Showing 96001 words to 99000 words out of 133935 words

Chapter 33 - Mijin Buzuwa Book One Complete Hausa Novel

27 Oct 2025

276

kikeyi khadija nace wallahi ya tafi yace sai da safen ku tunda anan kuke son kwana indai kula daku naso ce mashi mudake nan wake kula damu ?
Da sauri tace da kin muna tsiya wallahi nan dai muka sake muna ta hiran mu kayan bukin da muka dawo dashi a tare dasu mukai amfani dashi.
Sai hiran buzuwa da Binta ke ta bamu a dakin wanda inda tasan yadda raina yake baci da ta daina bamu labarin abin haushi haka.
Washe gari ma kusan tare dasu muka wuni a hostel din mu sai da yamma muka je gidan tare dasu yiwa sauran yan uwa sallama.
Mommy tace khadija kice bakin naki ne dai wanan irin fresh da sukayo haka wurin ki dan kwana daya da rabi injin dai ba dan abincin naku suka cinye ba.
Shine ya shigo nan ya gan mu kallo daya yai muna ya kawar da kanshi gare mu gaishe shi suke yi yace da alama kunji dadin zama a inda kukaje din ke nan.
Mun dan jima tare dasu mukai masu sallama suka rako mu zamu tafi sai ga driver yace ance ida zamu koma a sauke mu .

