Showing 51001 words to 54000 words out of 133935 words
alheri a rayuwana ba irin wanan fatan ba na shiga wurin da fitina ta nuna kan ta a fili.
Khadija kin taba ji ko ganin Abdulsamad ya taba bata lokacin shi ga wata mace irin haka amma sai gashi a kanki abubuwa na ta shirin faruwa a tsakanin ku.
Na tabbatar da su hajiya mama zasuyi fari ciki da jin wanan labarin don wata kila adduan su ne ya fada kan ki.
Shiru nayi ina sauraren ta tace abu daya zuwa biyu ne na farko gaba dayan mu sai mu dage da addua gaba dayan mu na biyu kuma kiyi kokari ki cusa mashi so da kaunar ki ta yadda buzuwa ba zata iya mashi gibi ba.
Har muka gama magana ta fita ban iya cewa komai ba ta barni ina cike da tunane a raina na yadda abubuwa ke zo min a haka.
Sai dare sosai suka shiga Abuja inda Yusuf ya aje shi gida ya nufi nashi gidan da motar shi da ya bari gidan don tafiya da ba shiri sukayi.
Ko da yashigo gidan shiru yaji kamar yau mutanen gidan nashi basu ciki bai tsaya falon ba ya haura sama inda dakunan kwanan su yake.
Ga kaya nan ko ina a warwatse ko ina agidan anyi amfani dasu an kasa kawar dasu don tsabagen kiuya da lalaci har ya kai kofan dakin ya tura a hankali ya shiga.
Baiyi mamakin ganin ta a yanayin da ya samay ta ba don duk kwanankin nan a yamutse take a gidan ba wani gyara ko kwaliya da take samun yi .
Tana zaune saman gado gashin kanta a wawatse ba gyara ta dago ido ta kalle shi tare da kallon agogon bangon dake dakin tace Samad ina kafito a wanan lokacin.
Aikena kikayi da kike tambayana ya bata amsa tare da wuce wa wurin wardrobe din shi yana rage kayan jikin shi.
Samad neman mata kafara ko mai yace idan na nemay su ba namiji nake ba wallahi baka isa ba ta fadi da karfi ya juyo gare ta yace ban isa ba fa ki ka ce Nafisa.
Tace baka isa ba wallahi may na rage ka dashi a wanda ban baka da har zaka lakanci neman mata a yanzu daga sama.
Ya ciro wani dogon jallabiya baka yana fadin waya san iyaka Nafisa baki san komai ba banda son kan ki da kashin kudi abaki kuma baki godiya.
Kudi dole ne ka bani don kasan sune buri na kuma akwaisu bathroom ya shiga ya barta ta ta fadin bakaken maganganu gare shi har ya fito bata fasa magana ba.
Gadon ya duba yace duba don Allah wai a inda mutum zai kwanta ke nan ya fara kakabe shimfidar da wani dan karamin towel daya fito dashi daga ban dakin.
Yace mace sai tarin kazanta na fada maki bani son wanan kazantar taki amma ke abin sai gaba yake yi gare ki.
Ai kasan a haka nake kuma ka aure ni na dauka idan kin shigo cikin daula zaki canza ne ashe ni ban san abin a jinin ki yake ba.
Kazantar ne a jina na yake Samad yace in ba ajiin ki yake ba za a ce duk yawan ku baku iya gyaran wuri tace samad wa kake so in sa aiki a cikin gidan nan.
Kafa san daga kanne na sai yayyena anan sai kuma kawu naina da gwago na yace may yasa kika boye min hakan da farko kin fada min yan aiki ne kika samo min kuma biyan su nake duk wata.
Sai yanzu zaki ce min wai yan uwan ki ne na jini baki iya saka su aiki a gidan nan kin zo gidan nan kin samu masu aiki kika ce baki yarda dasu ba.
Na baki go ahead da zaki kawo wanda kika yarda su suyi mana aiki ashe ke yaudarana kikayi ki kwaso yan uwanki kika cika min gida dasu.
Samad ta fada da karfi kawo yan uwana danayi a gidan shi ne kake kira da yaudara yace yaudara ne mana mutum da gidan shi ba dama ya shigo ya huta a ciki yaji dadin ranshi.
