Showing 213001 words to 216000 words out of 223329 words
magana raɗa-raɗa. “Ko tausayinama baƙyaji kin barni da kwana da little ke kinacan kina morewarki ko?”.
Dariya zancen nasa ya bata, amma sai batayiba tai murmushi da ƙoƙarin ƙwace kanta. “Yayanmu ai amfanin mata biyu kenan, ni ina fama da wannan fiɗan inani ina ɗaukarka. Kawai aunty Farah ta dawo kaga ni sai nayi arba'in”.
Gani tai ya saketa baki ɗaya yana tsuke fusaka. Ya watsa mata harara yana jan guntun tsaki, batare da ƙara cewa komaiba ya juya ya fita a ɗakin. Bayansa tabi da kallo tana murmushi, a fili tace, ‘Uhm ka gama mazuranka ne dan nasan kana son kayarka’.
Iskeshi tai yana zuba abincin da kansa. Batai maganaba ta matsar da little kusa da shi ta zauna, “Ina waje. ciwon Alhaji?”. Ta faɗa tana kamo ƙafar little. Nuna mata yayi, ta buɗe man zafin ta shafa masa yana wani shii da baki da yarfar da hannu. “Daddy kace tayi a hankali zafi”.
“Oh ALLAH, ALLAH yaron nan saika kashe auren da babu soyayya, yanzu shafa maganinne da zafi?”.
Zancen nata ya bama AK dariya amma sai ya gimtse bai yiba. Yadai kamo hannun little ɗin yana bata amsa a daƙile. “Dama can babu soyayyar ne ai”.
Tasan da biyu ya faɗa, dan haka taja bakinta tai shiru. Sai dai ta cigaba da kallonsu yanacin abincin yana bama yaronsa har suka kammala.
Bai wani jima da gamawarba ya mike yana kallon agogo. “Saifudden zai kawo muku cefane. Dan bazan dawo ba sai dare”.
Mikewa itama Zinneerah tayi da faɗin, “ALLAH ya saka da alkairi ya kara buɗi, miza'a dafa maka da daren”.
Kallonta yay cikin ido sonta da buƙatarta na ɗawainiya da shi, yaja numfashi da duban inda little yake. Ganin hankalinsama ba'a kansu yakeba sai ya sake kallonta. “Abinda nakeso a dafamin kam ai ba bani za'aiba. Sai dai nayi manage da tuwo”.
Murmushi tayi tana maida kanta gefe dan tasan ina ya dosa, ta hau tattara kwanikan, “Uhm ni Yayanmu ALLAH fitina kake ƙarowa kullum, na kawo mafita kuma kaji haushina”.
“Ke dai kika sani” ya faɗa yana nufar ƙofa.
Murmushi kawai tayi ta cigaba da abinda take. Sai da ta kammala ta tisa ƙeyar little da baima lura da fitar Daddyn nasaba ta rufo sashen. A sashenta ta samesa zaune suna gaisawa dasu Yaya Gajeje ƴan biyu duka na'a jikinsa yana kallonsu zuciyarsa fes da farin ciki. Inda yake little ya nufa ita kuma ta nema waje ta zauna. Ya ɗan jima a falon suna maganar jikin Inna daya fara lekawa tana barci dasu Yaya Gajeje kafin ya basu yaran da musu sallama ya fice, bayan ya jefeta da wani kallon duk randa na kamaki. Murmushi mai sanyi kawai tai masa da rakashi da addu'a.
Shima daga nan sashen Farah ya shiga inda ya samu su Mammah na karyawa. Sun gaisa nanma yaɗan zauna suka taɓa hira sannan yay musu sallama yabar little anan ya fice.
★★★
Daga ranar Zinneerah bata sake masa zancen Farah ba har ALLAH yasa sukai arba'in. A randa tai arba'in ɗin kuma su Mammah ke shirin tafiya katsina duba su Farah daga can su wuce london.
Gaba ɗaya Zinneerah sai ta shiga damuwa. Dan zamansu a gidan ba ƙaramar shaƙuwace ta shiga tsakaninsu ba. Ganin shine zai kaisu katsinar ta sake daurewar masa zancen dawowar Farah sai ya balbaleta da faɗa, duk da tasan bayason wargi bata taɓa ganin fushinsa irin yau ba. Ita kuma yanda yake mata ihu akai yasata fara kuka.
