Showing 15001 words to 18000 words out of 223329 words

Chapter 6 - Makauniyar Kaddara Hausa Novel Complete

21 Nov 2024

1162

suma.. Kusan mintuna goma Maryam tazo tai kiransu.
     Kamar ɗazu daga ita sai Gwaggo Laritu suka shiga. bayan sun zauna likita ya dubesu da murmushi yana faɗin, “Masha ALLAH mamana ga sakamakon gwajin hitsarin da mukai mata ya hito. Duk da dama dai kafinma hakan na fahimci ciwon na ƙanwata abin so ne. Amma duk da haka dai nafi yarda da'a gwada ɗin......”
       Cikin ƙosawa Gwaggo Laritu tace, “To madallah, mike damunta?”.
       Sake faɗaɗa murmushi likita yay yana duban Zinneerah da kanta ke a ƙasa tana wasa da yatsun hannunta. “A'a Inna ba wani abu baneba face ƙaruwa muka samu. Tanada ciki na kusan watanni huɗu. Kuma Alhmdllh yana cikin ƙoshin lafiya kamar yanda itama alamomi suka nuna tana cikin ƙoshin lafiya, sai dai kuma ya kamata a ringa kula da abincin da zataci saboda shima yaron cikin nata ya samu nagartaccen raino.......”
     Sam Gwaggo Laritu da Zinneerah ba fahimtar bayanin likitan sukeba tunda ya ambaci ciki. Dan Zinneerah ma wani irin hajijiya take gani. Tun ofishin na juya mata har ta koma ganin duhu a cikin idanunta. Sai kawai ganinta sukai a ƙasa daga ita har kujerar robar da take zaune a kai.
       “Ya subahana”. Doctor ya faɗa yana zabura saboda faɗuwar Zinneerah. Hakan kuma yay dai-dai da dawowar Gwaggo Laritu datai suman wucin gadi itama hayyacinta. Yayinda su Kawu Rabilu suka shigo da gudu saboda jin sallalamin da likita da budurwar nan Maryam keyi akan Zinneerah da alamomi suka tabbatar da suma tayi............✍


“Hummmm!!!! Turƙashi, masu karatu wannanfa shi ake kira da ANA DARA GA DARE YAYI. shin yaya akai hakane? Yaya kuma za'ai? Mi kuma zai faru?. Gadai likita ya tabbatar da ciki a jikin Zinneerah baiwar ALLAH. yayinda Zinneerah ta tabbatar mana kuma bata taɓa iskanci da kowa ba. Shin tayaya aka samu ciki idan babu mahaɗi? Shin wanene uban wannan cikin? Ta yaya aka samar dashi? Da sanin Zinneerah ko fyaɗe ne? Mi Inna ta sani akan barin Zinneerah gida? Anya kuwa babu lauje cikin naɗi masu karatu? Ina mahaifiyar Zinneerah? Yaya Baba zai kasance da tabbatuwar wannan cikin dake jikin ƴarsa dake a matsanancin rayuwa a gidansa? Yaya jama'ar garin Danya zasu cigaba da ɗaukar Zinneerah yanzu? Yaya rayuwar Zinneerah zata cigaba da kasancewa a gidansu da garinsu?.

Wannan amsoshin duk suna ƙumshe a cikin littafin MAKAUNIYAR ƘADDARA da zai zo muku akan naira 300 kacal insha ALLAH. Dan girman ALLAH ina roƙonki ƴar uwata. Kibi ta hanyar data dace domin mallakar naki cikin kwanciyar hankali. Idan kin zama mai shigewa gaba wajen girmama sana'armu kema sai ALLAH ya ɗaga darajar taki komai kanƙantarta. Idan kin zama jagora ko mai burin ruguzamu UBANGIJI ya fimu sanin ke wacece.. Fatanmu kowa ALLAH yay riƙo da hannunsa akan neman halak ɗinsa. Dan ALLAH kuzo ku saya kafin ku karanta. Dan ALLAH idan kin saya karki zama ɗaya daga cikin masu fitar mana dan kawai ganin mun koma baya ko kuntata mana. Ku tuna da tarin alkairinmu na baya gareku, koda bazaku rama manaba karku cutar damu dan girman ALLAH mun roƙeku dan shine kaɗai zamu iya haɗaku da shi🤓🙏🏻.