Samad yau ni kake fada ma haka don ka gani da ciki kake kokarin ka wulakantani yanzu ko may babu zancen wullakanci sai maganar gaskiya.
Haukace mai tayi ranan tana fadin bai isa ya rabata da yan uwanta ba don tare ya gansu ya kuma yarda ya aureta a hakan.
Haka ya kwana da tarin bakin ciki babu kunya washe gari kuma sai gata ta neman sulhu dashi don dai kawai ya biya mata bukatan ta don bata iya hakkuri dashi duk yadda ranta ya baci dashi ga wasu kudi da take son karba a wurin shi masu yawa don ai mata aiki a kan shi.
Bata samu ko daya ba ranan don asubanci yayi ya fita wirin aiki da wuri koda yaje gurin aikin bai iya aiwatar da komai ba.
Yusuf ya shigo ya samay shi a haka yake tambayan shi wai may ke faruwa dashi ne bai tsaya boye mashi ba ya sanar dashi halin da yake ciki da nafisa a gidan shi.
Da yan uwanta da suka cika maigida da sunan yan aiki ta kwaso yana biyan su a wata ashe ba haka abin yake ba.
Kai inji Yusuf lamarin Nafisa akwai daure kai wallahi Abdul yace nima bashi ba kazantar nan ke damuna Yusuf.
Ka san dai halina da kyakyami wallahi komai na gidan nan yanzu kazantar shi nake ji in ba ruwan gora ba ban iya cin komai a gida na .
Yusuf yaya zanyi da wanan masifa dana dauko ma kaina nasan ina son nafisa sosai why da ba zata gyara halin ta ba may ye ban ma Nafisa a rayuwan ta.
Kamar karta samu cikin nan yanzu abin ya karkare jagule mata mace ba wanka ba saka sutura a jiki idan anyi magana sai tace wai lalurar cikine haka take cikin ta.
Au dama ta taba ciki ke nan naga auren budurwa mukai mata wani kallo ya jefe shi dashi yace Nenan yar waye idan bata taba haihuwa ba nima daga bayan nan na fahinci yar tace ashe.
Yanzun haka zan kare ga yawon restaurant ina cin abinci a garin nan kamar wani mara galihu dani.
Kai innalillahi abin nakune akwai daure kai wallahi saukin abin khadija zata dawo next week zaka dan samu sauki a awurin ta.
Saukin may zan samu a gurin ta ya tambayi Yusuf a yanayin rashin fahintar maganan shi Yusuf yace koba komai tunda ta iya girki naga ai zata dan dinga maka idan tana da time.
No ban san in jefa rayuwan yarinyar ga halaka ko kadan nafi son ayi komai a kaidance yace kana nufin auren ta zakayi.
Shiru yayi ya dafe kanshi bai sake magana ba ya fahinci bai son maganan don haka ya kyale shi tare da canza topic.
Yusuf na fita ya jawo wayan shi ya kira layina muna gida ya Hauwa mai jego ya kira wayana ina wanke kayan miya a kitchen aka kawo min wayan.
Sai da ya kusa katsewa na dauka tare da sallama yace ina kika shiga kika bar waya na ruri haka nace ina kitchen ina girki wa ya hauwa da ta haihu.
Kuna gidan ta ke nan ya tambaya nace eh may kike girka mata nace miyar shuwaka zanyi mata da tuwon shikafa.
Ke wa ya koya maki girki haka ne wai nace girkin ma har sai an koya ma mutum yin shi idai kana mace ai zaka iya girki ko wani iri dole.
Aranshi yace ga macen da ta san kanta ba sai kuma yace ke wace irin yarinyace da baki iya kiran mutane kiji ko sun sauka lafiya ?
Na aiku tafiyan dare ne ko ni na saka ku yin tafiyan da kuyi din yace OK haka zaki ce ma nace haka din ne ma ai.
Sai naji ya kashe wayan dariya nayi nace zaka kaji ai ka daina in yar da magoro in huta da kuda har dare muna gidan sai tara muka dawo gida a gajiye .
