Showing 114001 words to 117000 words out of 144533 words
zasu yi gado da makara aranan ga Fatima naga uban daya isa ya daura auren ta ina raye. Yasake kifa kansa yafara rusa kuka kamar yaru ba necewa shine Shiddams mutumin yafi SHEHU da gomna acikin garin meduguri adon mutane
Baban bai ceko maiba azagin da Nabil yayi dan yasan halin d'an nasa idan ransa yabaki zai iya bude baki yazageshi ma
Malam yayi Gyaran murya zai cewani abu Baba ya tashi yakara sa inda yake cikin kunne sa yarada masa wani abuda duk bacin randa Malam yake ciki saida yamurmusa
Daganan Malam yarufe da adua ya sallama kowa Akkam yanawajen Ummi har zasu fita
Malam Dauda yace" ina mesunsn nawa ita ko Fandau kuka take sosai Habiba tayi bangaren Mama da ita su BaGaji ansamu abin fada sai kira suke duniya abin tsoro abin magana irin wanan agidan Malam mama de shigewa tayi bata kulasu ba Hadim kam dama batazo ba
Baban Nabil shima bangaren Mama yashiga Fandau yaja gefe sunjima sannan yafito yatafi Fandau ta rungume Mama sai kuka suke har dare matan gidan suna shiga suna fita har zance yafara yaduwa gari itako Fandau burinta taga Bagana dayaran ta kawai
Shiko Nabil kinfita yayi agidan yasa Zannah agaba yana kuka har 10 dare shima Malam dannewa kawai yake amma jiyake kamar yayi kukan dan bai san hanyar da zaiyin ya gyara kuskure karyar da yayi ba dan bai zaci abin zai zoda hakaba amma ya danne nasa yake lellashin Nabil amma ina kamar kara masa suke sai zaje zaje yake ganin idan ya matsa shidin ma Nabil gaya masa magana zayi yasa Malam yafita wajen Abokin sa akaramin parlour sunfita sun barshi
Sai wajen 11 Malam yashigo ganin baiga tafiyan Nabil ba yace "Nabil yau kenan agidannan za ka kwanan?
"Eh wllh namai da matata sakin umarni nayi kuma na mayar zanga wanda ya isa yazo yafitamin da mata tunda na mayar ta Malam ka tekamin kar na rasata.
" a a Nabil wanan rigimane tsakanin kada mahaifin ka kana gani yahanani magana yace nabashi DAMAR sa amatsayin sana ma mahaifinka kaga dolo nabashi damar ko yanzu haka ma maganan daurin aure yake agobe karfe 8 nasafe Nabil tayi yayi yafada jikin Malam yanawani irin fitar da nunfashi saida Malam ya tsorata yace kaga tashi tashi kashiga ciki kasame ta idan tace kai tafiso akan BilAL sai insan yanda zanyi injuya abin bana son kasake danuwa irinna wancen lokacin kasha wahala kaji.
Nabil yace" tana ina?
"Tana wajen uwarta.
Nabil yameke da sauri zaifita.
Malam yace "ina zuwa kuma?
"Malam wajenta.
Dariya yabawa Malam yace"amma saida safe ko?
Aiko waigen Malam baiyi ba yafice
Mama kam yau ba bacci ita da Fandau fira kawai ake ayi kuka ayi dariya tayi mutukar mamakin yanda Nabil yake kula da Mama suna cikin haka sukaji anata dukan kofan falo da karfi kamar za aballe duk suka sorata itada Fandau saida ta zo kofan Mama tace "waye?
Yace "Mama kibude nine.
Mama tace "lafiya Nabil yace" kibude.
Mama takalli Fandau alaman ta shiga ciki tunkafin ta karasa fudewa ya fado ciki yayi falon yazube agaman mama yana kuka yana mata magiya yagaya mata yanda sukayi da malam
Mama tace"tunda yabaka dama ka shiga tana ciki.
