Showing 147001 words to 150000 words out of 223329 words
ɗin da tayo a waya. Shi kansa abin ya burgesa da bashi dariya. amma sai baiyiba yaɗan murmusa kawai yana ajiye wayar da dubanta cike da kulawa.
“Yaushe zakije ki gaida su Mammah?”.
A take fara'ar fuskarta ya ɓace, ta shagwaɓe fuska idanunta na cika da ƙwalla. “Bro ka barni Please basai najeba, kuma bama kace tana katsina ba tunda mukazo da Mahma?”.
“Kema ai katsinan zakije, gobe idan ALLAH ya kaimu zanje sai muje tare na baroki can ki biyo Mahma ranar biki”.
Hawayen da suka cika mata ido suka gangaro, sai kawai ta miƙe tabar dining ɗin ta shige ɗakin Hajiya iya. Binta yay da kallo kawai yana dariya a ransa. Dama tsokanarta kawai yakeyi, shima yaso zuwan amma Mahma ta hana, tace ya bari ai zata ɗakko su Mammah suzo wajen bikin dan dole suma dangin mahaifiyarsa su kasance ai tunda aure abin farin cikine ga kowacce zuri'a. Yanzu kuma Mammah ɗin kanta a zafi yake zuwansa bazai haifar da ɗa mai ido ba.
_________________________________
A washe garin da aka kai lefe hajiya iya ta samu Zinneerah a gidan Hajiya Falmata ita da Adilah. Yanda Zinneerah ta ƙara canjawa a cikin sati ɗaya ya saka hajiya iya jin daɗi matuƙa, hakama Adilah da sau ɗaya kawai suka taɓa ganin juna a london rungume tayi dan tunda ta ga yarinyar dama ta shiga mata rai, da Hajiya iya ta bata labarin komai kuma shima AK ya bata sai ta ƙarajin tausayi da ƙaunar Zinneerah, tare da ƙara taya ɗan uwanta murnar samun mata dai-dai da shi da zata kawo ma rayuwarsa farin ciki tunda Farah taƙi kwantar da hankalinta ta daina biyema Mammah ta riƙe mijinta kamar yanda ta fara a farkon aurensu.
Daɗin yanda Zinneerah tai ƙyau mai ɗaukar hankali yasa hajiya iya harda ƙarama hajiya falmata kuɗi tana jera mata tagwayen godiya. Cike dajin daɗi itama hajiya falmata tace, “Ai hajiya namaso ace daga gidan nan sai gidan mijinta za'a kaita, amma hakanma babu laifi tare dani zata tafi can ƙauyen muɗan ƙarasa abubuwan da suka rage”.
Hajiya iya taji daɗin wannan karamci na hajiya falmata, dan duk da yanda Zinneerah ta canja kogi bayaƙin ƙari. Da wannan damar hajiya iya ta zauna ta sakema Zinneerah nasiha, a yau kuma ta sanar mata an ɗaura mata aure amma bata sanar mata da waye ba. Share-share sai ga Zinni na kuka da hawaye tana kallon haijiya tamkar wata sokuwa.
Cike da kulawa hajiya iya ta kamo hannunta cikin nata da sigar lallashi tace, “Nasan bamu ƙyauta mikiba Inno, amma insha ALLAH wannan shine gatan da zamuyi miki na har abada. Ki saka a ranki wannan itace taki nasarar cin jarabawar, insha ALLAH nasan bazakiyi kuka ba a wajen wanda muka baki, inamiki fatan alkairi da tarin farin ciki mai ɗorewa a rayuwarki da rayuwar aurenki”.
