Showing 24001 words to 27000 words out of 133935 words

Chapter 9 - Mijin Buzuwa Book One Complete Hausa Novel

27 Oct 2025

244

in makara take cewa dani zata fita amma wai za a kawo mata sako shine take son in karba.
Nace zarah fitan kuma zakiyi yanzu tayi dan guntun tsaki tana fadin eh wani friend dina zaiyi tafiya nake son inje muyi sallama dashi.
Zarah ba zaki wankan ki fada ki zauna ki abinda iyayyenn mu suka kawo mu yi ba wanan dabiar da kika dauko bai da amfani gare ki nan gaba.
Ta dan yi murmushi ta nufi wurin da taga na aje plate din abin ci da tukunya tana bude bayan ta bude ta dago tana dariya tace an fada maki yadda bakin san wayen kai ba haka kowa yake yanzu da anganki kamar may wayayen kai .
Nace in dai irin wanan wayen wane kada Allah ya nufe ni da yin shi ina neman tsarin Allah ga irin wanan dabian naku Allah kuma ya shirye ku ku gane gaskiya.
Ta juya ta debi arish a plate ta zauna ta fara ci ni kuma ina ta shirina nace kiyi ki gama gada ki makarar dani anan don banson in makara.
Tayi murmushi tana kai abinci a bakin ta sai da ta hade tace wanan halin naki na ina kika fito karatu ina zaki karatu sai ke khadija.
Khady look at you me kika rasa ke kanki jarin kanki ne amma kin tsaya kina wahal da kanki haka har kina wani girki tunda safe kamar wata matar aure amma waike nacin karatu sai wahala kike haka.
Wallahi da zaki yarda akwai wanda zan hada ki dashi cikin kwana biyu kiyi clean ke baki daukan misali a kwaina khady da haka nake ?
Amma yanzu gani tunda hanya ya bude min mai na rasa na rayuwa atare da ni amma ke gaki da abin kawo kudi kina ta faman kumshe shi a jikin ki ta fada tana dariyan shakiyanci.
Ni dai ina tsaye ina mata kallon mamaki da huduban shedan da take min har kuryan dakina ta dauka nasihan ta ya na shigana ne ganin yadda na tsaya ina kallon ta.
Tace ina son ki fahimci wani abu tsarin rayuwa yanzu ya canza ki shigo kawai a dama dake yarinya.
Nace cikin murmushi zarah baki fance ni batsarin rayuwa ta daban yake da naki ban sanya ma zuciyana kwadayi ko son jin dadi a ko wani irin yanayi ba don haka kada kiyi tsammanin guntun huduban ki zaiyi tasiri a raina .
Ni da kika ganin nan ina da mutunci na kuma nasan ciwon kaina dana iyayyena kada kiyi tsammanin kananan kwarin da kike bi zasu iya rudana da wani abu.
Shi jin dadi lokaci indan lokaci yayi sai inji amma ba ta hanyar wullakata kai yadda kukeyi din nan ba kema idan da zakiji sharata da kin watsar da wanan rayuwan ki rungumi abinda ya kawo ki Abuja.
Su kansu mazan da kuke bi aida karatun suke amfana yanzu bance maki ban saurayi ko rayuwa ba sai dai in gajarce maki ni indan zanyi mai tsabta da sanin ciwon kai zanyi amma bana kwanan gida irin naku ba.
Baki zarah ta tabe min tana dariya ta saba da nasihana kullun wanda ita a ganin ta ni har yanzu ban waye ba ban san ciwon kaina ba bansan ta kan duniya ba kuma.
Nace keyi dariya amma ni idan zan faso gari ba irin wa yan nan kanana kwari masu gurbata rayuwa zan tsaya dububa ba sai wanda ya san kanshi da mutuncin kanshi.
Ta mike bayan ta gama ci dama ina magana ina kallon agogona ne kada in makara tace ina son ki fahince ni a yanzu ba a samun irin wa yan nan mazan da kike hasashe kinga ko zaki shawa wuya wurin neman su.
A naki ganin ke nan zarah amma muna nan dake zakice na fada maki watarana ta miko min key din ta nace kenan yauma till down zakiyi tace yo may za a fasa kuma.
Ta fita na rufo kofana muka fito tare da ita a titi muka raba hanya tana neman lift ni kuma na nufi cikin makaranta ina mamakin wanan rayuwa da zarah ta daukan ma kanta.
Itama yar minna ce kama na dalilin haduwan mu ke nan da ita don ko a minnan ba unguwa daya muke ba su suna zama a cancaga ne ni kuma muna tsakiyan gari.
Kasancewar mu yan gari daya yasa muka zama kamar yan uwa da ita da farko halin ta mai kyaune kafin idon ta ya bude da bin mazan abuja.
Sai lokacin muka raba hannu da ita amma hakan baisa mun daina kula junan mu ba kamar baya sai dai ban taba yarda naci abinda take samuwa ba daga wurin yawon banzanta ba.
Tun abin na damun ta har yazo ya daina damun ta ta daina ba sai wanan da iyayyen ta suka kulla suka aiko mata yanzun tana ganin tafi karfin shi ita shine ta kawo min inyi amfani dashi.