Da sauri yayi hanyar dakin da akace Fandau take
Amma me yana shiga yatsaya jin wani irin dariya Fandau takeyi awaya
Haba my BilAL kasan fa aurenmu na gaggawa ne
Amma nide nafison koda bayan daurin aurene ayi dan events wanda zai nuna munyi auren SO dakuma yanci
Nima na dandani irin abin da yan gatan amare sukeji
dariya ta sake fashewa dashi
tace kamar ya gobe iyanzu muna manne kana nufin daga an daura aure zaka rabani da
Mamata kenan nima zanso ace gobe iyanzu muna manne.........
Wani irin mari taji yasauka afuskan ta wanda saida ganin ta yadauke na wucen gadi duk da tasan yana wajen bata zata zai tabata ba aiko bol yadingayi da kita mama da take falo taji marin da gudu ta shigo taga Nabil yana ball da Fandau wanda gaba daya hankalin sa baya jikin sa tako ina dukan ta yake Mama kasa kwatar ta tayi gashi da zafi safi yake dukanta aiko da gudu Mama tayi wajen ganin yana neman hallaka mata yar tafita tana kururuwa neman
akawo agaji
Shiko Nabil tunkarfin sa yake makarta yana surutai
"aiko gawar ki bai isa yagani ba zan kashiki in yaso nima akashine kin huta.....
*Tofa shikenan kurunkus Nabil kafutar dani*
*B JATTKO*
[3/12, 8:50 AM] Hauwa: DAMATA
NA
BATUL ADAM JATTKO
🌈Kainuwa writers Asso🤝🏻
45
*M*atan gidan kowa da yaran su sunfito jin yan da Mama take niman temako ta san su mata ba abinda suka isa dan haka bata tsaya cemusu komai ba ta wuce part din Malam tana shiga yana sama dan haka tadinga zan bada masa kira
"Sayinnan kafito zai kasheta."
yana karatu a parlourn sama yaji kiran Mama da abinda take cewa ai da sauri ya fito yana tambayan ta
Tana gaya masa ya fara taka stareas da sauri
Yayi ban garen Mama har yanzu Nabil dukan yakeyi duk ta gala baita
"kaiiiii wani tsawo Malam ya doka masa
Yana ganin Malam yabar dukan yayi wajen Malam din dafe da kirji yana wani layi kamar dan ganye amma sai ya kasa karasa wa inda Malam yake dan jiri yana iban sa kuma duhu yake kani
Lun ya zube awajen
Dasauri Malam ya karasa inda yake yana kiran sunan sa ya dagashi ya daura kansa acinyar sa
Nabil ya kama hannun Malam ya fara magana cikin tsarkewar murya yace "Malam Fandau ta yarda da auren BilAL taci amana na bata sona na rasata na....
Bai karasa ba yanemi nunfashin sa ya rasa jijiga shi Malam yafara
Bagaji tace "lah meta masa Malam yasuma fa ko?
Jin wannan yasa mama ta saki Fandau tayi inda Nabil yake
Ita ma Fandau afir gice ta juyo aiko da gasken taga Nabil ba alaman numfashi Mama ce tayi yunkurin tauko ruwa a fridge ita ko Fandau tana ganin haka ta meke duk da kafanta yana mata wani irin zugi amma sai da ta meke da gudu ta karasa inda Nabil yake acinyan Malam hannun sa ta daga sai taga ya koma kamar ba rai wani kara ta kwalla daidai ta zuba masa ruwanda Mama tayi hakan yayi daidai da farfa dowan sa amma bai bude idon jin yanda Fandau take kuka
Dan ALLAH ka tashi Abu Fuji wasa nake maka wllh ne ban taba waya da BilAL ba bansan shiba sai dazunnan
Baban kane yace....
Dasauri Malam ya doka mata tsawa Kiyiwa mutane shiru yadubi Ba Alta yace daukomin wayata
Fandau ta koma gefe itama goshita akumbure gashi ko ina ciwo yake mata musamman hannun ta da take jin kamar ya targa d'ata
Mama tace" kai Sayinna dama mesunan ka yananan da wanan bakar zuciyar tasa wai meyasa duk masu sunanka suke hakane nekam Shateema da yaban shawara ban bari yasa maka mesuna ba dan shima Tajudin da gani irin halin masu sunanka yayi.
