Showing 120001 words to 123000 words out of 223329 words
samun gamsuwa akan abinda zai fito, dan haka suna isowa suma su Mmn Sadiq suka iso ɗauke da Little.
Yanako ganin AK ya maƙale masa, duk da ɓacin ran da AK ke ciki sai da yay murmushi yana mai rungume little a jikinsa. Ganin yaronma da yayi sai yakeji a ransa ALLAH ma yasa ya kasance nashi ɗin, dan har cikin ransa wata irin ƙauna yake masa mai ƙarfi da saka zuciya nutsuwa.
Cikin mutunta juna suka gaisa, inda mamaki ya cika Dr Mahmud saboda ganin Abba. Shima Abba daya ganesa sai wani tunani yazo masa. Cikin kasa jure abinda ke ransa yake tambayarsa ko ina bawan ALLAHn nan daya sakama little sunansa?.
Kai tsaye Dr Mahmud dake dariya ya nuna AK, “Baba ai gashima zaune, ina takwaran nasa kuwa? Nasan ya girma yanzun ko?”.
Da sauri Abba ya kalli AK da Little ke a jikinsa zuciyarsa na bugawa. Cikin ɗan rawar murya yace ai ga yaron nan a hannunsa”.
Ba Dr Mahmud ba, hatta AK sai da zuciyarsa ta harba. Yay saurin duban Abba da faɗin, “Uncle kana nufin kaine wanda ya bani damar zaɓama yaro suna shekara uku data shuɗe?”.
“Tabbas nine kuwa. Kuma wannan shine yaron”.
Sosai maganar Abba ta sakasu jin shock su duka. Baffah dake saurarensu ya nemi jin ƙarin bayani. Dr Mahmud ne yay masa bayanin komai har yanzu firgici da al'ajabin kamannin little da AK na bayyane a fuskarsa.
Murmushi baffa yayi yana jinjina kansa. Sai dai komai baiceba yabarma zuciyarsa. Dan yama gama yarda AK na ɓoye masa wani abune game da yaron kenan, inba hakaba yaya akai hakan ta faru? Tunda a wannan zuwan basusan yazoba sai a shanun ƴan talla yaji. To lallai kam zaiyima tufƙar hanci, dan yama gama yanke hukunci saura zartarwa.
Baffah ne ya dakatar da wannan hasashen su Dr Mahmud suka shiga aikinsu. Duk wani gwaje-gwajen daya dace akan ƙwayoyin haluttar little da AK akai musu. Abinka da masu abu, ba'a wani zauna wasaba suka shiga ganin sun tantance komai dan Baffah yace bazasubar asibitinba sai da result.......
_________________________★
*DANYA*
A lokacin da gwajin ƙwayoyin halitta ke gudana acan Shira Hospital tsakanin AK da Little anan danya kuma baƙuncin Baba su Inna suka samu da farar safiya babu zato babu tsammani.
Duk suna zaune a tsakar gida ƴan barka na shigowa jefi-jefi da ƴan gulma. Karima na ɗaki kwance ita da ƴar jinjirarta tana kwasar kuka akan abinda ya barota da Kaduna, dan wahalar ciki tasa bata samu damar nazari akan komaiba sai yau da take jinta sakayau.
Tinene na kwance a ƙofar ɗakinsu wai ƙirjinta da kanta na ciwo, tun safe data tashi da abinda ta wayi gari kenan. Sai Sa'a daketa kaikawon yin aiki ita da Yaya Gajeje. Inna kuma na zaune kusa da Tinene tana gyaran gyaɗa da Yaya Gajeje tazo da ita gidan domin yin miya.
Sallamar mace da sukaji ya sakasu ɗan juyowa kusan su dukansu dan duk zatonsu ƴan barka ne ko cikin dangin Babawo dakan zo jefi-jefi, dan innarsa ma da tace zata dawo tun jiya har yau basuga ƙeyartaba. Sai dai ta aiko musu da kayan kunun da tace dana barka kuma kamar yanda uwar miji keyi a al'adar ƙauyen.
Ƙyaƙyƙyawar mace mai tarin kamala da ƙwarjini ta sake maimaita sallamar datai musu ganin duk sun zubo mata idanu basu amsaba. Yaya Gajeje ce tai ƙarfin halin amsawa da cewa, “Maraba, bismillah shigo baiwar ALLAH duk da dai bamu wayekiba”.
