Showing 108001 words to 111000 words out of 144533 words

Chapter 37 - Dama Ta Book 1 Hausa Novel Complete

nata har yayi dialing amma aka ce masa anrufe layin gaba daya cikin haushi yasake shiga cikin sakon nin nata yaci karo ko da sokon da take cewa.
_To YASHIDDAS yaune tashinmu fa dan ma nasan zakaje bikin mudan yazame maka dole_
Afili yace.
" Towai ko da gaskene?." da sauri yagirgiza kai yace.
" Sam bade BilAL dinaba bayanda za'ayi ya shirya aure batareda ya gayamin ba."
amma shi yanzu duk bawanan ba yafison yaji muryar wanan wanda take masa gizo da Fandau

Yana cikin haka wayansa ya fara ringing yana dubawa BilAL ne ya dauka yana cewa. "Kamar ko kasan kaine araina dan yanzu nake shirin
kiranka."
BilAL yace.
"Sai kuma gani ba toya akayi?."
Dariya Nabil yayi yace.
"kimanin 3 months kenan muna chat da wata yarinya har tace galabata mukayi dan sabo da ita to dan tamin tayin kanta nace a a, yanzu kuma naci karo da sakonta wai dama shaharata a wasan ball take so yanzu tasamu wani shima shaharare ne burin ta yacika kawai saigashi ta toromin pic dinka dan ita wawuyace."

Dariya BilAL yayi yace. "Me abin wawanta kan aciki ai wanda Fatima tayiwa tayin kanta yaki amsa shine wawa domin *DAMACE* babba sosai tazo masa yasake yarinya yar sarauta yar babban gida bata inda bata kai macce ba,
burin kowane namiji na karbeta nikam dan gudun kar *DAMATA* ta kubcemin,
yanzu haka ma ina airport din London zan tafi neman auren ta ahe dasai dai kaji na angwace."

"Wai dama da gaskene ?to wacece ita tacemin sunanta Fatima Muhammad garga,
kai kuma gashi kacemin Yar sarauta ce yar wane gidane kaina yadaure? ."

BilAL yace,
"yes da gaskene naji tausayin tane dan tafadan min tarihinta kakaf kusan irin abin da Hadim tayiwa matarka,
aka mata saide ita ba aci nasaran sa mata alluran ba,
kuma ita nata zalincin ma yayi yawa wai fa auren sukayi dan ta haifu su dauka sumata sakin wulakanci kuma har ta haifun yanzu haka yaranta ukku suna wajen su amma tafita da cikin nabiyu amma acewar ta wai nima nasan mijin nata masai dai dan tanason cusa masa haushi bazata gayamin ba sai bayan munyi aure,
Da auren gaggawa naso muyi da ita saboda nina daukawa kaina lefin nina yaudareta na aureta gudun kar abata wani wada Iyayen suka zaba mata nikuma inason ta shine muka gugu na aureta,
dan tacemin
kishiyoyin Mamar ta zasu mata gorin taje karuwanci amma dayake ta na tsorace da abin da wancen mugun ya mata shine tace ita sai anje gaban iyayen tukun ."


Cikin firgice Nabil da yaji kamar ya dankare awajen kode Fateen sace
Dasauri da rawan baki yace.
"tagaya ma ya zaman ta kewansu ta kasance? tagayama ya yanayin yaran nata yake mata ko maza?

"Eh tagayamin da farko macce ta haifa na 2 kuma twins duk maza
Yana yin zaman su kuma labarin da tsawo idan kanason ji ka sameni a airport din dan bayanzu zamu tashiba."
ai Nabil baima gama sauraron BilAL ba yakashe wayan jikin sa yagama bashi Fateema sace kawai da sauri yashiga gidan.

amma me yatarar ana wani danjan da Inna ZAINABU idan maku manta ba a koi photon Fandau adakinta na itada Bagana da Mama kuma na taba cemuku Fandau da takeson koyan rubutu tarishin rayuwan ta take rubutawa to pic din yana cikin wannan life story nata ta turashi kasan bed sai yau yasmin ta fito dashi tana gama karantawa ta cikin kuka tace.
" Wllh awannan karon idan ba ayarda dani ba zanfasa kowa yaji." kunsan Yasmin lawyer ce mekare hakkin dan ADAM dan haka tana da mugum tausayi gakuma ta jima tana tara bayanan dan bata yarda da yanayin Hadim ba su Jidda ko dasu aka karanta Inna ZAINABU da Maman Fandau duk suna dakin sai da akayiwa Inna filla filla ta tusiye maman Fandau akan ta fada mata gaskiya aiko Mama ta fadi iya abinda Nabil ya fada musu dai ita bata so hakan ba ta fison taga Nabil yacire taurin kai yafadi komai da kansa kuma ko min daren dadewa tasan gaskiya zaiyi halinsa.