ALLAH kai mana jagora. Yanda zamu fara lafiya ALLAH ya bamu ikon gamawa lafiya. Masoyanmu da basu gajiyawa wajen sayen hajarmu da mun fitar muna sake godiya a gareku, ALLAH yabar zuminci. Masoyanmu da basu taɓa sayaba kuma ku garzayo dan bana Zafafa shiri sukai na musamman domin farin cikinku. Masu jira a fiddo ku karanta kuma dan ALLAH kuzo ku biya ku mallaki naku a wannan karon kuma sai ALLAH ya kawo muku Customers akan naku kasuwancin. Mun gode. Mun gode irin trillions ɗin nan😘😍😘😍🤗😊😉.

*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_

*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_

*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_

*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_TYPING📲_*


*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*


*Page 6*

_________________________

Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗

Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali
Ina masu pimples
Tabo(spot)
Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance
Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba

Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki

Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu

Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself
100%tested nd trusted

Soap price:3k
Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free

Maiso kindly message 08062991549
Call 08064532391

Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏

Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝

Mg's skincare

Mg's bakery
You can still order ur birthday cake, cupcake,slice cake,meat pie,shawarma,samosa nd spring rolls for ur event @mg's bakery
Kindly call or chat
07046881166
07067210195
08062991549

Masu bukatar abayas,takalma da jakunkuna,ashobe,laces d atamfofi, materials nd the rest
07046881166
👏🤝



Page 6

.........Tun bayan wucewar su Zinneerah kusada Inna ta kasa zaune ta kasa tsaye. Ba komai ke mata kai kawo a rai ba sai maganar Gajeje da take cewa babu wanda ya binciki Zinneerah yaji ina taje. Idan har bata ɗauki matakiba to lallai abinda bata buƙatar ya fito da ga bakin Zinni shine zai fito, dan suna dawowa gida kowa zaiso jin ina taje ɗin? Yaya akai kuma ta dawo?.
     Tsulum ta miƙe da ga zaman da tayi a bakin gado, ta rarumo yamutsatstsen gyalenta daketa tsamin dauɗa. Tana ƙoƙarin warwaresa ta yafa Magajiya ta shigo ɗakin...
        “A'a, Asabe ina zuwa kuma?”.
Ɗan duru-duru tayi na alamun rashin gaskiya. Sai kuma tai saurin faɗin, “Uhm Magajiya zanje nan ƙauyen kwangi ne na amso kuɓewar dana bada a daka saboda miya. Na sha'ahwa gaba ɗaya sai yanzu na tuna. Gashi Atine tace tuwo aka ɗora yanzu da za'aci da rana. Kinga kuma dole ne miyar ɗaurin aure ma na gobe a haɗa da miyar yauƙi dan taushe ɗin nan ba isa zataiba”.
      Kai Magajiya ta ɗan kaɗa mata, sai kuma tace, “Amma nikau da dai kin aiki ko Tinene ko Sa'a mana. Ke da mutane keta shigowa kuma ace kinje wani waje ai babu daɗi. Sannan waɗanan masu tahiya asibitin ya kamata ki jira kiga dawowarsu ko”.
     Nannauyan numfashi Inna ta sauke tana ƙyaɓe fuska. Tace, “Kinga Magajiya hita batun waccan watsatstsiyar yarinyar. Dan babu mai ɓata mani taro aradu. Maganar amso kuɓewa kuwa gara naje da kaina. Dan daga Tinene har Sa'a mashiririta ne da kike ganinsu”.
       Magajiya tace, “To ni haɗani da Tinenen muje. Ai in dani dai batacewa bata zuwa ko?”.
            Sosai wani irin tuƙuƙin baƙin ciki ya turniƙe zuciyar Inna. Ji take kamar ta kaima Magajiya duka. Da ƙyar ta shanye abinda ya tokare maƙoshinta ta ƙaƙaro murmushi dan tasan nacin Magajiya batun yanzu ba. Tace, “To nahi yarda da wagga shawarar kau. Bara naga giccin Tinenen saina hiɗi maki ku tahi”.
      Da to Magajiya ta amsa, tare da ɗaukar buhun da garin masara ke ciki wanda dama shita shigo ɗauka ta fita. Da wata muguwar harara Inna ta raka bayanta tana jan tsaki. Ta sauke gyalen nata tana ƙudundunesa ta cusa cikin lalitar bujenta na ciki. Ganin ya kwanta babu mai ganewa ta fito a ranta tana ayyana. (Ai idan kinsan wata bakisan wataba magajiya).
     Shigewa tai cikin masu hidimar aikin abinci ta cigaba da harkokinta. Sai da taga kowa hankalinsa baya kanta tai wuff zuwa bayinsu tabi ta cikin dannin geza da akai musu sakamakon zubewar katangar bayin lokacin damuna daya wuce. Har yanzu kuma ALLAH baiba baba damar gyarawa ba.
       Saurin zaro gyalenta tai ta warware ta aza bisa kai. Cike da sauri da sassarfa ta dinga ratsawa ta cikin gonaki dan kar wani ya ganta........