Suna haka Mammah ta shigo falon. Saurin share hawaye Zinneerah tayi tana ƙaƙaro murmushi da yima Mammah ɗin dake binsu da kallo sannu. Daga haka ta zame ta gudu ta barsu, dan tasan tunda Mammah din ta shigo nan da kanta magana zatayi da shi.
Da kallo tabi Zinneerah harta fice kafin ta maida ga AK dake ta wani bata fuska. “Abdul-Mutallab mi kaima yarinyarnan?”.
Guntun tsaki yaja yana murza goshinsa. “Mizan mata kuwa Mammah, itace da neman fitina kawai”.
Shiru Mammah tai tana kallonsa cike da nazari, sai kuma taɗan girgiza kanta da cewa, “Fitina kamar ya? Ai kowa Yasan Zinneerah bata da kwaramniya, dan nidai a zamanmu gidan nan banga wani abun ashsha daga garetaba sai dai ajizanci irin na ɗan adama kawai. Amma yarinya mai kawaici da kunya ga haƙuri. Sai dai idan kai ne da laifin tunda sarai na san halinka bawai baƙona bane. Miya haɗaku?”..
“Nifa Mammah babu abinda nai mata. Kawai ta isheni da zancen Farah ne”.
Kallonsa kawai Mammah keyi dan maganar yanayintane da faɗa sosai. Ta sauke numfashi da gyara zamanta. “Abdul-Mutallab nasan Farah mai laifine tabbas, amma karka manta harda gudunmawarmu, kuma maganarta da yarinyarnan take maka tasan kantane. Dan wannan haline irin na mutanen ƙwarai da sake tabbatar maka ita mai tarbiyyace da hangen nesa. Ni bazance dole ka dawo da Farah gidankaba, amma zan baka shawarar ka daina ƙuntata yarinyarnan akan abinda ba laifinta bane saima alkairi da takeson ɗoraka akai. Ita rayuwa komai ɗan haƙuri ne ai. idan akai haƙurin sai komai ya zama labari wataran”.
Shi dai kansa na ƙasa baice mata komaiba harta gama zancen Farah da Zinneerah ta ɗakko abinda ya shafesu sannan ya tsoma baki.
Duk da Zinneerah tasan su Mahma basu rasa komai na rayuwaba sai da ta shirya musu tsaraba domin girmamawa. Musamman turarurrukan khumrah dana wuta da a koda yaushe suke yaba kamshin a jikinta da gidanta. Hakan yasa tasa Hajiya Falmata ta haɗa musu na musamman akai musu packaging nashi.
Sai gata harda ƙwalla da zasu wuce. Bama ita ba hatta su Yaya Gajeje sunji babu daɗi. Inna ma da take ɗan magana yanzu kuma takan ɗan motsa jikinta tafiyace dai batayi sai da ta nuna alhinin tafiyar tasu, dan kullum sai sun shiga sun gaidata sau uku a rana babu fashi.
Duk yanda Zinneerah ke share hawaye AK na kallonta ta mirror. Yay ɗan murmushi yana cizar lip ɗinsa dan yau kam yasan ango yake tunda Mahma ta ɗaure mata ƙugu sai da tai arba'in duk da ba haihuwa tayi da kanta ba.
Baisan Mahma ta masa wayo bane tanata gyare masa Zinneerah ɗin a ɓoye. Ga gyaran Hajiya Falmata datake ɗorata a layi, hakama Hajiya Iya kullum cikin faɗa mata dabaru takeyi. Ita kanta tasan idan taje hannun boss din nata sai ta yabama aya zaƙinta. Shiyyasa yau duk take a tsure.
Kasancewar da little ya tafi suna wucewa mai ƙunshin da zatai mata tana isowa. Ƙunshi akai mata na gani na faɗa na jan lalle da baƙi, Yaya Karima ta yarfa mata kitso kananu da ya fiddo mata ƙyawunta sosai musamman yanzu data yi wani bulɓul da ita tamkar ba itace tasha fama da rama lokacin cikin ƴan biyu ba.