Ban kara bi ta kanshi ba har akai bukin suna aka watse lafiya drinks din da suka kawo muna yayi muna rana do shi mukai amfani dashi wurin taron sunan.
Mun fara shiri don tare da yaAmina zamuyi tafiyan kamar yadda na fada mata yace zai turo mota hakan ne ya faru sai ga mota zuwa sha biyun rana ya tsaya a kofan gidan mu.
Nan muka fito mukayi haraman tafiya nasha nashi ha a wurin mama da daddy kafin mu wuce muka dauki hanyar Abuja tare da ita don zata kwana a wurin mu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
INA BUKATAN ADDUAN KU YAN UWA ALLAH YASA MU DACE
Washegari da safe ban tashi da wuri ba don fashin sallah da nakeyi sai da naji motsin daddy ya dawo na fito don in gaida su har lokacin a cikin damuwa nake.
Daddy yana zaune a cikin dan karamin falon mu ga abin karyawa a gaban shi mama tana gefen shi ta motsa mashi kunun da ta aje mai a gaban shi sai kamshi kosai ke tashi a falon.
Daga kofa na tsuguna ina gaida su daddy yace a a baby na shigo mana daga ciki na tashi na karasa shigowa cikin falo har lokacin na kasa sakin jiki dasu kamar kullun.
Daddy yace ya karatu nace daddy Alhamdullah yace babu matsalan komai ko nace daddy ba matsalan komai na fada tare da sunkuyar da kaina kasa.
Ina kokarin mai da hawayen da ya ke shirin silalowa a idona nace daddy sai dai wanan mutumin da ya hado ni da kayan nan wallahi ban san ya sakasu a mota ba sai da muka zo nan taimakon shi nayi shine ya saka min da haka.
Ido duk kan su suka tsura min da nake masu bayanin daddy yana kallona yana yaba hankalina don yasan ba zan boye masu komai dake faruwa ba.
Saboda karya ba halina bane kai tsaye nake fadin gaskiya ga mutum yace dakata khadija kin mashi alheri kin shirya shi da iyayyen shi.
Shi kuma yaji dadin hakan ya saka maki da alheri ko kamar yadda yace na gyada kai nace hakane daddy.
Mama tace ina kika hadu dashi haka khadija nace mama a wurin da aka tura mu aiki ne na hadu dashi ya samu matsala da iyayyen shi da yan uwanshi.
Shine na basu shawara ya nemi shiri da yan uwanshi da mahaifar shi ta hanyar aikata masu alheri daya jaraba hakan sai suka shirya dashi.
Shine yazo yace zai saka min da alheri akan abinda nayi mashi tace khadija shine ya kashe maki wanan uban kudin daga taimako kawai irin haka ?
Nace mama wallahi ni ban san haka zai min ba daga ta Hussai yace ma mama kin san ni ya kamata in dauki zafi akan maganan nan fiye da kowa.
Amma sanin halin ya ta danayi yasa na yarda da bayanin mutumin nan tunda ya rantse min da bata roke shi ba kuma ba da wani manufa yayi mata haka ba.
Yai min bayanin da hankalina ya sa na yarda dashi da ita sai dai yanzu ba yadda muka iya tunda kayan nan sun riga sun shigo gidan nan.
Kiga ba komawa zasu yi ba tunda dai ba rokon shi tayi ba sai dai khadija a gaskiya nayi mamaki da wanan abin don ba karamin kudi ya kashe ba ga kayan abincin nan.
Da sauri nace daddy ba kayan abinci bane kawai har da na sakawa da kudi sune a cikin wanan akwatin da ga gani jiya.
Ido maman mu ta fitar waje tace khadija anya ba dan yankan kai bane kika hadu dashi kada fa watarana ya gama zolayar ki da abinduniya mu nemiki mu rasa.
Dariya maganan ta yaso bani sai na dake nace mama ba dan yankar kai bane don nasan kowa nasa na kuma san matar shi.
Share kawai duk wanan tunanen nayi shi a daren jiya har nafila sai da nayi akai banga wani abin cuta ba daga gare shi sai tarin alheri da na hango ga wanan alamarin.