★★★★

        
            A asbiti kam bayan tabbatar da Zinneerah ba suma tayi ba ruɗanin maganar likitace kawai ta haifar mata da hajijiya sai suka saka mata ƙarin ruwa. Hankalin su Gwaggo Laritu bai kwanta ba sai da likita yay musu bayani.
     “Ku kwantar da hankalinku tana cikin ƙoshin lafiya. Kuma Alhmdllhi bama suma tayiba. Yanayin da take cikine ya kawo hakan, da alama kuma ko karin kumallo bataibama kuka fito”.
      A kusan tare suka sauke ajiyar zuciya. Rabilu yaron Kawu Haruna daya kawosu yay saurin faɗin, “Likita to ko za'a samo mata wani abune taci?”.
         “Eh za'a iya. Amma a yanzu dai mun saka mata ƙarin ruwa ta samu barci. a cikinsa kuma akwai abinda zai taimaka mata akan yunwar, da alama dai kai ne mai-gidan nata ko?”.
      Murmushi kawai Rabilu yayi batare da ya amsawa likitan maganarsa ba. Sai dai Cikin ƙarfin hali duk sukai masa godiya. Amma a ƙasan ransu su kaɗai sukasan irin tashin hankalin da suke ciki game da wannan ciki na jikin Zinneerah. Suna tsananin tausayin yarinyar saboda halin data tsinci kanta a ciki a gidansu na rashin mahaifiya. Ga yayansu shi da babu duk ɗaya a gidansa saboda makircin matarsa Asabe. Sunyi iya ƙoƙarinsu dan ganin sun maidosa hayyacinsa tun tuni amma Asabe ta sake shiga ta fita ta raba tsakaninsu da shi. A yanzu haka ko mu'amula bayayi da kowa a cikinsu, ko maganar auren Karima bai sakasuba sai ji sukai a gari. Abin bai ɓata musu rai ba sosai saboda sunsan baya a cikin hayyacinsa ne sam. Yanzu haka maganar cikin nan Sa'a ce taje ta sanarma Gwaggo Laritu tana kuka, kuma da'ace ba Zinneerah abin ya shafaba cikin ƴaƴan Inna ne ko takansu bazasubi ba. Lallai lokaci yayi da zasuyi wani abu game da gidan yayan nasu kam a wannan karon. Dolene kuma susan wanda ya shiga mutuncin Zinneerah kar rayuwarta ta ƙarasa shigewa cikin garari sunaji suna gani.
        Kusan su dukansu haka suka dinga tanani a cikin zukatansu har ruwan da aka sakama Zinneerah ya ƙare, sai dai barci takeyi sosai. Sallar azhar su Kawu suka tafi yi massallaci. Itama Gwaggo Laritu saita fito dan neman inda zata gabatar da tata. Bayan duk sun idan da sallarne Rabilu yaje ya samo musu abinci dan su ɗanci, dan su kansu akwai waɗanda basu karya ɗinba a cikinsu..........