Kasa magana Zinneerah tayi sai kuka, ta faɗa jikin hajiya iya tana abinta. Itace kuma aka ɗaurama aure bayan taci alwashin bazata taɓa aureba. Gaskiya da anyi shawara da ita da haka bata kasanceba, batason tai aure a gorantama little, batason tai aure a aibantata akan ta taɓa haihuwa a waje. Bata da burin daya wuce yin karatu mai zurfi a rayuwarta, sai dai kuma duk waɗanan burikan nata da farga basu kai daraja da kimar hajiya iya ba a wajenta. Ta cancanci sadaukar mata da komai kodan alkairinta a gareta. Takumayi imani hajiya iya bazata badata ga wanda zata cutuba insha ALLAH, dan haka zatai haƙuri tayi biyayya a gareta insha ALLAHU. Ashe shiyyasa mmn sadiq keta mata nasiha mai harshen damo ita da hajiya falmata.
Lallashinta sosai hajiya iya tayi da sake mata nasiha itama tana hawayen, dan dauriya dama kawai takeyi, amma harga ALLAH tana tsananin ƙaunar yarinyar, wannan kuma hukuncine na ALLAH mai saka soyayyar wani a zuciyar waninsa dominsa badan wani abu dake garesaba. Sannan ta sanar mata yau za'a kaita danya wajen babanta, daga can za'a ɗakkota insha ALLAH zuwa gidan mijinta.
Nanma dai Zinni tayi kuka dajin fargabar tunkarar garin nasu data baro bisa ga dalili mai ƙarfi, takumaji ɗokin zuwa taga babanta da akace ya dawo da ƴan uwanta kuma.
Hajiya iya na gidan har Zinneerah da hajiya falmata suka kammala shirinsu na tafiya, sai Saifudden da zai kaisu wanda ya iso gidan hajiya Falmatan daga baya ya samesu.
★★★★★
Koda suka baro gidan hajiya Falmata gidan mmn sadiq suka nufa domin ɗaukar Gwaggo Maryama, ai ko Zinneerah nayin arba da ita ta faɗa jikinta tana kukaama. Ta basu tausayi daga ita har maman sadiq, to amma wannan shine kawai gatan da zasuyima rayuwarta koda ace babu ransu ta dinga tunawa sun mata gata. Dan little ga mahaifinsa kawai zai kasance itama ta samu kwanciyar hankali da nutsuwar zuciya. Lallashinta suka sake zamanyi da mata nasiha, kafin Gwaggo Maryama ta shirya su fito dan da ita zasu wuce danya kafin su Mmn sadiq su biyosu suma daga baya.
Tunda suka ɗauki hanya Saifudden ne kawai ke hira da hajiya falmata da Gwaggo Maryama, itako tayi shiru lafe cikin kujera idanunta a lumshe. Kasancewar tafiyar ba ita kaɗai bace sai taji fargabar tunkarar danyan ta ragu mata a zuciya. Har suka iso gidan mutun ɗaya suka ɗauka hanyar kusada bata buɗe idoba. Sai da taji sun hau hanyar Danya ta buɗe idanu da kallon hanya cike da kewar garinta da tunano abubuwa masu yawan gaske da suka gudana. Isowarsu cikin garin yasa zuciyarta karyewa, sai gata tana hawaye shaɓe-shaɓe.
Zuwa yanzu kam ƴan Danya sun saba ganin yawan shigowar waɗanan manyan motoci, dan haka kai tsaye aka fara ƴan ƙananun maganar cewar angon Zinneerah ne yazo.
Su Zinneerah dai basusan anaiba, dan motar na tsayawa a ƙofar gidansu daya sha gyaran biki da aketa shirye-shiye sai zuciyarta ta ƙara karyewa. Itace ƙarshen fitowa jiki a sanyaye, sai da ta ƙarema anguwar tasu kallo da yara da suka baibaye motar waɗanda takeda tabbacin babu wanda ya shaidata, wasuma basu santaba. Murmushi tayi a karo na farko da ambaton Alhmdllhi cikin matuƙar rauni.