Dasauri Inna ZAINABU ta sauko har tana hardewa ta haye saman Hadim da dama Mamar ta da Ummi sun sata a sakiya ta fadi gaskiya dan dama agaban Ashuwa kanwar Hadim abin yafaru dan haka ita tazo da gudu da gaya musu shine fa gidan yasake cakud'ewa Inna tana ganin Nabil tace.
" Zonan babban munafiki itan idan shegiyar muguwa bata fad'i gaskiya ba ai kai baka isa kak'i amsamin ba."
daganan tabasa bayani komai yace.
"Hakane amma batun yara natane ba gaskiya bane,
"K'arya take yaran Hadim ne."

"Kunci uwar da kaida uwar Hadim din munafuki matar taka mai kugun mazanne zata ta hafi yara har ukku,
Dama Dr Hafeez yace min bata taba haifuwa ba kuma tana da matsala,
bazagin da banyiwa yaron nan ba har maita na daura musu har uwar Hajja meram saida naje nayiwa cin mutumci kuma nace idan Halima bata haifu lafiya ba to dasa hannun dan ta sai nayi shari a dasu yanzu haka ina cuku cukun makashi kotu,
wannan abin ya bullu gaskiya tayi halinta ashe kune abin jefawa kotun wannan wane irin masifa ne ALLAH kakawo mu karshe zamani da mutum zai iya jin abinda yafi karfin jinsa wanan wane irin masifane?."

Shiko Nabil bama fahim tar ta yake ba hankalin sa yana wajen BilAL ga ihun da ake masa yarasa ma meyazo d'auka cikin dan haka kawai yace "kuhada kayanku kusameni a airport."

"au ni ban isa kagayamin ba sai munje gaban uban ka za kama fadi gaskiya ai dama yasmin tace min a haifu wan fari ranan da Hadim tace ta haifu tagan ta tana sallah da sauran bayanai dan de nak'i yarda ne ashe kune mak'aryatan ko duk jikina kunne ne bazan yarda dakuba."

Shide ficewa yayi bai tsaya ba."

Zaune suke wani kebeben daki na musamman acikin airport din
"Yanzu kana nufin har ka yanke shawaran aure batare da sani naba kenan?."

"Shiddams kenan ai ance *ASIRIN CIKI SAI HANJI* kuma kai ba auren ma kayi har kazauna da matar tayi ciki batare daka gayamin ba,
nima kuma surprise din ka nasoyin dande kazomin da batunne da bakaji ba amma yanzu ai andena yarda da kowa yaro kayarda da kanka kawai."

Nabil yace.
"Kai kasani niyanzu bani tarihin nata tukun."

Dariya BilAL yayi yakwashe komai yagaya masa...
Ai tun kafin yakarasa jin lbrin ya zube k'asa yanayiwa ALLAH sujjadar godiya yad'ago yana cewa Alhamdulilah Rambana."

Bilal yayi murmushi irin na nuna ana tayasa murnan nan
Yace.
"ai nasan dole duk wani masoyina ya tayani murna sai ma kaganta wllh nasan har kyutan kujerun Makkah sai kayi thanks kum....!"
Nabil yace.
"Wane kai wllh itace Fandau d'ina ita nake nema."
BilAL kamar da gaske Afirgice yace. "what!?"

"Wllh itace nima bansan yanda akayi ta samu lafiya da kuma zuwa London ba."