Murmushi matar tayi tana ɗan juyawa bayanta jin motsin takowar abokin tafiyar tata. Kafin ta samu damar bama Yaya Gajeje amsa Baba ya shigo shima da sallama a bakinsa. Duk da ƙyawun da yayi cikin ɗanyar shadda fara tas da ƙiba daya ƙara da haske hakan bai hana iyalan nasa shaida shi ba.
A take fara'ar fuskar Inna ta ɓace ɓat sai gabantane ke wani irin bugawa da sauri-sauri kamar zai buɗe. Cikin rawar murya tace, “Malam?!”.
“Na'am Asabe”. Ya amsa kansa tsaye yana kallon cikin ƙwayar idanunta.
Baya tai a tsorace zata zube dan ruɗani, a dai-dai sansa du Yaya Gajeje ke haɗa baki ita da Sa'a da Tinene data tashi zaune da ƙyar wajen kiran “Baba!”.
Nanma kai tsaye ya amsa musu da “Na'am ƴaƴana”.
Ai tuni Sa'a ta kwasa da wani irin gudu tayo kansa batare data saniba. Ta faɗa jikinsa tana fashewa da wani irin kuka maiban tausayi. Hannu biyu yasa wajen riƙe abarsa yana murmushi, ya miƙama Tinene hannu itama. Da sauri tayo kansa duk da halin ciwo da take a ciki itama ta shige jikinsa.
Hayaniyarsu tasa Karima fitowa itama. Ganin Babansu yasata kware baki cike da firgici ta kwala ihun daya jawo hankalin maƙwafta suka fara leƙe ta kantaga. Sai gashi cikin ƙanƙanin lokaci gida ya ɗauki harama. dan tuni ashe jama'ar gari sunga baba sanda yake shigowa garin tare da matarsa.
A take gida ya ɗauki murna, dan tuni dangin baba su Gwaggo Laritu harsun iso jin labarin dawowar ɗan uwansu. Sai koke-koke akeyi na farin ciki. Da ƙyar aka samu gidan yaɗan natsa aka kawoma Baba da baƙuwarsa ruwa. Babu musu suka amsa suka sha dan sunada buƙatarsa.
Baba Rabilu cikin kasa haƙuri yace, “Yaya gaka da baƙuwa kuma bamusan wacece ba?”.
Murmushi baba yayi yana mai kallon ƙyaƙyƙyawar matar, zuciyarsa fes da farincikin daya bayyana a saman fuskarsa yace, “Itama yayarku ce. Dan tazama ɗaya daga cikin zuri'armu tunda ta kasance Matata harma da tsohon ciki gashi nan”.
Cikin mamaki da nuna bayyanannen farin cikinsu suka shiga sake mata gaisuwar girmamawa. itako cike da fara'a da mutuntawa a garesu take amsawa. Babu wanda ya lura a cikinsu sai jin faɗuwar Inna sukai timmm a ƙasa. Dan hatta da Tinene sai da ta gaida matar da baba ya kira da matarsa. Karima ce kawai ta wani gwalalo idanu tana kallonta.
Kusan su duka kan Inna sukayi, banda Baba da ko motsi baiyiba sai dai ya kalli wajen. Ruwa Sa'a ta ɗebo da sauri ta kawo, Gwaggo Laritu dake riƙe da Inna ta amsa ta shafa mata a fuska. A take ta kawo numfashi tana binsu da kallo. idonta ta sauke akan baba da Amaryarsa. Babu zato sukaji ta fashe da kuka kawai ta fara sambatu
“Dan girman ALLAH na roƙeku ku taimakeni ku hwaɗa mani gaskiya, kuce dani mahwalki nake ba gaske baneba, na shiga uku ni Asabe. Yanzu malam irin sakayyar da zakaimin kenan akan wahalar ganin ka dawo gida da nakeyi tsahon shekaru? Yanzu malam duk hwaɗi tashin da nake akanka karasa da abinda zaka dawo gareni sai kishiya? Na shiga uku na lalace ni Asabe. Shikenan watan lalacewata ya tsaya kuma sai abinda ALLAH yayi. Ku dubetahwa jama'a kamar aljana. Wlhy tahi Hauwa kyau da ƙuruciya.....”