Da sauri ta buɗe idanun nata saboda jin maganar baba dake fitowa yanama Saifudden sannu da zuwa. Juyawa tai a hankali ƙirjinta na harbawa da sauri-sauri. Shima baban tunda idanunsa suka sauka akanta dukkan maganar bakinsa ta gagara fita. Yay tsai yana kallonta zuciyarsa fal wasiwasi. Tabbas fuskarnan dai ta ɗiyarsace, kuma irinta tsohuwar matarsa mafi soyuwa a garesa. Sai dai kuma yana tantama ace Zinneerah ɗinsa ce ta zama budurwa haka tamkar wata jinin larabawa. (Dan gyaran datasha ya sake ƙawatata da ƙyawu mai ɗaukar hankali)
A wani irin slowly Zinneerah ta nufi baba, batama san ta faɗa masa a jikiba ta fashe da kuka ba. Hakan yayi dai-dai da isowar Tinene ƙofar gidan wadda tun ɗazun aka aiketa amma sai yanzu take dawowa gidan, dan yanzu bata samun damar fita yawonta saita hanyar aikan.
Da mamaki take kallon wadda ke runme musu da baba, dan haka cikin sassarfa ta nufi cikin gidan kai rahoto. A zabure Inna data gama yima yarinyar karima wanka ta miƙe, hakama Sa'a dake wanke-wanke. Karima ma madai da Yaya Atine dake a cikin ɗaki sai gasu waje wuff babu shiri. Yaya Gajeje dake can gaban murhu ita da ɗiyar Baba Sabi'u suna suyar naman ragon sunan Karima suma dai duk duban Tinenen sukai, amaryar baba dai datasan ina zancen ya dosa tana ƙofar ɗaki zaune tana gyaran ƙumba da tsohon cikinta, murmushi kawai tayi hankali kwance. Kafin bakin wani ya samu damar furta kanzil sai ga baba ya shigo baki washe yana sharar ƙwalla, hannunsa riƙe da Zinneerah dake kuka rurus. Hajiya Falmata da Gwaggo Maryama biye dasu suna faman murmushin jin daɗi.
Yaya Gajeje ce ALLAH ya bama ikon gane Zinneerah, a take ta saki ludayin hannunta tana ƙwalalo idanu waje da faɗin, “Zinneerah!!”.
Da gudu Zinneerah ta saki hannun Baba tai kan Yaya Gajeje. Bata damu da a yanda yaya Gajejen takeba ta faɗa jikinta suka saki kuka tare. Tuni Sa'a ta saki soson wanke-wanke itama tayo kansu. Su kansu su Yaya Atine da ba ƙaunar Zinneerah ɗin sukeba, kuma tunda aka kawo kayan lefen nan nata ƙiri-ƙiri suka nuna hassadarsu suda Inna basu san sanda suka nufo ƴar uwar tasuba suka haɗu wajen rungumeta.
Hakan da sukai ya matuƙar saka baba jin daɗi, yayinda Inna ta daka musu wata irin gigitacciyar tsawa. Sai dai ina su bama susan tanaiba. Amaryar baba kuwa tashi tai da ƙyar tanama su Gwaggo Maryama barka da zuwa, waɗanda sai yanzu Inna tama gansu. Gabanta ne yay matuƙar faɗuwa datai tozali da fuskar Gwaggo Maryama, dan sarai ta ganeta. A kiɗime tace, “Dangin Hauwa a gidana?”. Karaf kuwa sai a kunnen baba. Kansa tsaye yace, “Hauwarma tana nan tafe a gidan naki”. Ya raɓata ya wuce abinsa dan tabarma zai amsa ya kaima Saifudden.
Ba ƙaramin dukan ƙirjinta furucinsa yayba. Tai baya tana neman faɗuwa ALLAH ya taimaketa ta dafe bango. Babu wanda ya lura da halin da take ciki dansu ta murnar ganin ƴar uwarsu sukeyi.
“Zinneerah kece kika koma haka kamar wata ƴar ƙasar waje?”. Yaya Gajeje ta faɗa tana sharema Zinneerah hawayenta, itako murmushi kawai take ga hawaye shaɓe-shaɓe.
