Showing 87001 words to 90000 words out of 144533 words
amma wanan cikin nata yazama dole azubar a sallame ta."
Yace "bazan iya zubar waba."
Ido hadim ta zuba masa ta san halin Nabil baya taba cewa no yace yes, bazai yiba tunda yaki.
"To yanzu me mafita nima baza azubar da nawaba."
Yace"na sani Halima idan na nace azubar ban miki adalci ba, amma wllh bazan iya yarda a zubar da na Fatima ba."
"Aishine nace maka me mafita?
"yace kibari mudawo daga tafiyan nan kafin nan nasan zamu sanu mafita. "
Numfasawa tayi tace
"Tomorrow ne ko?
Yace" yes
Gyada kai Hadim tayi dan ta riga ta aiyana kudurin ta aran ta wanda kafin yadawo two weeks tagama abinta dan shi taga bazai iya ba kuma ta san ba komai bane illa tsabar tausayi irin nasa dan haka batasa wani Nabil zai sowani Fandau aransa ba tasan de yana da tausayi.
"haba Fatima sati 2 kawai zanyi nema inajin yanda zanyi missing naki datun da muka hadu bamu taba rabuwa na sati ba sai awanan karon dan haka kikula da cikin ki da kanki kuma ai ga waya zamu dinga fira idan na samu lokaci kinji my Fajjjiiii ta.'' Share hawayen ta tayi tace" ALLAH yakai ka lfy yadawo da kai lafiya cikin nasara da ribar tafiya yakara maka daukaka da karfin mulkin sa."
bai san sanda yasake rungumo taba yana cewa "Ameen nagode my Mata."
Yakalli agogon dayake daure ahannu sa ya mike dasauri yana rike da hannun ta har falon karshe
Har yabude bakin sa zayin magana waya yafara ringing yana daga mata hannu ya fice ita kuma ta juya cikin tana juya kalaman sa kobai ce yana sonta ba amma ai ya gaya mata kalamai masu dadi wani kalma da yake yawan gaya mata ne ya fadomata *so abaki ba sobane son gaskiya a aikace ake ganeshi* murmushi tayi ta fada gado.
Hadim kam duk ta zube sabo da bakaramin azaba cikin yake bata ba da yace zai tafi ko kanta bata daga ba balle rakiya ya dauki Ma'aruf da Bilal yakama hannun Fujjirat suka fito driver yaja suka tafi har club dinsu haka akayin ta rubibin daukan yaran nan ana cilli dasu bare Fuj har oga ita ya d'auka, aida zasu tafi yameka wa Security's dinshi su dakyar Fuj tayar da sai kira take "my ci" wai zata ce my Star yanda Hadim take kiran sa yana gani aka dannata a mota yajuya kansa bayajin akwai wani abinda yakeso fiye da son yarinyar nan yanzu idan yatafi yabar ta haka zatayin ta bulayin awajen yan aiki bawani kula Hadim yanzu take dasuba dan ta kanta take, tuno da kukan ta har cikin dodon kunnen sa yasa yayin saurin zaro wayan sa yakira su yace sudawo masa da Fujjirat haka yatafi da ita abinsa abokan sa suna masa dariya na cewa sun samu karin yar autan club
Nabil yace" ba kuyi karya ba, yanda idan kunci wasa ake dauka kofi abaku, ita ma an bata" dariya suka sakeyi.
Sun tafi da kwana 2 tukun ya kira Fandan da safe, tana dauka yace"Mata kinga ban kiraki bako wllh ban samu nusuwa ba gashi da Fujjirat nazo kan kara akeyi sosai akasan sanyin ya zuba mata zazzabi amma yanzu da sauki,
Yakike ya MAMA Aisa kina kulamin da ita ko?
Murmushi tayi tace" Mama kuma?
"Eh mana bakisan da me sunan ta kike tare ba."
"ALLAH da naji dadi amma yajikin Fuj din? dama da ita katafi?
"dasauki eh muna tare."
"Kuma idan zaka shiga wasa ya kakeyi da ita?
"akwai abokai nada sukazo ta matan su awajen su nake barinta."