BilAL yace.
"To kadawo hankalin ka dan ita taka bata tab'a haifuwa ba niko wanan ta haifu yanzu ma cikin da tafita dashi yananan tana goyon d'an,
in maso kake na barmaka ita dan kai tafara cewa tana so to wllh baka isaba,
nariga nakamu da sonta kariga kasaki daman ka niko bazan yarda nasaki *DAMATA* ba dan sau d'aya take zuwa arayuwa kuma inajin son....!"
Ai kafin yakarasa fada Nabil ya wankeshi da wani irin marin da yajawo hankalin Security's d'in BilAL dana Nabil suka shigo da gudu amma ganin abokai mafi kusa wanda basu isa su shiga tsakani suba yasa sukayi curku-curku shiko Nabil duk yagigice mari kawai yake zubawa Bilal ya cukumo wuyan rigansa shiko BilAL tsayawa kawai yayi yana kallon ikon Allah wai yau shi ake mari bai taba sanin mezafin mari ba sai yau sai da yagama iya marin sa yagaji har fuskan BilAL ta kumbura yayi jajir abin kida fari ga hutu sakin sa yayi kuma yadurkusa agaban BilAL din yana rokon sa yagaya masa inda matarsa take da gaske cikinta bai zube ba.
shima BilAL dur kusawa yayi yace.
"Haba Babana me yayi zafi ka hukunta danka haka kaga yanda kamin akan mace,
lallai na yarda mata masifane kalli yadda kamin."
yaja hannun Nabil ya d'aura kan fuskansa shiko Nabil hanunsa yajanye yace.
"Ba maganan wasa bane seriously ina matata?
Kai kanka sheda ne yanda nasha wahala akanta gayamin inda matata take?."
Bilal yazaro wayansa yace.
"Ni kaga tawa banajin tana kama dataka."

Dasauri Nabil ya d'ago jajayen idon sa ya zubasu kan pic din Fandau da tayi wani mugun kyu wanda bayan kyanda tayi saida akayi editing duk yanda aka canzata idan yaganta bazai kasa gane taba yafara magana
"kagani ko Wllh itace ina take?."
Ya Allah yasake daga hannu yana godiya ga Allah

Daure fuka BilAL yayi.
"To idan itace me hujjan ka kokana da huja bazan barmaka ita ba ai koda itace wllh baka isa na hakura da itaba azabure Nabil ya tashi yana tunkaran BilAL yana cewa.
"Matata cefa da aurena akanta ko atarihin kaji kalman saki a ciki da kake abbaton kana sonta zakayi mugun nadama idan bakinka yakara furta wani kalma akan matata."
a hatsale
Bilal yace.
"Kai kaine zakayi nadama idan kak'ara cewa kasan Fateema dan tawace ka.....!

ai BilAL bai karasa ba sabo da wani irin shaka da Nabil yayiwa makoko ransa........!


*To mabiya DAMATA yakukaga page gaba zai kasance dan kunsan dole agurfana gaban ZANNAH MODU abinda kuka dad'e kuna nema anza wajen fa ga Inna danja natafe ya Hadim zata dauki bai yanan FANDAU*
*dan Fandau tace mata rance ba kyuta bane* ...!

*karku manta fa tsakanin abokan biyu akwai rigima NABIL yayiwa BILAL rashin kirki bayan uban BilAL shine yayiwa Nabil gata ko ya manta ne

*

*B JATTKO*
[3/12, 8:50 AM] Hauwa: *DAMATA*



*NA*

*BATUL ADAM JATTOKO*

*44*




*j*uyowa BilaL yayi yakalli securities dinsa dana Shiddams alama yamusu da sufita,
sumi sumi suka fito amma na BilAL ba ason ransu ba sunso su dauki mataki amma ba yanda zasuyi shiko Nabil sai sake shakansa yake yana cewa
"nace kafitomin da mata maci amana agabana kake cewa matata zaka aura....
"to sakeni na gaya maka."
Da sauri Nabil yasakeshi
Yace" gayamin."

"haba my Abu zauna mana yanuna masa kujera sai da yabari Nabil ya zauna ya fara magana amma yana maganan yana tafiya hanyan fita adakin cikin dabara yana cewa "Gaskiya nayar da matar kace don da bakin ta tacemin mijinta makusan cinane dan haka ma tace ayi auren gaggawa dan idan nasan waye mijinta bazan Aureta ba amma saide gashinan da nasanen ma bazan iya bar maka ba dan nikuma Dagaske na kamu da sonta dan haka mufafata agaban Zannah ko."