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Tun wanan ranan ban sake ji daga gare shi ba ban kuma koma ta kan su ba ina karatuna hankali kwance don komai ina dashi a tare da ni.
Ashe suna da kwana biyu bayan tafiyan bakin shi tafiya ya kama shi nan Nafisa ta tubure akan may zaiyi tafiya yanzu bayan yan buki basu gama tafiya ba.
Idan na zauna may zan maki a gidan ina kudi kika sani na kashe maki wanda ni kai na ban san iyakar shi ba.
Yan uwana sun tafi da takaicin abinda kikai masu a gidan nan bayan sun san da komai nayawa kike kadagi a gidan nan amma kika rufe ido kika hana masu komai da na kawo gidan .
Haka suka tafi da bacin rai a tare dasu don ma mommy mace ce mai tunane da sanin ya kamata ta sa na samo masu abinda zasu koma gida dashi.
Don baki da kunya yanzu zakice ba zan tafi neman kudi ba idan ban fita ina samo kudin nan a zaune kudin da kike kashewa zasu samay mu ko may ?
Tunda ya fara magana bata katse shi ba sai da yakai karshen maganan shi tace ina da sunana kasai abin bukin ?
Baka ce da wasu yan uwa naka zamu raba shi ba idan bakayi ba wa kake son yayi min da ?
Tafiya kuma kana nufin ni kadai zaka bari da wahalan dubar yar ka ko may tare muka samay ta don haka tare dakai zamu rene ta babu inda zaka a yanzu kaji na fada maka.
Yace tunda ke kika ajeni sai ki hanani zuwa mugani idan zaman ki nake yi ba ke ke zama na ba a gidan nan Nafisa kin dauki kanki ki kai inda Allah bai kaiki ba fa.
A da ana fadin ina ganin don ba a kaunar ki cikin mu ne yasa ake maki haka ashe halin ki ne hakan ban sani ba ina jiye maki ranan da reshen ki zai juye maki a gidan nan idan har baki nemi shiri da yan uwana ba.
Tace wanan tunane kake a ranka dama akwai wani rana da zaizo min ba daidai ba gidan nan har in neme shiri da yan uwan ka to kasani babu wanan ranan a rayuwana da zan shirya da yan uwanka.
Tunda tun farko sun iya nuna min rashin kaunar su gare ni yanzu may zai sa in dawo ina shiri da mutanen da basu so na ko kadan.
Yace aike baki da kunyan fadin magana wani irin sone basu nuna maki ba da kika zo gidan nan musanman ma mommy amma kikai fatali da kowa don ke kan ki kawai kika sani .
Ya ture ta gefe ya fita rai bace zuwa inda ake neman su dan bayanin tafiyan su ta tsaya tana kallon shi cikin mamaki.
Don dai malamin ta yace da ita yanzu AA a tafin hannun ta yake saboda sun gama daure mata shi yadda take so kuma ba karamin kudi ta tura wurin yin wanan aikin ba.
Shiko bayan ya fita daga gidan rai bace bai tsaya ko ina ba sai inda club din millonear in the world yake ya cika komai da zai cika na tafiyan shi kasan.
Take a nan wurin suka maida mashi da amsa sakon shi ya karbu sai kudin da zaiyi tafiya da na komai suka turo mai yana barin haraban wurin ya wuce wurin Yusuf kai tsaye.
Ya samu Yusuf wajen gidan yana shan iska taee da waya a hannun shi yana yi wuri ya samu ya zauna daga gefen shi ya tsiyaya lemon da yagani wajen yana sha.
Yayi mamaki daya fahinci Yusuf da mace yake wayan yana kashe murya tare da zuba soyayya baki ya tabe ya kawar da kan shi gefe yana jiran ya gama wayan.
Ya gama yana kallon shi fuskan shi dauke da murmushi yace ya dai ina ka fito yanzu haka sai da ya dauki cup din juice din ya kara korawa yake fada mai inda ya fito.
Yace amma kasan may wai ni yar rainin wayon nan zata raina ma hankali wai bata yarda inyi tafiya yanzu ba.
Nafisa ke nan Yusuf ya fada yace ai kaima ka sani wazaiyi wanan haukan idan ba ita ba yusuf yace wai may matar nan ta dauki kanta ne halan ?
Komay ta dauka zan bata mamaki ai kwanannan kuwa don sai ta rena kanta wallahi yusuf yayi saurin fadin baka iyawa ne ai shiya sa take kawo maka raini haka.
Haka kake gani ko kamar yadda kowa yake dauka na ban iya aiwatar da komai akan nafisa yanzu kaima hakan ka dauko ke nan ?
Yusuf yace ai haka din ne yanzu fa don haihuwa kai mata wanan irin sayayan haka bayan wanda ka din ka mata wanda zata fita dashi ga kuma sayayya kamar na hauka da ka da mata daga baya.
Wanan ba komai bane Yusuf har in zatai amfani dashi ni mutum ne mai son in ga iyalina suna shiga suna fita a gida don haka ban jin kyashin kashe ma iyalina na kudi ko nawa ne.
Kasan wanan halin ne ya hadani da Fati bata sawa bata kuma gyarawa amma mutane basu ganewa ida matsalan mu yake da ita.
Mutum ko yaushe baka gane dadin ran shi kullun ya zauna kamar an mashi wani abu babu marmari ko kadan.
Ita nafisa tana maka yadda kake so ne halan da ita da fatin duk jirgi daya ya kwasosu a gidan banbanci dai kace ita nafisa tana sakewa da kai kawai ne.
Yanzu badon yarinyar nan khadija da ta muka saya ma yara da ita fatin kaya ba a kwanaki ina ban dashi tunda suka tafi har yau bakai tunanen ka kara saya masu komai ba.
Yarinya ta dauko saka ka a hanya tanayi hanyar alheri wanan bakar shu,umar ta shiga ta fita yanzu ta raba ka da ita nasan wurin shige shigenta can aka bata labarin khadija din ta sani.
Khadija khadiji Yusuf ka fasan tafiyan mu ba zai zo daidai da wanan yarinyar da take daukan kanta wani tsiya ba.
Yasuf yace yanzu ka gama fadi da bakin ka mace yar kwalisa da iya gyaran gida da jiki kake so a gidan ka.
Daga cikin wanan wani khadija ta rasa a tare da ita ka fada min ya ja iska yace baka san wani abu ba wallahi ranan naje dauko su Binta da dare wurin ta.
Kasan yarinyar nan sai da taso ta rikitani gaba daya Yusuf ya tambaya yace akan may kuma yace wallahi wani shegen shiga tayi tafito waje dashi sai da na kasa kallon ta.
Ban san lokacin da nayi mata fadan haka na ba don wanan shigan sai ya rikita mutum a banza wallahi.
Dariya sosai Yusuf yayi mashi har sai da yaji haushin shi yace malam na fada ma son yarinyar nan kake yi wallahi ka tsaya kana wani noke noke.
Bari garin kallon ruwa wani ya rigaka jefa fatsan shi kana kallo dama ya samu ka fida zuciyar ka ka tsaya kana wani izza haka.
Shiru yayi mai yace bazan bata lokaci na ba kan wanan da yanzu ma take zama mace bata gama mallakan hankalin ta ba.
Zaka sha mamaki wallahi khadijan ne macen da bata san wani abu ba idan bata san komai ba yanzu akan may take fushi damu.
Badon share tan da mukayi bane kwana biyu ta dauki wanan zafin haka kana tunanen ita ma bata fada tarkkn son ka bane ko may ?
Kallon Yusuf din yake yi yace abinda take ma fushi ke nan dama yace don may baza tayi fushi ba kuwa ?
Kwana biyu da yin maganan su ya shirya ya tafi club din su inda zai buga game a can .