Tun asuba yake tayar da ita ta tashi tayi sallah amma tana kwance tana barcin ta har yagaji yatayar da ita da karfin tsiya ta zauna tana mustsukan ido alaman barcin bai isheta ba har lokacin yana ganin ta tashine yasa shi fita daga dakin azaton shi zata tashi tayi sallah.
Ya fita zuwa dakin motsa jikin shi da yakeyi duk safe inda kuma yake aje wasu kayan amfanin shi jiya anan yabar wayan shi yana canji ya je ya kwanta yana tunanen rashin son ibadan da batayi.
Ya gama komai na motsa jiki da yakanyi da safe ya wuce zuwa inda wayan shi yake jone ya dauko din ka idan shine sai takwas yake bude waya da safe.
Budan wayan yasa sakon da suka taru mai shigowa ya gane su wanda farko budewa nawa ne ya shigo da farkon.
Mamaki yayi don ba suna sai lamba ga dogon sako kuma da maishi ya turo mashi kamar kada ya karanta tunda baisan mai sakon ba sai kuma wata zuciya tace dashi karanta kaji mana abinda sakon ya kumsa kila mai amfani ne gare ka.
Fara karanta sakon ne yaji ranshi ya baci don ya fahinci inda sakon ya fito don ganin farkon rubutun nawa kamar haka
Mijin buzuwa a zaton ka zaka iya rabani da hajiya mamane ko ka zubar min da mutucina da take gani kayi kuskure wallahi kuma kayi karya don bakina da naka ban fada ma hajiya mama tana gida an mata rasuwa ba.
Ga wanda yasan mutuncinta yasan darajan ta na fadawa shida ya tambaye ni ko ina da labarin su bakai da buzuwa wace bata da daraja da galihu tasa ka zubar da matan ka da yayan ka da kowa naka kana ganin tsohuwar buzuwa tana maka rudi da huduban shedan kullun.
Kai bari ma kaji wallahi wanan buzuwar ta zubar ma da kima da komai naka a idon duniya tunda kiri kiri ta mai dakai mijin hajiya.
Ga mutum har mutum amma baida ta cewa saboda mace macen kuma buzuwa wace bata san Allah how dear you kaida mace bata bari ka zauna dako matar sunnan ka har kake da bakin yi mun hadi a wurin mama, , , ,
Jikin shi har rawa yakeyi da yake karata text din kasa kai kashen rubutun daki ya nufa da sauri da zuman ya shiga yai wanka ya fita ya samu Yusuf shida yaja mashi rene da wullakanci wurin yar karamar yarinya harta iya turo mashi text din banza haka.
Sai yayi magani na a garin sai yasa na raina kaina may nike dashi may nake takama dashi da zan iya yimai cin fuska haka ina aibanta shi shi da matar shi.
Waya ya fada min maganan da sukayi da hajiyan su hajiyan ne zata fada min kowa komai dai may nene sai ya rena min wayo sai na gane banda wayo yau a garin nan duk inda na shige sai ya tononi a cikin garin nan yayi min wulkanci
Sai dai yana shiga dakin su kuma sai bacin ran nashi ya karu ganin Nafisa kwance tana barcin ta hankali kwace rashi ne ya kara baci ya tuna abinda nace a text dina.
Bai san lokacin da ya isa wurin ta yakai mata mugun maka a tsakar bayan ta ba ta mike firgigit tana fadin Samad may nayi maka ?
Tsawa ya daka mata yace wanan abin zai hada ni dake ke sai yaushe ne zaki rike ibada a zuciyar ki ne yaja tsuki ya shige wanka.
Da sauri ya watsa ya fito ranan ya fito bai wani dauki dogon lokaci ba ya shirya ya fita daga gidan koda ta fito ta samu baya gidan.
Tun a mota ya kira Yusuf yana fadin kana inane yanzu?
Gani gidana ya bashi amsa OK kajirani ganin zuwa yanzu gidan yace eh mamaki Yusuf yaji yana tunanen mai zai kawo Samad gidan shi wanan lokacin haka.
Don ka idar shine sai takwas yake fitowa ko takwas da rabi ware hannu yayi alaman shi ya sani ya mike ya shiga wanka kada yai mashi girshi.
Yana shiri ya sake bugo mai waya gashi kofa gidan shi ya fito ya karasa ya fito ya samay shi don ko driver bai fito dashi ba Yusuf din na gani haka ya rufo gidan nashi ya fito ya samay shi.
Anan ya bude mai mota ya shiga yarufe sai ya dauki hanya batare da yasan inda zasu nufa ba sai yaga ya miki mashi wayan shi duban wayan yake da mamaki yake fadin na maye wanan kuma ?
Ka duba mana cewa fuska a daure ya karbi wayan ya fara karantawa a hankali yana sake murmushi ya gaba yana mika mai wayan yace kai amma wanan yarinyar takai jaruma wallahi haduwan zai zama abin shaawa ga mai kallo.
May ne kace yanzun kai baka ga abin jin haushi ba a nan yace ban gani ba sai ma wani abin da na hango na daban tsakanin ka da beauty din.
Yau sai nanu namata ita ba kowa bane a garin nan sai na wullakanta ta a garin nan dariya yayi sosai yace da kaima kan ka wallahi da ka tozarta kan kuwa.
Wai kaiko kaga yadda kukai balain dacewa da yarinyar nan kuwa wallahi ni abin naku burgeni yake yi idan kuna yi har wani dadi nake ji.
May kake nufi ne wai yace abinda idona ya hango min mana a kai saidai fatan alheri amma zancen ka ci mata mutunci bai taso ba ko kaje ka tozartata duk ba wanan a tsakanin ku ko kamanta da hikimar hajiya na hada ka da wanan yarinyar ne ko kana nufin kai baka gane hakan ba.
To bari kaji Khadija itace zata iya fitar dakai daga zargin da ake maka na cewa Nafisa ta gama dakai da cewan da ake saboda ita ka kasa zama da Fati.
Akan wani dalili zata fitar dani ta yaya din zata fitar dani yace muje zuwa nan gaba zaka sani idan lokacin hakan yayi yanzo ina zamu ne kadauko ni tunda safe haka.
Wurin ta zamu in gwada mata ita din ba kowa bace ya kwashe mai da dariya yace ta zama kowan ke nan tunda har zaka iya biye ma shirmay ta na mata.
Bai kara magana ba sai juya kan motar yayi zuwa office din su ya shige bai tsaya jiran Yusuf din ba.
Anan malam musa driver ya tsayar dashi yana fadin yana da magana dashi na siri da yake son suyi a tsakanin su yace da malam sani din wani abu ya faru ne yace eh to sai dai maganan nason siri gaskiya yace dashi babu damuwa kasa may ni a gida da yamma idan mun tashi.
Ga haka suka bar zancen da malam sani din sai dai ya barshi da tunane a zuciyar shi ko akan may yake bukatan kebewa dashi bai sani ba ya san dai abune mai muhinmanci sosai.
Shiko gogan acikin office maganan da sukayi da Yusuf ne yake ta mashi yawo arai wai zata zama mai garkuwa a kan matsalan shi da Fati da Nafisa ta yaya ma haka zai faru .
Nan dai ya watsar da maganan ya ci gaba da aikin dake gaban shi sai dai yanayi yana tuna zancen a zuciyar shi.