Ta ƙare maganar da ƙara jan wani nannauyan numfashi alamar ta sake suma.........
____________________________★
*_KANO_*
Bayan dogon zaman jira dasu AK sukasha sakamakon gwajin DNA ya fito daga likitocin guda uku, Batare da ko su Dr Mahmud sun dubaba aka mikama Baffah. Shima ɗin bai buɗeba ya sake miƙama Dr Mahmud dan yasan amintaccen AK ne. Kuma shina ya yarda dashi ɗari bisa ɗari.
Dr Mahmud da duk al'amarin yake neman rikita masa kai ya amsa ya buɗe takardun ɗaya bayan ɗaya zuciyarsa na wani irin harbawa da sauri-sauri. Sai da yayma takardun kallon kusan sakan biyar kafin ya ɗago ya ɗan dubi sashen da AK ke zaune rungume da Little dake barci yanzun. Cikin wani irin rawar murya da firgicin abinda ya gani ya maida kallonsa ga takardun yana magana da rawar harshe.
“Ba lallai ku fahinci duka bayanan cikin takardun ba saboda wani abun daga bincike likitocine kawai. sai dai ina mai sanar muku cewar zan faɗi gaskiyar abinda na gani kamar yanda baffa ya bukata tsakanina da ALLAH”. Ya ɗan sharce gumin daya taru masa a goshi da cigaba da faɗin, “B...Baffah sakamakon duka takardun ya nuna ya..ron... Na na na AK ne, dan duk ƙwayoyin halitarsa babu banbanci da yaron kamar yanda ya biyosa a kammani”. Ya ƙare zancen da tsananin raunin harshe dana zuciya.
Kusan a tare suma su Baffah zukatansu suka buga. AK dakejin kansa na neman tarwatsewa ya ƙanƙame little a jikinsa yana rumtse idanunsa da matuƙar ƙarfi, har takai yaron ya farka daga barci yana ƙoƙarin fara kuka saboda jin matsar da akai masa.
Yanda yayi ɗinne yay matuƙar tada hankalin Dr Mahmud da gaba ɗaya hankalinsa ke akansa. Da sauri ya miƙe zuwa garesa yana ambaton sunnsa. Hakanne ya fargar dasu Baffa ruɗani da ɗimuwar da suka shiga suma duk sukai kansa.
Da ƙyar suka iya ɓanɓare little daga jikinsa, Baffah da Abba suka riƙe AK ganin jikinsa na wani irin rawa maiban mamaki da tsoro, cikin ƙanƙanin lokaci kuma duk sai gaɓoɓinsa suka saki alamar ya suma.
Wannan shine tashin hankali wanda ba'a saka masa rana, dan kuwa dai Baffah ji yay tamkar ya fasa ihu dan tashin hankali goma da ashirin, yana matuƙar ƙaunar AK a ransa. Dan yana ɗaya daga cikin ɗa mafi soyuwa a garesa, sai dai yana dannewa ne gudun rarraba kan ƴaƴansa.
Da ƙyar suka iya ɗagasa zuwa gadon duba mara lafiya dake a office ɗin Dr Mahmud. Mmn Sadiq kam kuka take sosai dan gaba ɗaya ta gagara fahimtar wannan al'amari maiban ruɗani da al'ajabi........
*_BAYAN WASU AWOYI_*
Bayan wasu taƙaitattun awoyi aka samu nasarar farkawar AK da tun ɗazun ya farfaɗo daga sumar da yayi. A hankali ya buɗe rinannun idanunsa ya saukesu akan Baffah dake zaune riƙe da hannunsa. Sai Abba dake ta wajen ƙafafunsa shima a zaune. Mmn sadiq kam ta wuce gida tuni tare da little dan taje ta huta itama gudun kar taje ƙasa. Dan kallo ɗaya zakai mata ga gano tsananin tashin hankali da ruɗaninta.