"To wane kasane har ake yayyafin kan kara haka?
"yace Rasha ne."
Sunyi fira sosai kafin yace" bari nakira Aunty ki zumudin jin muryar ki ya hana nafara kiranta."
Kafin tayi magana harya kashe wayan.
Ba ajima ba Hadim da wata suka shigo matar farace Hadim tanuna ta tace "gatanan matar tabi Fandau da kallo ita cikin gurbattacen hausanta tace"sannu ko za a miki allura ne".
Dasauri Fandau ta mike tana karanto Innalillahi afili cikin tsoro tace "wane irin allura?
Hadim tace "kinason sani kenan ai da kinbari an miki dan na taimakon kine kar kije gida ace kinje yawon karuwan ci shiya sa nasa amiki allura da zaisa ki manta komai akuma miki wada cikin zai zube dan wataran kar dan yace kinemo masa uban sa kinga kekuma bakya cikin haiyacin ki yazakiyi dashi ai gwara azubar."
Ido wajen Fandau take kallo su, ganin mata ta bude jaka tazaro allura da gudu Fandau tayi hanyan kitchen wuka ta dauko tace"wllh sai de ayita koni koku tana kuka tana zaginsu a haka aka kira wayan Hadim tana dubawa Nabil ne tayin saurin fita dan karyaji abinda ake tana fita doctor adegas ta karaso wajen Fandau tace ina hada ido dake naji tausayin ki meya kai ki beyewa mazan turawa daga kawo ki aiki suka baki ciki gashi yanzu kinsa uwar dakin ki tarasa yanda zatayi saide aminki allura."
Fandau tace" haka tace miki ni yar aiki ce?
Doctor tace "eh mana."
Fandau tace "bata gaya miki gaskiya ba."
Matar tace "daga yanayin kalaman ta tunfar ko nagane ba gaskiya bane dan Hadim kawata ce nasan halinta sarai gayamin gaskiya zan temaka miki."
Aguguje Fandau tabawa matar labarin ta.
Doctor tace "na gaskata ki kuma ciki tunna fari nagane cikin kawata ba na gaskiya bane amma kisani mijin ta yanada mugun kudi har ita kanta baza ki iya ja dasu ba temakon da zan miki dayane alluran batar da memory kine bazan miki ba amma na zubar da ciki yazama dole tunda zata gani idan bai zube ba dan tafiyanki sai gobe, inason kinuna na miki alluran kinuna kin manta komai idan kika je gida kikaga za'a iya dau miki mataki shikenan kinji kuma abin d...
Hadim ce tashigo "tana cewa tayar ko sai taji ciwo kafinnan
Doctor tace "ai har angama dayan saura na aborton din ai."
Hadim murmushi tayi tace"yanzu shikenan ta manta komai ko?
Doc tace" sosai."
Fandau tana gani matar ta dan na mata allura da zai zubar mata ciki takama ta ta zaunar ta ita abakin gagon tace "nan da anjima zakiga tafara zubarwa."
Hadim tace "nagode Hadim tana ganin wayan Fandau ta dauki wayan suka fita.
Suna fita Fandau ta fashe da wani irin kuka yanzu burina da kudiri na bazai cika ba kenan yanzu naje gida nace me, anya bazan kira matar nan nace tamin alluran nan ba kuwa? tana ciki haka taji cikin ta yayi wani irin murdawa juyi ta dingayi akan gadon tana ihu dan yafi nakuda ciwo tana jin abu yafara bin jikin ta har yasauko cinyar ta tasa hannun ta shafo tana ganin jinine tasake sakin wani kukan saide bawani jimawa taga jinin ya tsaya haka cikin ma ya dena ciwo.
sai yamma Hadim ta shigo, tasamu Fandau akwance jinin har yafara bushiwa anan Hadim ta sake tabbatar wa da lalle bata cikin hayyacen ta dan da tana cikin hayyacen ta zata tashi.
Tace" kinga anyi maganin ki yara sun zama nawa na har abada kije can uwar ki taci gaba da renon ki".