Yana gama cewa haka cikin zafin suna yan'wasan ball ya fada waje yaja kofan da sauri ya rufe Nabil aciki har da key yazare key din yayi office din Gdororo yabashi yace "ga key amma kar abude shi har sai muntashi."
Gdororo ya girgiza kai
Bilal ya wuce jirgi shida security shi wanda ya shirya tafiya dasu dama ankusa tashi

Hadim kam sabar bacin rai yau saida tarufe ido tayiwa Inna ZAINABU rashin kunya
Inna taja hannun Fuj tace "zonan Hadim tareke hannu Fuj itama tace "agaban ki yanzu Nabil yace "yara nawane danme zaki karyata shi bashine uban su."

"ai duk kan shedu sun tabatar min da yara banaki bane gashi arubuce nima nagani yarinya tabar komai arubuce."

"to Inna tunda baki yarda anyi hakan nedan abata mana sunane ba kiyi yada zakiyi naga uban wada ya isa ya juya yananan su zama ba nawa ba aikin banza ina jiran naji an makani akotun."

Inna ta kame baki "Hadim ni kike zagi yau.
Kafin Inna ta karasa maganan har Khadija yar gidan Inna ta wanke Hadim da mari kokuwa suka fara Hadim ta doku dan bata da lafiya Ummi da Maman Hadim kuka suka fara da kyar da temakon Maman Fandau aka rabasu fadan Mama Aisa bataso abin ya kasance da haka ba aiko koba komai Hadim tanada nata hakkin na shayarwa akan yaran
Inna sai cewa take ai ayau kinkawo karshen Aurenki da Modu.
Hadim batayi magana ba dan ta kanta take ciwonta ya famu sosai
Maman tace"
de sukayi ta da Inna haka suka tarkata sukayi airport din rankowa ba dadi saide fa Inna ta hana yaran dukka ta goyi BilAL ta bawa Mama Aisa maaf Fuji tana wajen Zahra dasuka zo airport

Shiko Nabil yana ganin BilAL yarufe shi ya fara safada marwa komai nasa ya kunce dama da Fandau dinsa yake chat ya akayayi hakan ta faru ina alluran da aka mata ta samu hankalin chatting meyake faruwa maganganun BilAL da wanda Fatiman Chat idan suna chat take gaya masane kawai yake masa yawo a cikin kwakwalwa

*ummm Abu Fuj kenan baka ta bacewa kana sha awan ganina ba fa ina jiyema ka nadama ranan da kasan koni wayen*

A'lokacin ina shiko kulata bayayi dan yasan bawata a gabansa illah Fateen sa
Gashi yanzu abinda ta ke gaya masa ya tabbata
Wlh itace ina BG yaganta ina yasanta meyasa bai gayamin ba ina take yanzu har dororo yazo ya budeshi yace "yatafi ko? suntashi ko?
Dororo yace "Shiddams suntashi. dukan hannun sa yayi yace "AD shir yamin tafiya yanzu Dororo yace "a yanzu haka gaskiya bawani bucking na zuwa 9ja gaskiya idan ka matsane ma zuwa gobe akwai mezuwa Gabon kaga sai nasan yanda zanyi yafara sauka a Nigeria ko.
"a yanzu na keson tafiya ko akwai wada ya isa hanani tafiya asan da naga dama inada jirgi har 2 acikin airport dinnan.
"Dororo yace "oga gori najiran ranan fad'a amma ai duk da kana dashi bashine zaisa kasame shi sanda kaga dama ba dan haya kabada ba kyuta ba amma girmanka da kimar ka yaci a shirya madin saide ayanzu ba jiri akasa wanda ya fuce duk da safen yau suka sauka saide akwai wani Zg to gaskiya yayi girma idan akace kabiya Drop dinsa akwai kudi fa."
Tsaki Nabil yayi yace "akwai din kenan.

Nabil kam yamanta mada batun su Ummi saida yaga kiran Khadeeja ya dauka yace "dije yanzu zamu tashi fa ss dinsa yayiwa magana yaje ya nuna musu jirgin da zasubi
Nabil acikin jirgima jiyake kamar ba za ajeba duk wani fargaba ya gushe masa murin sa yasauka yanemi BilAL kawai
kulle kansa yayi awajen na musamman acikin jirin ya kasa sha bare ci
Inna kuwa sai sake jajjaba abin take maman Fandau bata hakuri har Allah yakawosu meduguri Nabil motan sa shikadai yahau sai drive da yake tuka shi bai san ina zaisamu BilAL ba dan haka yazaro waya ya kira babban yaron BilAL yace kuna ina yaron yakalli ogan girgiza masa kai bilal yayi alaban yace bai sani ba
"Sir kanason ganin ogane koni?
Uban me zanma ogan naka nake nema.