Banda labarin yayi tafiya sai dai ina murna a raina sun gaji sun barni ke nan tunda ban kara jin labarin su ba kuma.
Sai dai tunanen su yana nan a zuciya na inda nayi wani sabon saurayi dan kabilar nufe koshi haduwan mu dashi a wani shago ne yana waya da yaren su na Nufe sai ya yar da dan wallet din shi kasa.
Da yaren Nufanci da nake ji don zaman gari daya da nufawa da nakeyi nace dashi da yare kayar da wallet din ka fa.
Ya juyo ya dauka yana min godiya a cikin yare yana fadin (Nufe wayyo ni )nace dashi a a ke yar ina ce ya tambaya a cikin yare nace ni yar Niger ce yace (kiyyo sunayo) nace dashi khadija.
Sai yace Iam mamud by name yana aiki ne a CBN dake nan cikin garin Abuja shi mutumin garin Bidda ne dan murmushi nayi don kamar naga na gida ne da na ganshi.
Nomber na ya tambaya na nuna bazan bashi ba ya matsa min sai na bashi da na sai turaren da nazo saye sai gashi mun hade wurin biya ya biya min nafito zan wuce sai gashi yace in zo ya sauke ni.
Banyarda na bishi ba ashe ya biyo ni baya muna sauka shima ya tsaya yana dariya ya fito daga motar shi nan muka tsaya dashi yake fadi ashe karatu ya kawo ki, nan ke nan.
Murmushi nayi nace may yasa ka biyo ni har nan kuma yace don in san zahirin ki tunda kin ki yarda in dauko ki ni kuma ba zan yarda ki bace min ba ina ganin nayi babban kamun yar garin mu haka.
Tun daga wanan ranan muka hade dashi saboda nacin shi dole nasaba dashi don mutum ne mai saurin sabo da mutane ga baa da iya magana kamar shiyayi kan shi.
Tun ranan da suka fara haduwa da maryam tace yanzu kan kin samu daidai dake khadija haduwa da mamud yasa na manta zacen wani AA can a rai na.
Shiko yana can yayi nasaran tafiya don shi yazo na daya ga gasan da sukayi na wanan lokacin ya samo makuden daloli a wanan tafiyan.
Tsaraba yayo wa iyalin daga ciki Allah ya ciyar dani ya sako min a wani jakka na daban tun daga can ya ware min nawa.
Yusuf yazo gurina inda ya samu mamud yazo sai da ya jira ya wuce yana zaune cikin motar yana kallon yadda nake kwasan dariya daga inda nake tsaye.
Yana mamaki a ranshi yaushe har na hadu da mamud har mukai nisa haka dashi muna irin wanan hira don yaga na sake jiki sosai da mamud din.
Mamud ya wuce sai lokacin ya kirani yana fadin gashi nan tsaye bakin hostel din mu yana jirana waige na fara yi sai dai ban ganshi ya fara fada min irin kayan dake jikina da yadda nake tsaye ina waige waige.
Har na gano shi na iso gare shi abinda ya fara tambaya na shine waye wancan danaga ya tafi yanzu khadija ?
Mamaki nayi da tambayan shi nace wani abu ne halan sai yace a yanda naga kuna hira dashi yasa na sha jinin jikina khadija kada fa yayiwa abokina yankan baya.
Kai na rausaya nace wani abikin ka kuma ke nan yayana yace haba khadija tun yanzu har kina nufin kin manta damu ne.
Nace haba dai abokin ka ai ba saurayina bane kuma bai taba cewa yana so na ba asalima shiba irin mazan da nake so bane.
What har akwai irin mazan da mace ke so ashe sai yau naji wanan a bakin ki nace kowa da abinda ke masa kasani .
Yace kina Nufin bai maki ba shikenan ko ko sai wanan dan kyamazon ne yayi maki da sauri nace kada muyi haka dakai yayana.
Yace Allah ganin shi nayi kamar dan tsurut a motar bai wani cika motar tashi ba sosai nace akwai dai kishi ga maganan ka ke nan , ?
Dole muyi kishin ki khadija don kin cancanci hakan a gare mu saboda ke mace wance ko wani namiji yake fatan ya mallaka a gidan shi.
