Showing 27001 words to 30000 words out of 133935 words

Chapter 10 - Mijin Buzuwa Book One Complete Hausa Novel

27 Oct 2025

245

Yusuf din.
Har na karaso bakin motar nasu sai a lokacin nasan tare suke dashi fadi yusuf ke yi da na karaso wai wanan haduwa haka fa kanwata .
Kaike kara zuzuta yayi maganar kamar bashi ya fada ba yace ba dole ba in zuzuta kanwata yar gidan mama wanan ai kyasa ayi karo a hanya nidai murmushi kawai nayi mashi.
Na fara gaida su yace shigo mu sauke ki mana ba hostel zaki koma ba nace a a nagode yayana ku tafi abinku kawai dakai dayane zan shiga amma dai ku tafi kawai.
Yace au don wanan miin buzuwan da kika gani ai bashi ke jan motar ba ko shiga muje don ki kawai muka biyo nan fa.
Jin haka yasa na bude motar na shiga batare da na sake wani magana ba shiko sai aikin shi yake yi kawai ana tafiya mun kai wurin wani babban shago yace don Allah ku bani minti biyu in dawo.
Ya faka motar yafita sai mu biyu a cikin motar kowa da abinda yake yi a lokacin sai can naji yaja tsuki yana kallon shagon na dauka dani yake yi nace dakata malam bafa kai ka dauko ni ba da zaka ja min tsuki haka.
Da mamaki ya dago kai yana kallo yace ke dani kike nace da wani nake haka kawai zaka kama jamin tsuki a mota da mamaki yake kallo na yace ke wata irin yarinya ce da bata da tarbiya.
Kadai gyara maganan ka malam tarbiya ai ko makaho yasan akwaishi nan sai dai a lalaba a gani ai ba bace marasa tarbiya suke ba.
Bai kai karshen magana ba cikin zafin nama da kunar zuciya ya juyo inda nake yace wa kike nufi baida tarbiya cikin muryan nan nashi mai dadin saurare da yake rowan ta.
Tsoro naji ganin irin kallon da yake bina dashi mai kama da harara ko tsana sai nayi kasa da kaina na kasa furta komai don kwarjin da yai min a idona
Ya nuno yatsan shi daidai saitin fuska na tare da tsure ni da idanuwan shi lumsarsu yana fadin ke in badan Yusuf da bai san ciwon kan shi ba har kucaka irin ki ta isa ta shiga min mota na a tare dani.
Yace kallani nan ko a hanya nagan ki baki isheni kallo ba a cikin mata don banga abin gani a wurin irin ki ba cikin dakiya da dauriya nake kallan shi ina jin kalamin shi har cikin raina sai dai ina tara abinda zan mayar mashi ne a zuciya ta duk da naji tsoran yanayin shi.
Yaci gaba da fadin idan baki hankali da ni ba watarana sai na balbala ki wallahi don ni mace bata kawo min raini nace dashi.
Don Allah malam matsamin bakumayi mamaki jin haka don ba abin mamaki bane don ka fadi hakan tunda dama kai irin maza nan ne dake raina jinsin su sai kai ido ga mata ketere saboda zalama irin na rashin sanin ciwon kai.
Don wanan matar taka abin kyama ga jamma a da kai ka mayar mutum har kake ganin tafi ko wace macen kasan nan dadin abin dai kaima macen kasan nan ta haife , , , ,
Fat naji yakai min bugu a baki don zafi sai da na dafe baki na ina dubawa ko jini yake min ban san lokacin da idona ya fara fitar da hawaye ba na yun kura zan fita daga motar yasa hannu ya danna lock mutar ta rufe kit yace kuma ki saurare ni.
Duk kika sake ganina a mota kikayi gigin shigan shi sai ya jefar dake a waje mota ya take ki kin mutum in kashe ki in kashe bazan .
Nace ni wallahi ba banzan bace sai dai in kaine yace bakin naki bai mutu bako yana kokarin kai hannun shi ya kamo baki na na noke kaina a kafana sai bai samu kama bakin nawa ba.
A daidai lokacin Yusuf ya iso wurin da manyan ledoji a hannun shi yana bude motan zai sa ganin mu haka yasa shi ya sake murmushi.