Dole ita ta gyara ta, Ita kuma Fandau sai juya ido take alamun bata san ma me akeba, da Hadim ta doka mata tsawa tace "kina jina kitashi." Bata ko motsaba tana kallon Hadim a shagwabe kamar yarinya janta Hadim tayi tafiyan ma dakyar takeyi haka ta kaita bathroom ta kitsata suka fito tana rike da hannun ta ta zaunar da ita akan kujera ta janza zanin gadon
Har zata fita ta tuno da ai yaka mata ace ta bata abinci waya tayi wa ma aikatan gidan suka kawo abinci ba ajimaba taje ta karbo tazo ta ajiye abincin ko kallon abincin batayi ba, irin bata sani ba saida Hadim ta zauna ta samata abaki nan ma kin taunawa tayi saida Hadim tasa abakin ta tafara taunawa sannan itama ta fara ahaka ta gama bata.
ALLAH sarki Hadim duk abin da takeyi cikin karfin hali takeyi dan tana jin jikinta sosai.
Washe garin Hadim da dama tagama duk wani ciku cikun tafiyan Fandau haka ta dauke ta da kanta dan bata son driver yasani wani tasamu a maikatan airport tace ya hadata dawani fasinja zata bashi amana haka akayin kuwa aka hadata dawani yaro bawani babba bane tace "bawan ALLAH yasunan ka yace" musa." tace" idan badamuwa zan baka amana." yace"Allah yabani ikon karba da kuma rikewa" tanuna Fandau tace "kaga wancen yarinya bata da lfy kuma ni nasame ta tunda guntun lafiyan ta tace min ita yar maiduguri ce amma yanzu idan an tambaye ta ma bata bada amsa, nayi mana shirin tafiya tare maigida na yakamu darashin lfy shine nawa tafiyan bai yuwuba, nace sune mamin wanda zaije Nigeria musulmi shene
Aka hadani dakai, kai dan inane?
yace " ni dan kano ne karatune yakawo ni yanzu ma hutu zan tafi."
"Yawwa kanina inaso ka kai min ita maiduguri nauyin da zan daura maka kenan zan baka kudin jirgin da zai kai ka can dakuma wanda zaka dawo harma da kari."
Yaron yace"amma wllh badan kin riga kin hadani da ALLAH ba da bazan karbi wannan aikin ba tunda kema kince baki san gidan su ba to yanzu ina zan kaita?
Hadim tace " wanan badamuwa bane ka kaita B R TV ko N T A maiduguri kace katsince tane amma kace a garin ka tsinceta." Dayake yarone bai wani san haka zai zame masa illah ba yayi saurin karba , Hadim ta bashi kudi meyawa tayi saurin barin airport din.
Yaron bai wani kai saurayi bama shiya kama hannun Fandau har cikin jirgin
Itako Fandau tana shiga tana zama tafara kuka, ba wajen zaman su daya bane da wanda aka hadasu tunda ta zauna kuka take yanzu haka zan koma gida nazo a siya zan koma awulakan ce to ina shi Nabil din kikasani ko bakin su daya da matarsa yasan metayi koma dama bawani tafiya dayayi tunda ta zauna wata mata yar gayu take binta da kallo itako Fandau ba alamun zatayin shiru, matar tasowa tayi tazo wajen ta, kanwata meyake damun ki haka tunda aka fara tafiyan nan sai kuka kike ko da akazo tambayan mezaki ce bakice komai ba kuma naga da yayanki ma kuka shigo ko kanin kine ."
Fandau batasan dalili ba kawai sai jitayi tace"ba yaya na bane banma sanshi ba kawai gani nayi yakama hannun mun shigo ."
"to meya saki kukan nan meke damunki ki gayamin?
Tace" gaya miki ba wani amfani dan idan kikaji tarihin rayuwa ta bazaki yarda ba, a bune da banta bajin sa aduniya ba."
"Kigaya min ko dawani taimakon da zanmiki", saida Fandau taci kukanta ta more tukun ta kwashi komai na rayuwan ta tagayawa matar, a firjice matar take jinta itako Fandau tunda tafara bata tsaya ba sai da taje karshin labarin ta.