Kai tsaye da na fito kamar yadda na saba gidan da muke na nufa yau yawan ci basu da lectures sai karan gida ke tashi ko ina a cikin gida.
Yunwa nake ji don ban tsaya nayi karin kwarai ba da safe sallah nayi sana fara hada tea na nasha sai da na dan huta a wurin na mike ina sauya kayan jikina.
Na saka dan guntun rigan da nake zama a daki dashi gyaran dakin nayi na gyaro ko ina na dakin sai na dora girkin dare don shinkafa da miya nake son yi irin na yan makaranta.
Bayan na gama miya na dora shinkafan na koma na zauna a bakin katifa ina tunane zarah ne ta fado min a rai yau in zan lissafa kwananta biyar bata dawo ba.
Zarah tana daya daga cikin "ya"ya dake cin amanan iyayyen su don babu inda suka rageta don koba a fada ba zarah tafi gata don sati biyu bai shigewa iyayyen ta basu turo mata da sako ba.
Amma duk ta watsar da wanan gatan nata tabi ra,ayin kwadan abin hannun samari wanda ya rufe mata ido a yanzu har yakai ga ta watsar da karatun ta.
Ido na lumshe tare da girgiza kaina ina cewa ubangiji katsare mu ka karemu ya Allah kasa mufi karfin zuciyar mu don yanzu rayuwa abin tsorone .
Sai gata washe gari ta dawo dakina ta nufa don karban key din ta koda ta shige ban sake mata fuska ba daga inda nake kwance ta tambayi key din ta na nuna mata da hannu kawai ta nufi wurin ta dauka.
Harara na bita dashi tana ficewa daga dakin andan jima kadan sai gata ta dawo dakin daga ita sai wani dan guntun tawul da ta daura iya cinyan ta tana tambayana wai ban rage abinci ba in bata.
Wani kallo nayi mata nace inda kika fito gantalin ki kwana da kwanaki baki kici abinci bane acan ?
Tace kin san yanzu wata yayi nisa ba wani abin kirki ake samu ba sai maneji nace sai ki je gaba ki nema ni banyi abinci ba yau.
Ta ce khady yaushe kika fara rowa haka ba halinki bane rowa nace ban dafa ba nace maki ashe karyan iskanci kike yi da zaki dawo kwana da kwanaki hannu empty.
Ta dan tsaya jin ganin ban kulataba ina karatuna sai ta fice min daga dakin dagowa nayi nabita da kallon mai kama da harara har tafice daga dakin.