Kasancewar basu zauna wasaba kamar wasa kafin la'asar suka kammala komai tai fes da ita. Dama tunda ta fara zaman jegon nan take dilke jikinta da kayan gyaran fata na musamman da Hajiya Falmata ta haɗa mata ga kuma na Mahma. A gurguje ta shiga gyaran sashe. AK duk da bawani ƙura yayi ba. Sai da ta tsaftace komai yay mata yanda takeso ta baje kalolin ƙamshinta masu rikitashi. Sanda ta dawo sashenta ma su Mama A'i sun gyare ko ina sai ƙamshi yake.
Waya tai zamanyi da AK ɗin taji kosun taho. amma yace mata yana dai shirin tahowar. Taji daɗin haka dan ta samu damar shiga kitchen kenan ta haɗa abinci da kanta. Dan tunda ta fara zaman jegon nan kullum cikin ƙorafi yake akan abinci, idan kaji baiyi maganaba Mahma ce tai girki da kanta saboda shi.
Lafiyayyen abinci ta shirya masa da tasan zai gamsar dashi. Tare da haɗaɗen shayin barnawa daga Hajiya Falmata da kalolin kayan sha na zoɓo da kunun aya. Suna kammalawa dan da taimakon Mama A'i tayi ta bar mata idawa bayan ta ɗiba na AK takai sashensa.
Wanka takeson shiga Amaan ya wani saka kuka shi a dole yunwa yakeji. Ɗaukarsa tai tana dungurinsa da kiransa acici like Daddynsa. Tana gama bashi a tsaitsaye itama Anam ta saka tata rigimar. Kanta ta dafe da amsarta Yaya Gajeje na dariya. “Wai yaran nan mi kuke son maidani ne halan? Ku gama naku shima yazo ya isheni da tasa rigimar”.
“Ai daidai kenan”. Cewar Yaya Gajeje tana dariya. Murmushin jin kunya Zinneerah tayi da ajiye Anam din ta shige cikin dan watsa ruwa...........✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
_______________________
*Page 68*
..........Sai da Zinneerah ta fara gabatar da sallar magrib bayan fitowarta wanka sannan ta zauna ta tsara kwalliya ƴar gaske, tare da baje lungu da saƙo na jikinta da ƙamshin mayun turarurrukan ta sabbin haɗi daga Hajiya Falmata. Ta ɗakko less da yaji ɗinki mai ƙyau da tsari ta saka tare da kashe kan ɗauri. Awarwaraye da sarƙa ta zuba kai kace wani biki zata. Ta sake ɗorawa da wasu turarurrukan sannan tai zaman sallar isha'i. ALLAH ya sota ƴan biyu suna goye a bayan Yaya Gajeje da Mama A'i.
Sauri-sauri ta kammala ganin har isha'i su AK basu shigoba. Koda ta fito su Yaya Gajeje wani ihun dariya suka ɗauka da yaba wannan wanka nata. Kunya tasata jan mayafi ya rufe fuskarta.
Mama A'i da yake itama a ce, babu yawan magana sai lalata tace, “A'a wannan gayun bai kamata ki kaisa turaka ke kaɗai ba. Bara na ɗakkoma su Alhaji ƙarami kaya a canja musu suma dasu za'a”.
“Wannan zance nakan hanaya Mma A'i”. Yaya Karima ta faɗa tana dariya. Zinneerah ta tura baki kaɗan tana faɗin, “Gaskiya nai dai a'a, salon su batamin gayu”.
“Iyee, lallai Zinni binni ta buɗe miki ido da baki, a gabana babu kunya”. Cewar Yaya gajeje tana riƙe haɓa.
Dariya Zinneerah ta shiga kwasa. Ta faɗa ɗaki tanayi da faɗin, “Yi haƙuri Yaya gajeje na tuba”.
Suma dai dariyar suke tayata harta ɗakko kayan da za'a canjama ƴan biyu. Su Mama A'i suka shiryasu tsaf sannan Zinneerah ta kwashesu. Dan Yaya Gajeje korata tai wai ta tafi can yazo ya sameta zaifi jin dadi. Su Yaya Gajeje tsoffin masoyane da sukasan takan maza da muhimmancin irin wannan ranar. Aiko shawararsu Zinneerah ta bi. Dan dama itama akwai nata shirin a ƙasa.