Sa'a dake riƙe da hannunta tace, “ALLAH na gode maka daka nunamin wannan rana da naketa mahwalki da fatan gani, nagodema UBANGIJI daya maido ƴar uwata gida cikin kamala da mutunci harda igiyar aure akanta”.
Yanda take maganar da kuka ya sake raunana zuciyar Zinneerah dasu Gwaggo Maryama da amaryar baba ta sama tabarma a ɗakinta, dan suna jiyosu. Sake faɗawa jikin Sa'a Zinneerah tayi tana sakin wani sabon kukan.
Sai a lokacin baba daya dawo ɗaukama Saifudden buta zaiyi alwala yay sallar la'asar ya ɗauka hanyar komawa ya lura da halin suma da Inna ke ciki. Sallallami ya fara da nufarta, a take suma hankalinsu ya dawo kanta duk suka juya. Ita Zinneerah ma sai yanzu idanunta sukaga Innar.
Ruwa aka yayyafa mata ta farfaɗo, tana buɗe idanu sai akan Zinneerah, ai sai kawai ta fashe da kukan daya bama kowa mamaki da tsoro a wajen. Tashi Baba yay abinsa ya ɗauka butar data kawosa ya fice.
Zinneerah ta matsa jikin Inna tana hawaye da nufin rungumarta, hankaɗeta Inna tai cikin kuka da faɗa. “Munahika karki taɓeni, kinje kin gama yawon tazubar ɗinki zakizo ki goga mana ƙanjamau. To idan uwarki tayo asiri da rufe ido da bakin kowa akan hakan ni na gagareta, asirinta bazai ciniba. Nasan komai kina ikko kina karuwanci, shima shegen da aka ɗaura muku auren ƙaryar abokin cin mushenki ne. ALLAH ya wadatanki tambaɗaɗɗiyar yarinya gantalalla”.
“Kece gantalalliya, ni Sulaiman ban haifi gantalalliya ba”.
Baba ya bata amsa a fusace yana nunata da ɗan yatsa. Ya cigaba da faɗin, “Wlhy kika ƙara aibantamin ɗiya koda da furucin bakine saikin bar gidan nan, bari kuma nahar abada tunda ke bakisan ANNABI ya fakuba mara mutunci kawai.
Wani irin waro idanu Inna tai tana kallon baba, cikin rawar baki tace, “Malam ni kake cewa zan bar maka gida akan Zinni?”.
“Da giduma kuwa, harda jan kati”.
Da sauri Zinneerah ta shiga girgiza kanta tana hawaye. “Baba dan ALLAH kayi haƙuri ka daina faɗi, Inna uwace a gareni, komai ta faɗa a kaina ba laifi bane”.
Baba ya buɗe baki zai bama Zinneerah amsa Gwaggo Laritu da Tinene taje kaima rahoto ta shigo gidan. Zinneerah na ganinta ta miƙe da gudu tai kanta. Sai kuma gasu baba Rabilu suma harda ƴaƴansu. Cikin ƙanƙanin lokaci gidafa ya haukace da sabon murna. Makwafta nata shigowa ganin Zinni. Kafin kace mi zance ya fara yawo amarya Zinneerah tazo kamar an sata a injin gyara mutane ta koma balarabiya.
Haramin da gidan ya ɗauka yasaka kowa mantawa da wata Inna. Har Saifudden ma ya wuce su Gwaggo Maryam basu saniba. Aiko dai a wannan rana Zinneerah bata iya ta samu kantaba har dare, sai can kusan goma yaya Gajeje ta janyeta ɗaki ta bata abinci taɗanci. Daga haka aka zaman sake kafa sabuwar hira dan har zu baba Sabi'u suna gidan har lokacin basu tafiba. Zinneerah ta basu labarin daya sakasu kuka sosai dan tausayi.