Bayan ya gama saurare abinda malam sani ya gaya mashi jikin shi ne yayi sanyi karshe yayi mai godiya tare da jaddada mashi kan kada ya fada ma Nafisa komai ya dai saka ido ga alamarin ta kawai.
Bayan fitan shi gidan nine na fado mashi a rai wayana ya kira mun gaisa dayake shi mai son wasa ne nan yajani da wasa wanda bai wuce hiran mijin buzuwa.
Yace gobe dai weekend ne ba shiga aji ke nan nace eh sai dai ina son zan fita zuwa wurin wankin kai don ina son gyaran jiki gobe dai.
Yace ashe shi gyaran ma sai anje wani guri yin shi dariya yaban don irin zolayar shi nace ana mace ba gyara ne yace kwarai kuwa har in ta san kanta.
Karfe nawa zaki ya tambaya nace wuraren goma zan tafi nasan zuwa karfe sha biyu ko da rabi na gama yace da safe banda time da nazo na kaiki sai dai ki fada min sallin din da kike zuwa in duba ki idan na rarage abinda nake yi.
Nace No kabarshi kawai ba wani nisa yake dashi da inda muke ba nagode yace aini nace ki fada min ko nace beauty hair drasses na fada mai layin da yake a saman babban titi.
Munyi sallama ina mamikin halin shi da saurin sabo irin nashi na zauna na tsefe kaina a cikin daren nan don kada in makara in samu mutane a wurin.
Washegari da safe na shirya na isa sallon din ba wasu mutane dayawa don haka nabi layi sai da akawanke min akai min drying din shi kafin su fara min kitso.
Ranan nasha gyara sosai na jiki daidai zan fito sai ga wayan Yusuf shigo yana tambayana ina wurin ko wuce nace an kusa gamawa nan da minti talatin zanbar wurin .
Nakashe wayan akaci gaba da min gyara sai yaba yawan gashina da tsayi suke yi nidai murmushi kawai nake masu ban wani dogon magana da kowa a wurin.
Sun fito daga kubuwa duban fili da sukaje gani a hanyansu na komawa gida yaga Yusuf ya dauki hanya bai iya magana ba yana aiki a system din shi kan shi a duke yake.
Sai dai yasan ba hanyan gida Yusuf ya nufa dasu ba aikin da yakeyi ya dauke mashi hankali a lokacin ganin ya tsaya a bakin wani gyaran jiki na mata yasa shi dago kai yana tambayan shi ina ne nan kuma ?
Kafin ya bashi amsa yaji yana fadi a wayan shi fito gamu a kofa idan an gama maki nace gani tafe na fito tun fitowa na ya hango nice tafe kallon mamaki yake wa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login