AK bai shigo gidan ba sai wajen tara da rabi na dare. A gajiye yake matuƙa. Dan haka kai tsaye ya nufi sashem Zinneerah ɗauke da little dayay barci. A falon farko ya samesu dan sunfi zama nan, kai shi baima taɓa samunsu a falon ciki ba dan daga shi sai Zinneerah ɗin ke shigarsa da bedroom dinta na ciki, saiko little.
Mama A'i ta mike tana amsar little ɗin da masa sannu da zuwa. Suma su Yaya Gajeje sannun suke masa. Cike da mutuntawa yake amsa su yana baza idon ganin ta inda Zinneerah zata ɓullo da twins nashi. Ganin dai babu alamarta ya sashi leƙa Inna sannan ya fice.
Gulmarsa su Yaya Karima suka shigayi suna dariya. Dan yanda yaketa kalle-kalle sunsan matarsa yake son gani, gashi su kuma sun yi gum bama su nuna sun fahimcesaba.
Shiko harya ɗan shaƙa dan ya zata abinda ya faru tsakaninsu ɗazun da safe ne ya sata fushi. Sai da ya shigo sashensa ya shaki wani mayataccen ƙamshi daya nema karar masa da man kai lokaci ɗaya sannan ya sauke ajiyar zuciya. Taku yake tamkar mara laka a jiki yana bin falon data sakama hasken wuta kaɗan da kallo. Bukatar fara wanka ta sashi nufar bedroom ɗinsa ransa fal waswasin ina ta shiga.
A bedroom ɗinma ƙamshin da yafi na falo ɗaga masa hankali ya shaƙa. Kasancewar wutar ɗakin a kashe dindim ta sashi fara lalauben makunnar fitilar. Ɗan zabura baya yayi lokacin da haske ya gauraye ko ina a ɗakin. Kyawawan idanunsa kuma sukai masa gani na musamman daya sakashi hangame baki. Zinneerah ce zaune a tsakkiyar gadon lulluɓe tamkar sabuwar amaryar da aka kawo ɗakin miji yau. gefe da gefenta Amaan da Anam ne cikin showals suna barcinsu hankali kwance suma cikin gayu.
Jiyay gaba ɗaya yana neman daburcewa da salon nata. Ya shiga takawa a hankali zuwa gaban gadon jininsa na tsinkewa tamkar manjan da yaji zafin wuta.
الْحَمْدُ للهِ الَّذِي بِنِعْمَتِهِ تَتِمُّ الصَّالِحَاتِ .
*_Alhamdu lillahil-lazee bini’imatihi tatimmus-salihat._*
_Godiya ta tabbata ga ALLAH wanda saboda ni'imarsa ce kyawawan ayyuka suke cika._
اَلْحَمْدُ ِللهِ عَلَى كُلِّ حَالٍ.
*_Alhamdu lillahi ala kulli halin_*
_Godiya ta tabbata ga ALLAH a cikin kowane hali._
Ya faɗa lokacin da yake kaiwa zaune bakin gadon. “Dan ALLAH ki zauna a haka karki motsa harna fito a wanka, dan wannan sirrin ya wuce na gani da ido kawai ko fatar baki”.
Zinneerah da duk take jinsa tai murmushi batare datayi ko tari ba balle ta motsa. Bai damuba shima dan mikewa kawai yay ya nufi toilet.
A yanda ya barta ɗin kuwa haka yazo ya sameta. Tsane jikinsa yake amma ya kasa daina kallonta ita da yaran daga inda yake. Turarurruka ya cuɗe jikinsa da shi da ɗaukar wando fari ƙal iya cinya ya saka da ƙaramar riga armless ya haura gadon
Zama yay a gabanta ya tanƙwashe kafafunsa suna fuskantar juna. Yasa hannayensa biyu ya kamo bakin mayafinta ya ɗaga sama ƙyaƙyƙyawan fuskarta na bayyana garesa tana neman zautashi da wani sassanyan murmushi.
Da ƙyar ya iya fisgar numfashin dake neman ƙwace masa yana wani mar-mar da idanunsa dake neman zubowa jikinta. Luuu ta ɗanyi da idanun tasa tafukan hannunta ta rufe fuskarta. Hakan da tai ya bashi damar yin tozali da ƙyaƙyƙyawan ƙunshinta.