Shiko Malam yana kallon Nabil yasan ya farfado
Itako Fandau sai kuka take amma bana ciwon da take jiba
Ahaka
Ba Alta ta kawo wayan ta durkusa tameka masa
Kiran sojojin da suke tsaron kofan sa yayi dan lokacin doka yayi dole sai su zasu kai shi hospital
Su hudu ne suka shigo suka dauki Nabil zasu fita dashi itama Fandau ta meke zata bisu cikin tsawa Malam yace "ina zaki kuma tace" zan bisu yace"zauba." bude ido Nabil yayi cikin da shewar murya yace "kusaukeni a hankali suka sauke shi amma yana dubawa yaga duk matan Malam suna d'kin shiko arayuwan sa basu masa ba sam kuma bazai iyace komai agaban suba yadaga ya Kalli Malam yace "Malam inason ganinku kaida Mama
Malam ya Kalli matan da sojojin tunkafin yayi magana sojojin suka fice suma matan suna zunbure zun buren baki suka fita dan de basu isa su furta wani abu agaban Malam bane
Nabil ya Kalli Mama yace "Mama dan ALLAH kiyi Hakuri nasan ban kyuta ba na shigo har d'akin ki na dakar miki yarinya bayan banwake lefina nada ba na daura wani nikai na tsani hallina dan nasan zai iya sawa ha hanani
( *Hasken rayuwa ta Aisha sada* ,)
Amma Mama nasan Fandau bata san irin sonda nake mata bane bata san yanda na mutu akanta bane da ko na mutu ba zatayi sha awan cewa za ta auri wani ba yanzu lefin da nayi wa Fandau har yakai ta shukun tani da haka ina raye agabana take waya dawani kigaya mata inhar nine mijinta to ta kiyaye abin da zai tuzurani haka wllh wataran saide akwashi gawata
Tashi yayi ahankali yakara sa inda take ya zube guwoyinsa yakamo hannun ta yace "Fatina meyasa kika gujeni meyasa tun a chatting da mukeyi baki baiya namin ganki ba shiya sa kike cewa kina gujemin nadama duk sanda nagane kewacece baki san rashinki barazana ne na rasa rayuwa ta agareni ba
Kiyi magana mana ya matsa hannunta wada yake mata ciwonne kuwa wani kara ta kwallah cikin
Dama Malam da Mama sun fice tunda dama bakinta ne duk basu ga fitan suba
"me yasa kika boyemin kanki Fatina?
Zubura baki tayi ta janye hannun ta cikin tasa nata ta daura hannnun cikin tafin hannun ta dayan tafara juya kai
"Ayyya mata nine ko ya sake jawo hannun ta fizge har hannun ya kumbura yazubawa hannun ido yana gani yasan tar gadene kunsan dan ball baiwani dauki targade abakin komai ba dan she tunyana yaro ya iya gyaran targade idan yayi da kansa yake gyara kayansa ko idan acinkin abokan sa wani yayi yana gyarawa
Fakon idon ta yayi yaja hannun nata k'ara tasa jawota yayi jikinsa cikin dabara ya hadeta sosai da jikin sa yanda zata saki jikinta yana mata wani wasanni har ya fara gyara mata hannun ita ko Fandau jinta aduniyar da tajima tana nema yasa tayi lamo saida taji zafinyayi zafi ta fara jan hannunta tana kuka da yaga kukan nata zaiyi karfi kawai saiya hade bakinsu waje daya amma yana jan hannun wani kara tasa alokacin da yatsan ya fada ya gyaru kenan sake hade bakinsu yayi yanawani irin fitar da nunfashi itama haka sai da yayi facale da kayan jikinta da dafi zafi yake aika mata sakonne yazame mata tamkar wani mayunwacin zaki saida taga yakusa isa babban fada duk da itama ba abinda take so irin abin amma ta daure tameke da karfi ta fusge ta tunkuda shi tameke
Daga kansa yayi yana kallon ta idonsa yayi jajir cikin wani irin muryan da yake janyoshi cancikin makogoro yace "me haka Fatina?
itako sai kare jikinta take tana jada baya da rarafe ya karasa inda take zai kamota ta matsa
"yace mehaka?
