face and body mango butter=3k (250ml)
Face cream= 1800
Corretor oil/vitamin C oil=2k
Fairness skin lotion= 2500
Hot chocolate skin lotion 2500
Serum (for Nuckles )2k
Nuckles cream (stubborn)3500
Mix fruits Arabian black =soap 1800
Mix fruit glycerine soap =1900
Beetroot=1900
Coconut, milk,egg..face soap=1200
Lavender mix fruit soap =1800
Body wash =1500
cleanser=1600
Hair spray =700
Hair oil =1500
Hair relaxer =700
Hair butter 1700
Shampoo =1500
Breast=oil 2k powder 2k
Strech marks cream= 2k
Beetroot pink lips =700
Baby care soap glycerine=1k
Baby care butter =1500
Shea butter baby soap =700
Tsumin tula =2200
Tsumin zinariya =1200
Sliming tea =1500
Amarya set =25k
Liquid Arabian black soap =1900
Cleansing water =1500
*_Zaku iya bibiyarta domin gani da ido ta Handle ɗinta na istagram da facebook kamar haka_*
Ummu Dufail @ Facebook
Ummu Dufail @ instagram
Phone no: 07067943479.
_Ƴammata harma da masu auren karku bari ayi babuku. Dan gyara shine mace a wannan ƙarnin😉👍🏻_.
_____________________
*Page 14*
............Tsitt gidan yay na wucin gadi kowa na duban Zinneerah da mamaki. Cikin fushin da basusan ta iyaba ta nuna Aliya idonta na cikowa da ƙwalla. “Ki kama harshenki a duk lokacin da zuciya ke ingizaki wajen kuskuren suɓucewarsa. Zaki iya mani ni baki isheni ko kalloba. Amma idan kikace ƙarancin tarbiyyarki zai cigaba da rufe idanunki wajen raina waɗannan lallai zan maidaki cikin hayyacinki!!”.
A yanda tai maganar babu tsoro ko alama a cikin idanunta ne yay matuƙar saka shakkarta a zuciyar Aliya. Dan haka ta kasa komai sai kallonta da take hannunta riƙe da kuncinta.
A fusace Luba tayo kan Zinneerah, wani wawuyan cakuma tai mata wadda tai sanadin suɓucewar zanin goyon datake goye da little. A take yaron yay baya gaba dayansa. Ita kuma Luba ta cakumi Zinneerah ɗin sukai gaba.
Kusan a tare Maman Sadiq da Maman Halima suka iso wajen daf da Little daya tsage da wani gigitaccen kuka zai kai ƙasa. Cikin amincin ALLAH ya faɗa cikin hannunsu da suka tara a tare.
A can kuwa tsakanin Luba da Zinneerah dambe ne sosai ya harƙume. A tunanin Luba zata iya dukan Zinneerah ne dan tana ganin ta fita girman jiki. Sai gashi Zinneerah ɗin na tumurmusar hancinta a ƙasan sumintin gidan. Ganin irin dukan da Zinneerah kema Luba yasa Aliya da Maman Sakina rufe Zinneerah da duka suma.
Masu iya magana sunce sarkin yawa yafi sarkin ƙarfi, da wannan damar suka sami galaba akan Zinneerah duk da dai ta more sosai itama akan Luba ai. Ganinfa abin zai zama hauka Maman Halima ta sakarma Maman Sadiq Little dake kuka saboda tsoratan da yayi ta nufesu tana ƙoƙarin janye Maman Sakina da Aliya amma ta kasa. Sai faman kaima Zinneerah duka suke suna ɗura mata zagi, har takai Maman Halima ɗinma na samun rabonta.
Ana cikin wannan rikici ALLAH ya kawo sallamar wata baƙuwa mai tsananin kama da Maman Sadiq. Ganin abinda ke faruwa duk da batasan wa suke duka ba ta ajiye jakka itama ta shiga cikin masu rabo. Da ƙyar suka iya yakice Zinneerah a tsakkiyar su Maman Sakina daketa zage-zage tamkar dangin maguzawan farkon ƙarni.
“Innalillahi, mike faruwa kukuwa haka a gidan naku Yaya Hauwa? Maman Halima miya kaiki shiga wannan shirmen?”. Baƙuwar ta faɗa tana duban Maman Sadiq dake jijjiga Little, sai kuma ta maida kan maman halima. Kafin ta dubi Zinneerah data nufi ɗaki abinta kamar bada ita aka gama kicimilliba yanzun.
Cikin baƙin ciki Maman Halima tace, “Sannu da zuwa Maryama. Dolene ta kaini ga hakan ai, taya zasu tararma yarinya haka bayan ta fisu gaskiya. Sam Saude batason a zauna lafiya a gidan nan wlhy Maryama”.