“My Neerat zaki halakani wlhy”. Ya faɗa a wani irin sassanyan sauti da ita kanta sai da tsigar jikinta ta tashi. Hannayensa duka ya ɗaura akan nata yana janyewa daga fuskarta. Cikin idanunta ya zuba birkitattun nasa yana faɗin, “Ina ƙaunarki da yawan yawa My Neerat, zaki zautan ɗan Shira da salonki”.
Zinneerah dake amsar saƙwanninsa ta cikin idanunsa itama da wata irin muryar da batasan tanada shi bace, “أَحَبَّكَ الَّذِي أَحْبَبْتَنِي لَهُ.
*_Ahabbakal lazi ahbabtani lahu._*
_Wanda ka so ni saboda Shi, kai ma Ya so ka Yayanmu. Kuma nima ina ƙaunarka”_.
Gaba dayanta ya cacumo jikinsa ya rungumeta tamkar zai cusata a fata da ɓargon jikin nasa gaba ɗaya. Cikin fisgar numfashi ya shiga laluben bakinta ya manne a cikin nashi jikinsa na wani irin tsuma na zalamar son kasancewa da ita. Bata iya ta hanashi ba. Sai ma haɗin kai data shiga bashi.
Sai da labarin ya nema yin nisa kuma tsoro ya kamata, dan gasu Anam a gadon karsu taushesu. cikin taimakon da ALLAH yay mata sai Amaan ya farka da kuka. Da ƙyar AK ya iya sakinta yana cizar lip. Itama ta mike da ƙyar daga jikinsa dan tunaninta kar hayesa sukai. Ganin babu abinda ya samesa ya sakata sauke ajiyar zuciya da hararsa. “Ɗan ɗagwai na zatama hayeka akai”.
Idanu Ak ya buɗe da ƙyar yana duban inda Amaan ɗin yake. Kafin ya yunƙura da ƙyar ya matsa garesa yana dungure masa kai. “Haka kawai ka ɓatamin wasa. Shiyyasama bana Baffan da kai yaro”.
Murmushi Zinneerah dake kallonsu tayi, ta sauka ƙasa gaba ɗaya tana kai hannu ta ɗaukesa dan tasan yunwa yakeji. Komawa AK yayi ya kwanta dan cikinsa ya ƙulle tamau. Har Zinneerah ta gama shayar da Amaan ta maidashi ta kwantar sannan ta dubesa.
“Yayanmu ga abinci fa a falo kar dare ya ƙara zurfi”.
Lumsassun idanunsa ya buɗe a kanta. Akan laɓɓansa da ƙyar ya furta, “Ke kaɗai kin wadatar dani”.
Dariya zancen nasa ya bata dan tasan dai shi da abinci sai ta ALLAH. Ta miƙe tana fadin, “Nidai daka daure kaci bara na kai su Anam ai musu shirin barci. Uffan bai iya ce mataba harta fice a ɗakin. Bai kuma iya motsawa ba yana a inda ta barsa har kusan mintuna talatin sai gata ta shigo ɗauke da tea. Ajiye masa tai tana faɗin, “Ga tea nanto Yayanmu bara na ɗakkosu.”
Bai motsaba bai kumayi magana ba harta sake ficewa yanzu ma. Bata jimaba yanzu ta dawo ɗauke da ɗan gadon su Amaan. Ta ajiye ta koma falonsa inda Mama A'i ta rakota da yaran ta amso su sannan tai mata sai da safe dan tama su Yaya Karima sallama.
Jin ta dawo tana kwantar dasu ya sashi miƙewa da ƙyar zaune. Kofin tea ɗin ya ɗauka ya hau sha dan da gaske yanajin yunwar ma. Sai dai duk inda tai yana binta da kallo harta gama hidimar yaran tai musu addu'a. Dan ma sanye take da zumbulelen hijjabi a saman kayan barcinta.
Sai da ya kammala yaje yay brush itama taje tayo dan ta kimtso kanta daga can, alwala kawai tayo da brush ɗin ta fito. Tsugunne gaban gadon su Anam ta samesa yana musu addu'a fuskarsa ɗauke da murmushi