"kai kai zan tambaya mehaka zakazo har cikin dakin uwata kanemi kayi lalata dani bayan kasakeni kaban dinbin jama a
"Mata na mayar da kefa wllh karkimin haka kar.
" karka renamin hankali mana kana nufin Fandau din dane daka yaudara ka aura
a gaban din bin mutane ubanda ya haifeka yace bani da iddan ka tun dana haifu bamu haduba dan haka bawani maidani da kayi.
"kiyarda indaura miki iddan yanzu wllh dole su hakura subarmu."
"Lalle Nabil duk dama nagane jikina kake so fiye da komai wllh banzaci abin har yakai haka ba karasa inda zaka nemi jikina sai dakin uwata."
"wllh bakiyi karya ba inason jikinki kuma ko aina zan iya neman sa tunda ina son komai naki inaso.
Cikin karaji tace "dama nasan jikina kakeso ai duk sanda jikina yadena baka sha awa zaka dena yayina ne kawai nikuma yanzu kadena moran jikina dan......
Cikin muryar tausayi yace" karki min haka wllh bazan iya daukan wannan horan ba idan baki amince dani ba wllh nakai gejin komai zai iya faruwa dani yana maganan yana dafa maransa
Tana ganin gasansa jitashi gaban ta yayi mugun faduwa da sauri ta dauki riganta ta sa shiko yanda ta sunkuya ta dauki rigan ne idon sa akan dukkan halitun jikinta da yafi so maranshi yasake dafewa maransa da yakeji kamar zai kashi shi ya kwata yana birgima dafe da maran "yanzu mata bazaki ji tausayi naba itako tama gasa juyowa dan ita tsoron sama takeji
Ayanda yake
Karasa wa tayi gaban gadon ta dauki Akkaram da yake bacci ta tayi hanyan waje saida take bakin k'ofan fita tajuyo ta kalle shi yana nan inda yake yana ta juyi
Tace "shikenan tunda bazaka fita mana ad'aki ba nina bar maka.
"dan Allah karki fita wllh zan iya shiga kowane irin hali idan na rasaki.
Kiduba halinda nake ciki."
"Wllh bazanji tausayinka ba nagaya maka kadena samuna da araha."
"wllh ke bame arahabace idan kinason duk abinda na balla ka aduniya zanbaki kibiyamin bukata yafi."
Abinda nake so dayane awajen kuma ka tabbarar minda bazan samu ba shine kace kana sona."
"idan ana magana kidena kawo banun so Fandau sonki yayiwa bakina girma da na furtashi idan kuma kinaso nafurta ne _INASONKI INA SONKI_ ."
"Taya zanyar da kai bayan kai din makarya cine mayaudari kayaudare ni kamin karya har gaban iyayena kace nabi wata saudia bana sonjin son naka dan bansa meshi asanda nake soba taya zanyar da da kai bayan nasan kai waye ne afannin yausara.
"Wallashi yanda nake sonki ban tabajin ina yiwa wani abuso kamarki ba kiyar da dani ki bani DAMA ki karbi sona zaki sameni mai amana akaru na 2."
"a a Rike abinka dan banyar da dashi ba."
dukan kirjinsa yayi da karfi Wayyo zuciya bazakayi magana ba kafito kanuna mata son nata da yake dankare atare dakai baka da amfani inde bazaka yi magana ba kafito zuciya Fatina shiyasa nace miki sonki abaki bazai faduba.
Zatafita mamakinta kawai sai taji fashiwan kukan Nabil tana juyowa taga kuka yake wuiwui yana dukan kansa da kirjin sa rasa ma yazata yi tayi dan bazata iya fita ta barshi acikin wannan haliba dan tayi mugun tausayin sa gashi idan ta tuna gargadin Dr da Baban Nabil sai taji idan ta amince dashi yanzu ba ta kyuta ba amma sai wani zukiya yace idan yamutu wa akayiwa asara dama ba anacewa tsakanin macce da miji sai ALLAH ba kawai saita fara takawa ahankali har kinda yake shiko kukan yake cigaba da rusawa
Karasawa tayi ta zauna ta daura Akkam aciyar ta sannan ta dago habar Nabil idon sa yayi ja da fuskan sa
tace "ka dena dukan kirjin ka haka mekake sone.