"Sorry sir mun rabu da oga a airport ne yace yanada wajen suwa mu muzo gida kakira shi kaji.
''da suwa kukarshi?
Alama bilAL yamasa da hannu akan yace shi dayane ai yana gayawa Nabil yace karya ne BilAL baya zama shidaya dan haka duk inda yake kai nasan kana wajen idan baka gayamin inda yake ba na bincika nagano wllh zakayi nadama BilAL yasan halin abokin nasa dan haka yasa hannu yakarbi wayan yana dariya yace "anki afa d'ama inda nake din mugun uba Babana kanason karasani ko inde maganan matar da zan aurane kaje gaban Zannan kanemeni mana dan ni agidan na sauka na gama masa bayanin komai,
Kai mukejira muji ta inda me haifuwa 3 tazama matar ka.

Nabil yace "Please Bg ganinka kawai nakesonyi akwai wani tambayar dazan ma ne.

"Haba Baba inafa son raina dan nasan muka sake haduwa ba manya akusa rabani dashi zakayi.
yana gama fadan haka yakashi wayan gaba daya yamekawa yaron nasa dan shinashi nun ajirgi yakashe
Shikuma Nabil hanyan gidansu BilAL da yake porlor yayi

Su Fandau dama tun last week suka zo
Suna kaduna agidan Dr na *kinkinau* yau suka shirya zasuje gidan Malam Dauda da ita dan dama Dr yagaya musu komai amma yahana Malam kar yagayawa zannah dan yafi son Nabil ya fada da bakin sa
Fandau tafito cikin wani lafiyayen lace maran nauyi light blue takallmin ta flat shoe ne maki sai mayafinta baki da jaka mahadin takallmin kana ganin kasan ba kananan kudi ake kashe mata ba dan Dr dayasa muguta aransa sakin bakin aljuhu yayi yana ta barin kudi akanta ga BilAL yana bada nasa gudun muwar sosai suka fito da ita kalan fatanta kawai ya isa sheda cikin wani irin taku take saukowa tana lase lasen wayanta dan Habiba tasata grp na manyan mata harda Hadim aceki dan tsabar tsokana ma Fandau Mrs Shiddams tasa a sunanta sukuma yan group tunanin su Hadim ceta canza layi saiyi suke yajiki ashe kindawo na can London kuma suna cewa yaushe kika tafi
Dande Hadim yanzu ta kanta tace bata gani ba sukuma kawayen idan suka kira Fandau cewa take ba Hadim bace ita kuma Hadim bata masamu daman wani amfani da waya ba
Har takarasa saukowa Habiba baki bude take kallon ta
"Wow Aunty kinyi kyu inama yaya yagan ki haka.

Habiba tace"bana son gatse fa kinaganin kanki kuwa Fandau tafiyanki kadai abin kallone nede kar kidinga wanan tafiyan agaman mijina yagani yare namin dan ma nafara koya nima awajenki.

Dariya Fandau tayi"tace haba Aunty har wane tafiya na iya karki zama Abu Fuj mana wai atafiya ta kadai yafara jin sha awar yagani wacece wai atafiya na kadai yagane ni ba tsohuwa bace ranan da yafara ganina haka kowa yakecewa ni meyangace wllh Aunty bansan yanda zan canza ba.
Habiba tace"Fandau
Kin iya tafiya tun kina yar gargar dinki ma balle yanzu da kike jinkanki kema watace bame kalloki yace baki gama ganin karshen biro ba duk inda macce me aji takai awanan duniyar kinkai zanso Shiddams yaganki ahaka bame ganin ki yace kintaba sanin me aure.

"to ai Aunty dama girman ne na dole dakuma yanayin gidan muna rashin sa macce aboko amma har yanzu fa shekaruna 19 kinga ko acikin manyan yanmata ma baza asani ba har yanzu banfara nawa yan matanci.

"shegeya kinason kicemin sai agidan Shiddams azama nabiyu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login