Itama matar kuka take sosai, ko magana kasayi tayi tashi tayi tajen wajen ta, ganin kukan Habiba yayi yawa doctor Muktar yace" waike meya faru meke damun yariyar naga kin dade awajen ta Habiba ta kwasa shi komai ta fadawa doctor shikan sa abin ya firgita shi haka Habiba ta koma wajen Fandau ta yita lallashin ta har tadan saki jikin ta.
Hadim fal murna takoma gida. Dan ita abinda yake bata mamaki ba Nabil ba hatta yan gidan su da kawayen ta ba suwani nuna mata dokin cikin nan ba, ummin Nabil har yanzu bata kirata ba haka Inna ma mamar ta cema takira ta hatta kanwar ta Ashuwa bata kirata ba.
Ga babbar aminiyar ta ma Habiba data kirata cewa tayi baza ta samu daman zuwaba dan tana cikin shirin tafiya gida.
Kowa bayawani dokin cikin nan.
Jirgi su yana sauka atare suka fito da Fandau sun riga saurayin fitowa koya tsaya neman Fandau ne wayasan masa itade dama tun kafin susauka Habiba tace mata gidan mu zaki bimu dan mutantan ce gaskiya acikin maganan ki, sude har driver dinsu yaja basu ga idon Musa ba.
Sun sauka ne a ABUJA dan haka gidan doc na nan ABUJA suka yada zango suna shiga babban parlour gidan idon Fandau yasoma cin karo da tabkeken photon Nabil da yake jikin bango yana sanye da kayan ball yarike ball din ahannu sa turus ta tsaya tana nunu photon bakin ta yana rawa tafara magana "wllh gashinan shine shine shine".
"shine wa suka hada baki Muktar da Habiba."
"Shine wanda nake gaya muku sunan sa Muhammad ana kiransa Nabil ko Shiddams wllh shine."
Sai tasake yi musu bayani sosai suka yarda, abin yayi mugun bawa Habiba mamaki dan bata zaci kawar ta da wanan halin ba
"Abban Nofal me mafita."
"Mafita daya kawai mukaita gaban iyayen ta dan nasan bazasu iya jada suba, amma nima sheda ne alokacin cikin farko a toilet din office dina nace ta shiga tayi fitsari, saide mamaki na dana shiga sai naci karo da wani kwalba shima dana sa aka auna sai yanuna iran fisarin Hadim ne kinga yanuna da abinta tazo ko kuma ba abinda banyi dasu ba suzo awu suka ki, ga haifuwan gida suke dama abin yana bani mamaki amma awanan cikin sai suka yarda aka auna kuma bugu da kari ma ita Hadim awajen haka tace ashe itama darabon zata ga......
bai bari ta karasa ba."
Amma wanan bai isa sheda ba dan haka hakuri shiya dace dake mude zamu danka ki ga iyayen ki danni maiduguri ba bakona bane kusan ma garin mune anan aka haife ni kuma garin mama ta.
Inane anguwan ku?
Fandau tace " gargar doctor yace"ok anguwan Zannah Modu kenan Babana."
Da sauri Fandau ta kalle shi tace " nima shine Babana ai."
Da suari doc da Habiba suka kalle ta "Baban ki?
Habiba tace "haba sai yanzu na tuno inda nasan ta wllh itace wanan yariyar da nake gaya maka agidan Malam me girman kai kazama dinnan wllh tun agirgi nake mata kallo kamar na taba ganin me kaman ta Wllh itace."
Fandau daga idon tayi sosai ta zuba musu ido tabbas shine dan gidan Malam Dauda abokin Baban ta wanda idan yaje yan gidan su aketa turoruwan shiga bangaren bak'i gaishe shi shine take kiran matar sa me girman kai ashe ita ma kallon me girman kan suke mata.
Muktar yace "ke yar gidan Wacece acikin matan gidan." "Aisa
Rai abace doc yasake kallon ta yace "amma ba kanki kadai ba hatta Malam baki masa adalci ba shi me fada aji agari kuma duk abinda yasameki kije alhakin Baba Aisa ne dan ubanki kinsan Malam Dauda?
Tsawan yadaka mata yasa ta ja da baya tana gyada kai alaman eh
"kinsan ke me sunan wacece acikin matan sa?
tace " Inna Falta?