Suka shiga godema ALLAH daya saka Zinneerah faɗawa a hannun nagari har ya sadata da mahaifiyarta. Wannan rahamarsace da jin ƙansa ba wayo ko dabarar waninsu ba. Sun kuma tabbatar a katsina aka lalatama Zinneerah rayuwa itama bada sanintaba, saboda a yanda ta basu labarin zuwanta. Inna nata zaginta da tsinarta akan ta mata sharri ita ƙarya Zinneerah tai mata akan cewar itace tasa tabi hajji lanti. Babu wanda yace da ita uffan akan hakan kaf ɗinsu.
Itama Zinneerah tayi kuka jin labarin yanda baba ya kasance, amma tayi farin cikin ƙara aurensa wanda yasa Inna ji kamar ta kasheta, sai dai babu damar yin magana baba ya kafa sharaɗi. Yanda kuwa yayin ta tabbatar zai iya sakin nata akan Zinneerah. Shiyyasa tai gum da bakinta tana binsu da ido, lokaci-lokaci takan fakaici ido ta share hawaye. Dan ga abin faɗa fal a bakinta amma babu damar faɗin sai tsinar Zinneerah dai take kawai.
Murnar dawowar Zinneerah yasa yaya Gajeje kwana a gidan, acewartama sai biki ya tashi kuma kenan. Aiko kusan kwana sukai hira da Zinneerah dan ɗaki ɗaya suka kwana. Hajiya Falmata nason cigaba da aikinta dole ta haƙura, sai dai ta bata abubuwan sha da abinda yake mai sauƙi da bazai takura Zinneerah zaman hira da ƴan uwantaba............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
*Page 49*
_________________________
Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗
Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali
Ina masu pimples
Tabo(spot)
Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance
Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba
Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki
Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu
Sannan munada beauty kit🤗duk me bukatan (flawless skin/perfect glow) toh yy kokari yamallaki set dinnan wn zncn baa mgn🧚🏻♀️cuz duk inda kayi se ankalleka😀
Buh gsky wnd besan yy haske karyayi using set din cuz gsky yn sa haske buh bn bleaching ne b zaidai murje fatane nd bring out that hidden beauty in you😍
Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself
100%tested nd trusted
Beauty kit:11k
Soap price:3k
Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free
Maiso kindly message 08062991549
Call 08064532391
Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏
Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝
Mg's skincare
_________________________
*Page 49*
...........Koda suka wayi gari lafiya ma da ƴan zuwa tabbatar da dawowar Zinneerah suka tashi, dan babu kunya mata keta shigowa da ƴammata da yara. Duk da abinda ya faru a baya yana a zukatansu kwarjini da cikar kamalar Zinneerah a yanzu ya hana bakinsu aibantata, dan dama wasu suna zuwane dalilin wancan abun daya faru bawai dan Zinneerah ta kasance zinari ba.
Itako duk da kasancewar ta miskila haka taita dauriyar musu murmushi da nuna kulawarta garesu babu wani wulaƙanci ko yarfi. A ranarma dai duk yanda taso samun kanta bai yuwuba, haka suka yini amsar baƙi da ƴan tsirku har yamma.
A ɓangaren Inna kuwa a ranar taso bazama wajen malamanta baba daya gama karantarta tsaf ya hanata fita, yama kafa mata sharaɗin har Zinneerah tabar Danya idan ta leƙa waje a bakin aurenta. Wannan al'amari ya mata ciwo, ta dinga zazzaga masifa da jidali masu shigowa na mata dariya. Yaran nata da su Gwaggo Maryama kuwa babu wanda yabi takanta. Garama Zinneerah takance “Kiyi haƙuri Inna”. Aiko wannan kalmar haƙuri na mata zafi a rai fiye da masu mata shiru. Itako Zinneerah har cikin ranta batajin daɗin ganin yanda Innar ta koma kamar wata zararriya.
Da daddare aka buɗe mata kayan lefenta ta gani ita dasu Gwaggo Maryama, abin ya bata mamaki sosai, ta kuma jinjina ƙoƙarin su hajiya iya. Suna gama ganin kaya Hajiya Falmata ta