"kenake so much.
"To aigani gaban ga"
Kawai sai ya jawota zan hade bakinsu tayi saurin girgiza kanta
Tace "tokaga abinda yake tabarar min da jikina kawai kake sha awa kenan
yace "komai naki inaso nide nasan inason komai naki."
Ganin bazai yuwuba saida lallami yasa tayi da baran gwara ta lallaba shin
"to kaga yanzu bai kamata muyi wani abu adakin Mama ba kabari da safen asan yanda za ayi."
Dasauri yace "to mufita agidan.
"a a Abu Fuj baka tsoron yanda mutanen gidan zasu fassara ni yanzu ma tun dazu nakasa fita a part din Mama amma haka ma ban tsira ba har na ake biyoni da bakaken magan ganu sai ma gobe idan yaransu da suke aure sunzo zanji sauran."
"kigayanin suwaye suka gayamiki magana?
Wllh bazan bar duk me kunta ta mikiba. "
Tace"a a kar kaga lefisu ni cime babban lefi ai abinma yazomin cikin sauki banzata zaizo da haka ba."
"to yanzu yakike sonnayi."
"Kajen dasafen kadawo."
Kamar wani yaro haka ta dinga lallamin sa dakyar ta tasamu ya yarda zai tafi amma saida yadan rage zafi
Yana rugume da Akkam suka fito falo yace "wllh duk harda lefin Dr wanan yaron cemin yayi wai dansa ne shiyasa nake son ki gayamin gaskiya ya akayi kika gamu da su dashi shegen BG din."
" duk gobe zakaji.
A parlour ma daker suka rabu dazuman shikam anan sai kwana dan yajima da sallama escort dinsa ba inda zaijen sai anyita ta kare
Ita ko Fandau tana samu yana fita tarufo kofan tana cewa zaka gane kurinka tunda nasanu *DAMATA Bazan bari DAMAR* ta kufce min ba saina rama duk abin da kayimin amma har ta kwanta kalmo minsa na soyyyya daya furta mata ne yake mata yawo akunne gakuma kamshin turaren sa da tajima tana mafarkin sa ajikinta wani k'aran dadi tayi da tatuna wataran ko tace nanda dan kankani lokaci zata amarce juyi tadingayi tana murmushi
shima anasa
ban garin hakane kwana yayi yana juyin dan ALLAH ALLAH yake gari yawaye abashi matar sa banda suranta ba abinda yake bijiro masa
Sai asuba yasa mu bacci bayan yadado daga sallah falon da ya kwanan yakoma yakwata akan kujera saiko yasamu bacin ya kwashishi cikin mafarkin me dadi
Washe gari Fandau bayan anyi sallan asuba ta durkusa ta gaida Mama tace "Mama inason naje gidan Bagana Mama ta kalleta taganta da shijab har katsa kibari ita ma zata zo anjima kad'an zaki ganta idan kikaje sauran yan uwanki idan suka zo bazasu ji dadi ba.
"Mama idan na zauna ma awajen su ba fita zanyi ba ba komai zai kawosu basai sai yada magana.
Mama tace "to kema kinsani dole ki zauna ki karbi lefinki kafin komai ya wuce ai kinyi abinda ba atabayin ba azurir ku dole ayi maganan kuma dole ki karba kina ji jiya ma da nafita wajen girki su Ya Karu ba maganan da basu gayamin ba ashe su amin bai musu dadi ba wai nayi muku rokon Allah duk kunsamu masu kudi suke bakin ciki da Bagana ma balle ke wai zaki wari BilAL dan gidan Alhajji Maina Gange masu kudin garinan ga na hada jini da Nabil wanda zamu lashe dukan dukiyar sa nayiwa matar asirin ancire mata mahaifa Lalle nayi aiki,
kede kinsan ba rabuwa zakiyi da magana ba yanzu idan ki kaje gidan Bagana haka zaduce kinnuna ban banci kizauna sai andan kwan biyu.
Fandau tace " Mama idan nazauna agigannan to plan dinmu da baban YaShid bazai yuwuba ba YaShid yana da shigen naci akan abinda yake so kinga jiya ma wai saiya tafi dani dakyar nalallaba