Ina jin shi nayi saurin dago kai nace mugu kawai azzalumi yace kai yaya haka may kai mata don Allah take kuka kuma ya waigo zai kara jamin baki na noke ina son fita a motan Yusuf ya tare ni yana fadin haba dai yaya zakaci zalun ta kuma haka ?
May tayi maka haka wai kasa ta kuka ya juya yana cewa bakin nan mai rashin kunya na daka ido ya zaro yana cewa ka dake ta Abdul ?
Kadan ma ke nan nayi mata ai fita nake son yi ba hanya don Yusuf dake wurin yayi rufe kofan ya zagaya ya shigo motar sai da muka fara tafiya yace ka bata hakkuri Abdul.
Ina baya ina kuka naji ya fada mai hakan yace nace ka bata hakkuri yace wani zanba wanan yariyar hakuri ko wa yace bakai ka zalunce ta don may bazaka bata hakkuri ba ko kafin ka tafi da hakkin ta ne a kanka ?
Baiyi magana ba sai aikin shi dayaci gaba dayi yace wai may ya hada kune haka da sauri nace zagina yayi na rama.
Motar ya tsaya a kofa gidajen mu na fita da sauri ya biyo ni yana kirana ban tsaya ba wata yar gidan yaba kayan ta shigo min dasu suka tafi ban san yadda suka karata ba.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Ina shiga ruwa na saukowa daga sama da karfi dama hadarin da ya gama haduwa a lokacin kiris yake jira ya fara zuban ruwa.
Ruwa ake sosai a lokacin na kuma san basu kai gidajen su ba duk da ba zan iya cewa ga nisan gidajen su ba a lokacin.
Na fara cire kayan jikina aka turo kofan dakin nawa da na saya da sauri na juya don ganin wanda ya shigo min a wanan lokacin haka.
Maryam yace sabuwar kawar da nayi a cikin hostel din namu tana rike da wani warmer dain abinci na silver mai marika tashigo tana dauke da murmushi a fuskanta nima murmushin na mayar mata a lokacin nace cikin ruwan nan kika fito.
Tana aje kulan tace tun dazun nake dakon dawowar ki ai sai yanzu na ga wuta a dakin ki na san kin dawo gami da yi min sannu da dawowa na amsa ta.
Na karasa cire kayan na daura zani a jikina tace abinci na kawo muci don yanzu na samu yar uwa na huta zaman kadaici hakana murmushi nayi ina zama a saman katifan nace fitan nan nawa har kikai girki haka ?
Tace dama akwai miyan a fridge sai shinkafa ne kawai na girka muna yanzu nayi mamakin jin har da fridge a dakin ta don ban taba shiga ba sai ita ce mai zuwa dakin nawa.
Ido na ta kai ga ledan da na shigo dasu dakin yanzu na dauko na fara budewa kayan mata ne a ciki irin doganyen rigunan nan har kala biyar sai takalma da jakka biyu.
Sai dayan ledan mai dauke da kayan drinks da su packed din sweet irin mai tsadan nan tace woow duk wanda yayi sayayan nan yasa kansa wanan rigunan duk letes ne fa don anty na business din da take yi ke nan wanan dawowan da tayi daga dubai naga ta dawo dasu har nace taban guda daga ciki tace sai dai in saya.
Nace uhmm kyautar maya ne haka maryam wasu yan yan gari mu ne da suka zo yanzu muka fita tare suka saya min su.
Maryam tayi dariya tace manya ko ba nawa sa ba nerbough don wanan wawan kyautar sai da wata a kasa kin san ko ba karamin kudi aka kashe wurin nan ba.
Nace kuma kin ga ba wani abu a tsakanin mu sun dai ce ne mudan fita in rakasu wani wuri ni ban ma shiga shagon ba Yusuf kadai ya shiga sai gashi da wa yan nan kayan haka ya fito.
Tace haka abin yake ai don masu kudi basu jin zafin fitar da kudin su, ga abinda suke so don wanan kyauta ai ta maya ne daganin su duniya na damawa dasu Allah.
Nace sam ban san yayi min wanan mahaukacin sayayya ba da na dakatar dashi wallahi ni na dauka ko irin dan drink's din nane da sweet fa.
Maryam tace may ye na damuwan kan ki tunda bake kikace su saya maki ba sai dai gaskiya kyauta yana nuna alama ga abinda ake so ne.
Nace so kuma ai sun san ban da lokacin wani so a yanzu kawai dai raayin su ne yin hakan sai dai zan dakatar dashi ga yi min haka nan gaba.