Kallonsu yayi ya maida idanun ya lumshe a hankali yana wani irin murmushi da baida maraba da kukan ƙunar zuciya. Idanunsa a lumshe yace, “Baffah nasan ba lallai ku yarda daniba akan bansan yaya akai na samar da Abdul-Mutallab ba. Domin ni kaina na kasa yarda da kaina balle ku da zan faɗamawa. Sai dai ku sani lallai ina cikin *_MAKAUNIYAR ƘADDARA_* babu wani haske da zai haska min idanun ganinta kuma sai UBANGIJINA da haƙurin fahimtata da zakuyi na ɗan wanu lokaci dazanyi ƙoƙarin ganin bakin zaren, b.........”
Saurin katsesa Abba yay ta hanyar faɗin, “Ya isa Adnan. A yanzu halin da kake ciki baya buƙatar duk waɗanan maganganun. Dan Mahmud ya tabbatar mana da jininka yayi ƙololuwar hawa sama. idan kuma ka matsa da yawa za'a iya samun matsala. Mu dukanmu nan musulmai ne, muna kuma iya fahimtar yaran ƙaddara ko jarabawa, suk da dai ita wannan tazo mana a makance. Dan kai da Zinneerah ne ya kamata muji amsar tambayoyinmu a gareku, sai kuma gashi kuma neman amsoshin kukeyi a karan kanku. A ganina mafita ɗaya ce da shawara ta rage mana Alhaji”. Ya faɗa yana duban Baffah.
Kai tsaye Baffah yace, “Karka damu Alhaji Abubakar, kai maganarka kai tsaye dan kaima ubane mai cikakken iko akan su Adnan da wannan matsalar tasu da ni ta sakani a babban ɗakin duhu bama na makanta kawai ba”.
Murmushi Abba yayi, cikin son tausasa fushin Baffah da yake hangowa yace, “Nagode Alhaji Kabeer, abinda nakeson faɗa kai tsaye shine, mu koma ainahin ƙauyen Danya ko zamu samo bakin zaran inda matsalar take, dan a binciken da nayi wancan karan bazai gamsar damu ba saboda rashin samun mahaifin Zinneerah da nayi, sannan ƴan uwansa duk sunƙi bani haɗin kai akan wani dalilinsu da ban saniba. To amma sai nake dangantashi da fushi, sai dai ina fata da tsamanin insha ALLAHU zuwa yanzun sun huce. Maybe mu samu wani bakin zare da zaisa shima Adnan ya fahimci daga inda matsalar take ko zai tunano wani abu tunda dai babu wata hanyar samuwar ɗa sai da nasaba mai ƙarfi. Amma yaya kuka gani, dan yanzu ni wannan hasashena ne kawai”.
“Maganarka nakan hanya Alhaji Abubakar, kumani wlhy na gamsu da ita ɗari bisa ɗari”. Baffah ya faɗa yana miƙewa tsaye.
Zaune AK ya tashi da ƙyar, cikin son danne damuwarsa yace, “Uncle wannan shawaran naka yayi dai-dai, nima na gamsu da ita. Sai dai dan ALLAH ku gafarceni idan na ɓata ranku”.
Da sauri Abba ya girgiza kansa. “Ka kwantar da hankalinka Adnan kaji, ALLAH zai warware mana komai cikin sauƙi”.
Kai kawai AK ya ɗaga masa, dan yasan Baffah a ƙullace yake da shi. Duk yanda Dr Mahmud yaso riƙesa a asibitin yaƙi yarda, dole ya barsa suka tafi gida shi da Baffah Abba ma ya nufi nasa gidan. Bin bayansu Dr Mahmud yayi da drip da magunguna dan yasan AK na buƙatar hutawa na wasu awoyi ko hankalinsa zai dawo jikinsa.
Tunda suka taho ko sau ɗaya Baffah bai yarda sunyi maganaba. Shima bai iya cewa dashi komaiba saboda ciwon kai dake damunsa har yanzun.