★★★★

           Sauri sosai Inna ta dinga zabgawa harta iso ƙauyen mahuta dake can yamma da su. Ƙauyene sosai dan gidajen garin bazasu gaza biyarba ma gaba ɗaya. A farkon shiga garin ta gamu da yara sun dawo ɗibar ruwa rafi. Tsaidasu tai ta ɗiba ruwan tasha sosai tana sauke numfashi a jajjere. Dan ba ƙaramin sauri ta zabgaba a tafiyar tata.
     Daga haka ta isa gidan dake ƙarshe a jerin gidajen ƙauyen. Tun a ƙofar shiga zauren gidan ta zabga sallama. Daga ciki akai gyaran murya tare da amsawa, sannan aka bata iznin shigowa. Babu kowa a soron, sai dai akwai ƙofar dake nuna alamun ɗakine, dan akwai labule da takalma a ajiye, sai wata a gefe ta shiga ainahin gidan kuma.
      “Gahwaranku dai”. Inna ta sake faɗa tana matsawa ga ƙofar ɗakin. Daga ciki muryar namiji dattijo ta sake amsa mata da “ALLAH yay mana aikin gahwara shigo”.
       Labulen ta ɗaga ta shiga ɗakin dake cike da shirgin da zama lissafasu ma ɓata lokacine, sai Dattijon dake zaune yana rubutu a allo da tawwada da alƙalami. Kallonta yay cike da fara'a kamar yanda itama take faman washe haƙwara.
      “A'a Asabe ce a garin yau?”.
“Wlhy nice malam kallamu. Kasan gobe ne ɗaurin auren ƴar wajen tawa, gashi kuma banzo na amshi abinda ka ce ba tun kwanaki idan auren yazo. Bayan nan kuma ga watama matsalar datake neman sake taso mani kuma”.
      “Tofa babbar magana. Ai dama inata tsumayen zuwan naki, dan kwanaki hudu da suka shige na shigo Danya ɗin nakejin auren yarinyar wajen naki ya tashi. Harma naita mamakin banji daga garekiba”.
       “Ayya, ka gahwarceni malam. Abubuwane sukaima kaina yawa a tsakanin nan wlhy. Amma zuwa nanɗin yana raina kodan a shiryamin yarinyar tunda kaima kasan dai yanda abubuwan suke ai”.
     Murmushi yayi yana ajiye allon da yake rubutun da gyara zamansa. Ya jawo wani ƙwarya yana tura mata gabanta. “Kinga komai ma na haɗa. dama ko bakizoba ni zanje ɗaurin auren gobe, to niyyata dama naje miki dasu ai”.
        “Kai madallah madallah malam kallamu, nagode nagode sosai da wannan karamci naka. ALLAH ya saka maka kaima da alkairinsa”.
     “Amin. Yanzu minene gudar matsalar kuma?”.
      Nannauyan nishi Inna ta sauke tana gyara zama. Cike da takaici da baƙin ciki tace yarinyarnan da uwarta ta bar mani ciki ya bayyana ga jikinta jiya. Tofa shine shaggun dangin uban nata sukazo sukai tsaye akan lamarin har suna iƙirarin sonjin ina taje kwanaki. Kasan kuma munyi aiki kwanaki akan rihe bakin kowa bai sake tambayarta ina taje. Itama kuma karta hwaɗi ma kowa ɗin. To wlhy yau malam kallamu suna neman ɓalloman aiki musamman ɗiyar wajena dake aure Sanni. Kasan nayi-nayi na rabata da yarinyar abun ya hwaskara”.
       Kai malam kallamu yaketa girgizawa yana saurarenta. sai da taje har ƙarshen zancenta ya fara magana. “Kamar yanda na hiɗi maki tun kwanaki uwar yarinyarnan shu'umace ta gaske. Dan duk da kin hiddata a gidan nan bawai ta barki bane, sannan tana aikoma yarinyar da wasu ayyuka, shiyyasa da munyi aiki akan yarinyar baya wani nisa yake warwarewa. To amma ke kin tabbatar akwai cikin kuma?”.