Abinci ta fara zuba muna muna hira na kwashe kayan na kawar gefe guda ina ce mata kinga yanzu sai dai mu canza tsari ba wai kullun kita dafawa kina kawo min muna ci ba haka.
Dariya tayi tace kin manta da rana naki mukaci shiyasa nima na dafa muna yanzu muci ai ko hakan kuma laifi ne nerbough ?
Muna ci muna hiran makaranta da ita har mun kusa gamawa wayana dake gefe yayi kara da sauri na mika hannu na dauko don kada ya tsunke.
Daddyn mune akan layin na dauka da sauri ina hadiye abincin da ke a bakina yace may kike ci haka khadja ko dadi kuke ci a makarantar mu muna nan gida muna hadiyan shikafa da mai ya fada cikin zolaya .
Nace daddy Allah ya nuna muna mun samu kuma kuji dadin da iyayye ke ji ga diyan su watarana indai zakuyi farin ciki da hakan.
Yace ko yanzun ma mun gode maku don muna cin moriyan ku a haka yaushe yaushe kika turo muna da kudin hannun ki wai mu kara nayi fada ai da yar uwarki nace ke da kike makaranta kin fimu bukata a yanzu ai.
Burin mu daya shine muga kin tsayar da miji da wuri kiyi koyi da yar uwar ki kema kiyi aure basai kin yi dogon karatun nan dakike so ba.
Dariya nayi nace kai daddy aure yanzu kuma nida nake son in zama babban lauya kafin in aure amma tunda naga raayin ka ke nan ba damuwa .
Daddy da izzinin Allah zan cika maku burin ku daddy na karasa fadi cikin sanyin murya daddy yace da sauri .
Dear kada ki sa wanan a rai yanzu buri na fada maki kawai shi aure ai dan lokaci ne indan lokacin yayi ko da shiri ko ba shiri zakiyi ne ai nafison in ganku cikin farin ciki a koda yaushe bana son bacin ranku kada magana na ya kara maki zuciyar ki akan karatun ki.
Ya kara da fadin Allah dai yayi maku albarka dake da yan uwanki don baku taba bata muna rai ba da halin ku.
A hankali na goge hawayen da ya zubo min a idona nace mukai sallama dashi bayan ya gama kwatar min da hankali na.
Maryam ido ta tsura min ina aje wayan tace dani ina son nima inga ina haka da iyayyena wallahi sai dai hakan bai samu ba a gare ni don na taso ne ba tare da iyayyena a wuri daya ba.
Mahaifiyar mu sun rabu da babban tun muna kanana sai dai idan naje inkai masu ziyara dukkan su tunda riko na yadawo hannun yayata.
Nace Allah sarki lalai dole kiji sha, awan hakan gaskiya don iri haka babu daddy ni kinga iyayyena sun fi son suga nayi aure ko yaushe maganan su ke nan a kaina.
Sai dai ko yaushe auren nawa zai zo ban sani ba tunda ko sauriyi tsayayye ban kai ga tsayarwa ba a yanzu haka.
Tace to ina ga dai yazo din ne tunda ga wanan yanzu da ya fito ya fara nuna maki son shi dariya nayi nace maryam ke nan baki ganewa ne ke.
Bandai fada mata komai ba mukaci gaba da hiran mu sai goma ta koma dakin ta nima na gama abinda nakeyi na kwata.
Har na kawanta naji wayana na verviration a gefena nasa hannu na dauko wayar nace salamu alaikum.
Yar mama kina lafiya yaya ruwa , ?
Na sauke lafiyayyen murmushi nace lafiya kalau yaya Yusuf yace kina kara fasa min kai fa da yayan nan da kike kirana dashi nace kai ka saya a kira ka da sunan.
Nace yaya kuka isa gida kuma yace lafiya kalau sai yanzu na kai mutumin ki gida yanzu haka ina hanyan gidana ne na kiraki mu gaisa.
Yace bayan mun rabu dazu mun dade muna maganan ki da mutumi na nasan zai kiraki yau din na shiya na kira ki in fada maki don naga ya yarda sosai da shawarana.
Nace anya kuwa zan iya cika maka alkawarin da na dauka don mutumin naka akwai zuciya sosai wallahi ni kuma ban iya daukan haka don nice zan taimake shi ba shi zai taimake ni ba.