Yace"to ni Inna Falta ita ta haife ni, yanzu in ban da lalacewa irin na duniyar yanzu kamar ke da darajan ki da kimanki kibi na miji, gwara da suka miki haka kuma bawani gida da zan maidaki na kaiwa ubana wanan kayan bakin cikin, duk da Shiddams nada daman sani bazan kai ki ba sai kin koyi hankali da zaman duniya, wawuya sakarya ni ahannun na zaki dandani azaban da yawuce na gidan Shid ai."
"Haba dear kamata ahankali man da wanne zataji."
Doctor yace"Wanan yar iskan za'abi a sannu, ko ke bance kibita a sannu ba", yana gama fadan haka ya haura sama
Habiba tace "ishiru Mamana, dama Abban Nofol haka yake yanada zafi akan kannen sa, kiyi hakuri nasan kema kina da lefin yarda da namiji, shiddams abokin sane sosai nasan za'a shawo kan abin kafin akai ga manya, saide ina tsoron kishin Hadim nayi mamakin jin da kanta take kai miki Shddams na yarda lalle akan buri ba abinda bawa bazai yiba,
ga daki nan kushiga keda su Ummulkkairi ina zuwa."
itama ta haye saman
Nabil yayi yayi yarasa Fandau a waya yagaji ranan da gobe zasu dawo yakasa hakuri ya tambayi Hadim saicewa tayi tana nan nima ta kaina nake.
A ranan da Nabil ya sauka ita kuma Hadim har ranan akwance take jiki sai abinda ya karuma ciwo, sai dare Nabil ya lalla ba yayi bangaren Fandau ba inda bai duba ba bai ganta ba cikin faduwan gaba yafita
"Halima ina wannan yarinyar?
Cikin rashin damuwa Hadim tace "wace yarinya kuma?
"Fandau mana."
"au dana sunan ta kenan kai da karike sunan ma bakada aikin shine, to ma meya kaika part din nata ma, ya mukayi dakai."
"Halima amsa zaki ban tana ina?
Tana maiduguri, na kasa hakuri na turata dan idan na biyewa tausayi irin naka wankin hula zai iya kaimu dare na tura ta anan ta masa bayanin komai.
"Dan me zaki yanke hukunci bada sani naba."
Tace "dan baka da iko akai ne, ni na aurota kuma dan na sallame ta ban......
Ai Nabil yama manta dawani ciki ajikin ta wani irin shaka yamata wanda saida yaga alamun zata rasa numfashin ta yanda idannu ta suka fito.
Sakinta yayi ahankali yace" Halima dan ALLAH karki dauki al'amura na da wasa, wllh zuciya ta zata fashe da gaske kin zubar da cikin Fatima da gaske kinsa amma ta alluran idan ta ganni baza ta gane nima gayamin gsky kin illata min Fati na."
Hadim hannun ta awuyan ta tace "eh eh na aika ta."
"Hadim meyasa kika min haka inda kinsan halin da gangan jikina da zuciya ta suka shiga akan yarinyan nan da koda kudi aka hadaki bazaki min hakaba meyasa meyasa?
"Shid saboda nina samu na aura maka ita saboda wani bukata tamu kuma mun samu biyan mukatan zaman me zatayi mana a gida, yanzu wannan har yakai kayi yun kurin kasheni."
Nabil cikin wani irin karajin da ya firgita ba Hadim ba har su Fujjirat
Yace "ai yun kurin kashe ki kadan ne har uwar ki da kuman ki sai sunyi nadaman haifuwan ki idan baki ne momin mata ta cikin kwanaki ukku ba kuma da lafiya ta dan duk inda lfy yake sai kin nemo, zakuyi nadama."
"Nabil ne kake gayawa haka, uwata bata ci darajan ita Yaya ce awajen ta ka uwar taci darajan daukana da tayi tabaka aure bana."
"Aure fa kikace a tsakani na dake yanzu bawani aure naba ki kwanan 3 kine momin mata ta bawani aure a tsakanin mu balle naga darajan sa".
Hadim dafe kirjin ta