Ganin yanda su Maman Sakina ke ƙara hayayyaƙowa yasa baƙuwa Maryama cewa, “Kunga naga wata sabuwar fitinar ke neman tashi kuma. Maman Luba dan ALLAH kuyi haƙuri haka ya isa. Yaya shige muje, Maman Halima dan ALLAH kema shiga ɗaki kawai”.
Shawarar Maryama Maman Halima da Maman Sadiq sukabi kowa ya shige aka barsu sunata haushi kamar karnuka. Sai da suka shiga ne Maryama taga Zinneerah da ƙyau. Cikin ɗaurewar kai tace, “Wai nikam wa nake gani anan haka Yaya?”.
“Hummm Maryama bar wannan batun zauna ki huta. Sannu da zuwa kinsha hanya. Bansan kina tafeba ai”.
“Tafiyar bata shiri bace ba ai Yaya. Kuma nama nema wayarki amma sam bana samu, shiyyasa kawai nai ƙuru nace bara na biyo ɗin dai kar nai rashin hankali”.
“Tofa, ALLAH yasa badai wani abune ya faruba kuma?”. Mama ta faɗa tana mikama Zinneerah da kanta ke duƙe a ƙasa alamar kuka take little. “Ki tashi ki masa wanka a bashi abinci tunda yayi shiru”.
Sai lokacin Zinneerah ta ɗago tana share hawayenta. Ta amshi little ɗin kafin ta gaida Maryama. Amsa mata tai tana binta da kallo, hakan yasa Zinneerah miƙewa ta shige ɗaki da Little a hannu. Ajiyar zuciya Maryama ta sauke bayan shigewar Zinneerah ɗin, duk maman sadiq dake ƙoƙarin kawo mata ruwa na kallonsu. Sai da ta ajiye ruwanne ta sake maimaita mata tambayar ɗazun.
Maryama tace, “Lafiya ƙalau, sai dai lafiyar mai rauni. Inno ce jikin nata babu daɗi, dan sunce shekaran jiya da daddare kamarma bazata kwana duniya ba”.
“Innalillahi wa'inna ilairraji'un. Yanzu nan har jikin Inno yakai tsanani haka amma baza'a sanarminba Maryama, har ke dake a Minna kiji”.
“Kiyi haƙuri Yaya Hauwa, wlhy ba laifinsu bane. Buba yace tunda ciwonta ya fara motsawa a cikin satin nan suke neman wayarki data Yaya amma basa samunku. Ni kaina Baban su Atiku suka samu tunda kinsan dai ba wani muhimmanci wayata kedashi ba”.
“Eh kuma sun fini gaskiya, dan layin nawane ya samu matsala wlhy, Yaya kuwa bansan yaya akai suka gaza samun nasaba, kokuma matsalar network ne. UBANGIJI ALLAH ya ƙara mata lafiya. Jikine na tsufa sai dai Alhmdllh”.
“Wlhy jiki kam na tsufa. Dama na biyo ne idan babu matsala sai mu wuce Baucin tare mu dubata, to saima ina shirin tahowa danai waya da Buba yake sanarmin ai Hajiya Iya taje garin taga halin da take ciki ta ɗakkota suna anan kano wajenta”.
“Tofa, ita Hajiya Iya ɗin dama suna anan kano ɗin har yanzu?”.
“A'a yaya yakike wannan magana haka. Handa Hajiya Iya da iyalanta sukai ƙarfi a garin nan kina ganin zasu iya barinsa kuwa? Kenan baki cikama Inno alƙawarin da kikai mata na neman inda suke ɗinba?”.
“Humm Maryama bazaki ganeba. Ni wlhy kin ganni nan harka da masu kuɗin nan ba sonta nakeba sam. Bani ƙaunar shiga inda akafi ƙarfina a wulaƙantani”.
“Kai Yaya kenan har kin sani dariya. Aiko kinga Hajiya Iya bata da wannan, mace ce maison zuminci sosai. Danni kinga mun taɓa haɗuwa da ita kusan sau biyu kuma duk banga wani nuna ƙyama daga garetaba. Saima jana da taitayi a jiki tana min faɗa da cewar Baba ya rabamu da dangi bamusan kowaba sai Inno”.
“To kinsan abinne da wuya wlhy Maryama. ALLAH ya ƙaddara bazanje ɗinba sai ta silar zuwan Inno ɗin. Dan yanzu hakama ni nama manta yanda adireshin gidan yake”.
“Wannan mai sauƙine ai Yaya sai a kira Baban su Atiku ya kira Buba muji. Nidai na