Dariya yayi yace a yadds kuke yi din nan shakuwa zaizo ya shiga tsakanin ku sosai zakice na fada maki watarana bagashi yanzu ya fara saukowa ba.
Idan ba ta haka na fito mashi ba da wuya yayarda mu aiwatar da komai yadda muke so amma ki daure don Allah mubi abin sannu ni dai buri na shine ki san yadda kikayi kika kara ma wanan buzuwar kadarin ta a gurin jamma,a.
Abin ne da kamar wuya yaya na sai dai zan yi kokari inga nayi yadda kuke so din yace good girl Allah ya taimaka ya bada sa,a nace amin.
Shine kuma ka yi min dawainiya haka mai yawa don Allah nan gaba kada ka kara min irin haka don hakan zai yi maida ni cikin wani yanayi daba shi nazo yi a gatin ba.
Dariya yayi yace Khadija kin san dai sutura shine mutum yanzu don haka farawa akayi don ina son ki goge sosai ki fito a cikin classes ladies ta yadda zamuji dadin aiwatar da komai a cikin sauki nace to na gode sai dai a rage don Allah.
Kada kiji komai mana lokacin kine yayi kawai ki kwantar da hankaki kici arzikin ki a saukake wanan ba komai ba kada ki damu da hakan don har motan shiga ba dadewan nan ba zaki samu in komai ya tafi daidai.
Zanyi magana ya katse ni da cewa na iso gida zan shi sai dai indan mun kara waya don yanzu zamu rage haduwa sosai kada a zargi wani abu a gare ni.
Mun gama wayan ina mamakin su kudi kamar na sata haka nikan ban cika amincewa da irin haka ba azo ba a daidaita ba shirin mu ya watse abarni cikin wahala daga baya.

A hankali ya shigo gidan babban falon su ya samu su hidaya da sauran yan su zaune suna shan bakin shayin su na buzaye.
Gaisuwa sukayi bai tsaya ta kansu ba ya shige ciki bai jin dadin yadda suke cika mashi gida a ko wani lokaci haka.
Duk da wani lokaci abin yana taba mashi zuciya ganin yanzu babu wani nashi da yake zuwa wurin shi kamar lokacin da suke zaune kano da fati .
Yan uwan shi na yawan ziyarar su maza da mata amma tunda abin ya juye haka sai dai kulun idan ya dawo gidan ace mai akwai bakin da suka zo daga kauyen maradi.
Dakin ya nufa ya tura kofa a hankali dakin na nan a yarda ya barshi da safe ba a gyara shi ba in zai iya tunawa yau kwana uku ke nan bai samu lokacin da zai tsaya ya gyara dakin ba.
Don cikin yan kwana kin nan suna zirga zirgan filin da suke son saya a kubuwa ga kuma wanan shirin da Yusuf yake son yi a kan shi.
Rigar shi ta sama ya jefar a saman gado ya kara bin dakin da kallo ya ja tsuki ya nufi yanyar bathroom din shi wani zarni ne ya daki hancin shi da sauri ya fito ya nufi hanya wajen dakin.
Dakin Nafisa ya shiga don yana kyautata zoton tana ciki tunda bai ganta falo ba kuma bai ganta a nan dakin shi ba.
Yana shiga nan ma wani tsami ya tare shi mai kama da karni karni yabi dakin da kallo ga kaya a ko ina watse a dakin tana kwance saman godon dake tule da kayan da bai san ko na maynene ba.
Nafisa na ganin shi tace ka dawo ashe yanzu nake tunanen ka fa a raina nace ko ina ka shiga tunda ka fita da safe baku dawo ba.
Haushine ya kamashi yadda take kwance ta mike kafa sai kadasu take yi tana magana kamar wata basaraka da ita.
Kallon da yake mata ne yasa ta tsargu yace Nafisa wai ke dadin may kike ji ga kazantar nan naki ne haka don Allah dubi dakin da mutun ke rayuwa wai a cikin sa.
Kina mace kice ba zaki iya gyaran muhalin ki ba sai wasu sunyi maki wai ma ina masu aikin da kikace kin dauka ban ga wani abinda suke a yi a gidan nan ba.
Tace Samad yan uwana ne fa ko kuma yanzu kana bakin ciki da zaman su ne a gidan ko suyi aiki ko kada suyi zasu dai zauna anan tare dani ne ko ?
Nasan wanan munufakin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login