        Cikin wata lalatacciyar dariya Inna tace, “Ciki kau akwaishi malam kallamu, dan ƙuru-ƙuru ya bayyana kansa ga mutane”.
         “Tohwa babbar magana. Amma yanzu kunsan wanene yay cikin?”.
    “Inaaaa! Babu wanda ya sani, inada tabbacin acan inda nasa ƙawata ta kaita aikataune wani ya ɗura mata shi. Kasan yaran birnin nan akwai basira. Balle ƴar banzar yarinyar tanada ƙyau irin na uwarta. Yanzu haka jiran Hajji Lanti nake tazo naji miya hwaru. Amma itama bullum kakeji kamar an aiki bawa garinsu”.
        “Shikenan, yanzu dai ayau ɗinnan zanyi wani aiki. Kamar dai yanda na hwahinta ke dai bakiso yarinyar ta hiɗi ta sanadinki tabar gari ko?”.
       “Kwarai ko Malam Kallamu wannan shine hwatana. Dan nahi son kowa ya dinga kallonta da hita tai yawon tazubar ɗinta harta samo wannan cikin. Nihwa idan san samunane tabarma garin baki ɗaya yanda mutane zasu sake yarda komawa tai wajen farkan nata. Bazan ɓoye makaba zaman yarinyarnan a gidan na baƙantan rai, dan ji nake kamar har yanzu uwarta na tare damu, duk da na nisantata da garin tuni, to itama ɗiyar sonake na nisantata da Danya har abada, nahison na rayu gidan mijina dagani sai ɗiyana aradu”.
        Kai Malam Kallamu ya jin jina yana murmushi saboda shima mugunne na haƙiƙa, shiyyasa tasu tazo ɗaya da Inna. Kuma wai a haka shiɗin malamine, harda almajirai a ƙarƙashinsa yana basu ilimi🤦🏻.
      Ya sake haɗa mata abubuwa da yawa. Tare da tabbatar mata a daren yau zaiyi wani aiki akan Zinneerah. Ta ajiye masa kuɗi tana masa godiya ta taho akan sai gobe yazo ɗaurin aure zai tahoma da Karima wani haɗin neman sa'a a gidan Babawo.
(Humm ALLAH ya shirya mana zukatanmu. Babu wani banza daya isa baki ƙyaƙyƙyawar rayuwa a duniya sai UBANGIJI. Domin shima idan kura na maganin zawo yayma kansa mana. Idanma asirin kikayi akan wani kikaga yacisa dama can ƙaddararsa kenan koda bakiyi komaiba tunda ALLAH yay alƙawarin shigarsa wannan halin saiya shiga ɗin. Abindama jahilai suka gaza ganewa shine. Da yawan jarabawa tsanice na kaiwa ga nasarorin rayuwa ga bawa. Dan da wahala kaga mutum yaci wahala a rayuwarsa daɗi da farin ciki basu biyo bayansaba. Bawai dole sai a duniyaba. dan UBANGIJI yay mana alƙawarin samun babban tagomashi a lahira da yafi na duniyar komai. Dan kaci wahala a rayuwarka ba dolene sai kayi arziƙiba a ƙarshe. Ba dolene saika zama mai ɗaukakaba a ƙarshe. ba dolene saika zama tauraron al'umma ba a ƙarshe. UBANGIJI zai iya sakanka makane ta hanyar da kaima bakai zatoba. Amma fa saika zama mai juriya da haƙuri wajen karɓar jarabawarka da ƙaddararka. ALLAH kai riƙo da hannayenmu a komanmu😭🙏🏻).

★★★★

           Bayan farkawar Zinneerah a barci kusan ƙarfe huɗu suka baro Kusada zuwa danya. Kallo ɗaya zaka fahimci ransu a dagule yake su duka. Zinneerah kam bama a iya tantance halin tashin hankali da ruɗanin da take a ciki. Sam zuciyarta da ƙwaƙwalwar kanta basa aiki irin na kowanne mutum. Abubuwa da yawa ke zuwa mata a rai game da wannan ciki, har

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login