Nayi dariya tare da fadin kazo da wata magana ta daban ke nan idan kai nayi ma ai shi abokin naka ban mashi ba.
Ko ya taba cewa dakai son na yake da gaskiya kaga yayana mu bar wanan zancen muyi wanda ya kawo ka yanzu yace maganan tana cikin abinda ya kawo ni ai.
Bashi ya kawo ka ba kadai zo ne don duba kanwar ka na sani kuma gani ka ganni ai na kuma gode kwarai da gaske.
Khadija ya kira sunana wanda ya nuna maganan da zaiyi tana da muhinmaci sosai a lokacin gare ni amsawa nayi da naam yaya na.
Yace don Allah ki natsu kiyi abinda ya kawo ki garin nan ki bar biyewa irin mutanen nan da suke zuwa da karya.
Nace yayana ban yarda na tsaya da mamud ba sai da nasan ko shi waye da sauri yace dani shi waye din kika sani.
Dariya nayi nace yanzu dai mu bar maganan don Allah don naga bazaka fahince ni ba a yanzu gaba mayi idan mun hadu.
Yace to shike nan tunda kin hada ni da Allah yanzu ina maryam ina son ganin ta nace ayyah maryam yau taje gida da yamman nan gurin yayanta.
Kasan ita anan garin take da zama yayan nata ne tayi tafiya ta dawo shine taje mata sannu da zuwa yace ashe idan Abdulsamad ya dawo zaku zo tarun shi ke nan ?
Da sauri nace da zai tafi ya sallamay ni ne da zanje tarun shi yace kece baki bashi dama ba don kina fushi dashi yasa bai sallamay ki ba.
Wanan maganan kane kana kokarin gyara shi a wuri na ne kawai wanda ba zai taba gyaruwa ba kuwa.
Murmushi yayi yace zan gano ko waye wanan dake shirin hure maki kunne haka har kike son yin wa kanki zaben tumun dare.
Haka dai mukai ta zubawa dashi har ya kaimu wani lokaci a wurin karshe dai yayi min sallama ya tafi.
Maryam ta dawo daga gida tana fushi dani wai naki zuwa gidan su in gaida yayanta da dawowa nace ba haka na bane maryam kina dai gani ba fita nakeyi ba amma kullun Daddy fadan da yake min ke nan in natsu.
Kada ki damu watarana zan tafi mu gaisa da ita har ma in kwana ba shike nan ba haka yasa ta sake jiki dani tana bani labarin yayan nata da abinda ta dawo dashi wanan tafiyan.
Ta ciro wani dogon riga tabani tace yayan nata ne ta sayo muna ni da ita don yawan labarina da take bata ko yaushe.
Nayi godiya tare da karban lanbata nace zan kirata inyi mata godiya tace mutumin ki baizo bane yau nace yayi tafiya ai da yanzu kin gashi nan..
Yusuf dai yazo bakya nan ya gan mu tare da mamud yake wani maganan robish a kan sa tace saboda Allah nace wallahi ko.
Ai dama na fada maki ina jiye maki ranan da zasu san mamud ya shigo rayuwan ki gashi wanan mamud din da alama baizo ba kamar sai da ya shirya maki .
Nace kin jjiki da wani magana kuma ba wani shirin da yai min sone kawai wallahi ni kuma ya kwanta min sosai a raina.
Tunda bada wasa yazo min ba ke ma kin sani idan yau zan ba mamud baki ya fito a shirye yake da yafito din.
Allah ya zaba muna abinda yafi zama Alheri a gare nace amin yama zaba min din Allah sa albarka ya rage kice.

Kwana hudu da maganar mu na dawo daga class don yanzu karatun mu ya dau zafi sosai muyi nisa mun zama manya a cikin makarantan.
Kwance nake ina hutawa ban cire kaysn da na dawo dasu ba wata ta shigo tana fadin wai ina da baki a wajen hostel nayi mamakin ko suwaye ?
Sai lokacin na tuna wayana a kashe yake tunda zan shiga class na kashe wayan mikewa nayi daga kwancen ina gyara bujen jikina dakyau.
Dinkin wasu material ne na india da mijin ya Amina ya sawo muna tsaraba nasa takalmana flats shoes

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login