Da suka shigo gidanma baffah cayay AK yaje shi yana buƙatar hutu. Ganin Dr Mahmud biye dasu yasa baiyi musu ba ya nufi sashen Hajiya iya shima. Acan Dr Mahmud ya samesa. duk yanda yaso ƙin yarda ya saka masa drip ɗin haka Dr Mahmud ya dage sai da ya saka masa tare da allurar barci mai ƙarfi. Aiko cikin amincin ALLAH sai gashi a ƙanƙanin lokaci barcin yay awan gaba dashi.............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
________________________
*Page 40*
...........Da farko Baffah yaso kira ya sanarma Hajiya iya komai, sai dai a bisa wani tunaninsa kuma sai yace bara ya bari har zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu da yake da burin yanke hukuncin daya dace ya kuma san Hajiya iya zataji daɗi sosai. Bai sanarma kowa mike faruwaba a cikin matan nasa, ya dai nema ƙanwarsa Bilkisu a waya sunyi magana, anan nema take sanar masa itama gobe idan ALLAH ya kaimu takeson sake zuwa london ɗin domin duba jikin hajiya iya, tanata neman wayar AK ma bata samuba ashe ya shigo 9ja ne. Tace amma tunda wannan ta taso bara ta dakata harsu dawo daga danya, dan dama tanason su tattauna akan ɓoyema Ahmad rashin lafiyar Hajiya iyan da sukayi.
Cike da so da ƙaunar ƴar uwarsa Baffah yace, “Babu damuwa Bilkisu, kiyi haƙuri na kashe wannan ƙurar duk da nasan tawuce kasuwar gobe, dan yanda Adnan ya dage cewar bai aikata wani abu akan samuwar yaron nanba hankalina na tashi, inaji a raina kuma kamar akwai wani abu ɓoyayye da bamu saniba”.
“Gaskiya kam Yaya al'amarin yana buƙatar bincike, baka shaidar ɗan yau amma koni dai inaji a raina Adnan bazai aikataba, to amma jin cewar gwajin DNA ya tabbatar da ɗan nasane yasaka jikina duk yayi sanyi gaskiya. Amma inaga zan shigo zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu nan ɗin kawai”.
“To ALLAH ya kaimu da rai, kizo ɗin kozanji sanyi a raina na samu abokin shawara nima”.
Daga haka sukai sallama. Idan barci ya figi baffa a wannan dare sai dai ɓarawo. Hakama mmn Sadiq acan barci ya gagareta. Danma Abba nata mata nasiha da lallashi harya samu taɗan saki jikinta saboda kar matan gidan su fahimci akwai matsala.
*WASHE GARI*.
Washe gari Alhmdllh AK ya tashi garau a zahiri. a cikin zuciyarsa kuwa shi kaɗai yasan mi yakeji gameda son tunano ko ya taɓa aikata wani abu makamancin wanda yake tuhumar kansa akan samuwar little. Sam bai iya tuna komaiba balle ya gano, dan haka ya ajiye komai a ransa yay shiri kamar yanda baffa yace.
Yayi ƙyau matuƙa cikin ɗanyar shadda fara tas da taji ɗinki mai ƙyatarwa da ɗaukar hankalin mai kallo, ya murza hula a kansa wadda ta sake ƙawata tsarin adon nasa da bayyanarsa cikakken bahaushe. Turare ya saka ya fito yana baza ƙamshinsa mai sanyi da daɗin shaƙa. Yayi mamakin cin karo da matasan ƙannensa suma cikin shiri, sai dai baice komaiba ya shiga amsa gaisuwar da suke masa cikin girmamawa.
Baffa ne ƙarshen fitowa sanye shima cikin tashi ɗanyar shaddar, fuskarsa a sake tamkar babu damuwar komai tattare da shi, har hakanma ya bama AK mamaki da tsoro, dan tun yana yaronsa ya gama karantar irin wannan yanayin na Baffa. Idan kai masa laifi ya nuna kamar bai damuba to lallai akwai abinda yake shirya maka kuwa.
Motoci suka shiga, Baffa shi kaɗai sai drivern sa, dan acewarsa zasu ɗauki Alhaji Mansur babban amininsa a gidansa. Sai yazam su Moos'ab sun taru a mota ɗaya su huɗu. AK na shirin shiga wata motar shi kaɗai sai ga Dr Mahmud ya iso. Hakan yasa ya shiga motar Dr Mahmud ɗin kawai da shima dai da alamar shirin tafiyar yazo gidan dama.
Duk da AK cike yake da mamakin wannan gayya sai baice komaiba. Sun dai gaisa da Dr Mahmud ya tambayi yaya ƙarfin jikinsa daga haka