Shiyasa kika ga ban wani damu ba da hakan sai da ita din ta kula da kanta da mutuncin ta da irin tarbiyar da mukai mata zan sake yin yau na gani don ni kaina abin ya daure min kai sosai.
Mikewa nayi na dauko kudin da kayan na turo zuwa dakin nan na fara fitarwa ina masu bayani yadda kayan suke nima mamakin yawan kayan nake yi a cikin macewa jiki.
Daddy yace aje kayan zamuyi sai na nemi yar uwarki a waya naji shawaranta akai da yadda za ayi da kayan.
Zan dage da rokon Allah don ina jiba jikina kamar akwai alheri ga haduwan khadija da wanan mutumin sai dai mu bar ma Allah sanin shi.
Koda yakira ya Amina yayi mata bayanin abinda na dawo dashi wanan karon tare da fadin ta sake binkice na tsakani na da wanan mutumin don a gono gaskiyar maganan.
Ta kira ni lokacin ina kwance mara na yana damu na da ciwo na dauki wayan ina gaida ita bata tsaya amsawa ba sai cewa tayi Deeda make faruwa ne daddy ya kirani yana fada min wani magana da safen nan.
Shiru nayi sai da ta kara maimaita maganan ta nace cikin kuka wallahi ya Amina ba halina da kuka sani da na canza yanzu.
Nima ban san da kayan nan ba sai da muka shigo garin nan na gani nan dai na koro mata bayanin komai don ba zan iya boye mata ba ita.
Tace khadija kina nufin dama Abdulsamad ne ya yi maki wanan alherin ban sani ba khadija baki jin tsoron buzuwa ta san wanan labarin ta yi maki illar nace ya Amina yaya zanyi ni ban roke shi ba shiya bani.
Tace dama khadija kece kika saka yayi wanan alherin da yayiwa iyayyen shi ashe dama duk kece sanadi ni ba komai nake ji wa ba sai buzuwan matar nan tashi wallahi.
Takira daddy tayi mai bayanin komai yace shi zancen buzuwan matar shi bai damay su ba tunda ta sheda ba mugu bane.
Nema ne idan naga zan iya sai in yi dashi wanan ba komai bane Allah yasan abinda ya hada a tsakanin mu ya kawo hakan sai dai mu saka ido a kan yar mu don har yanzu khadija yarinyar ce karama.
Ya Amina tace gaskiya ne daddy zan shigo kafin ta koma dayardan Allah anan suka rufe maganan tare da taya ni addua ga wanan lamari tunda daddy yace abarwa Allah sanin shi a tsakanin mu.
Maryam ta kirani nake mata bayanin abinda ya faru dani maimakon ta tayani jimamay sai naji tana min dariyan shakiyancin da ta saba min tace shike nan ya nuna maki wayon manya ya gabatar da kan shi ke nan gare su.
Nace wai ke maryam don Allah may yasa kike irin haka ne sai a na maganan gaskiya sai ki dauko wani zance daban tace shike nan yanzu mubar zancen a haka dai.
Nace zai fi sauki muka dauko maganan karatu bayan mun gama wayan ne barci ya dauke ni a wurin wanda nasan barcin da ban samu bane a daren jiya.
Nan dai na kwashi barci na sosai a ranan sai wani lokaci na tashi don mama taki sake min fuska yasa ban son fita a tsakar gidan sam.
Wayana yayi kara na dauka Dan Baiwa nagani a rubuce wani haushin shine ya kamani a raina nayi banza da wayan nashi bandaga ba har kiran ya katse.
Ya sake kirana da kyat na iya daga wayan don har yanzu ina fama da ciwon mara dake cina jin murya na da yayi yasa shi saurin fadin.
May ya samay ki baki da lafiya ne may ke damun ki ne khadija haka yadda naga ya rude ne nace banda lafiya ne .
Tun yaushe nace tunda safe daddy na gida naji ya tambaya nace yana waje turo min da layin shi may zakayi da layin shi nace dashi.
Ban number shi nace maki ya fada a dake nace ban san number shi OK zan kira a bani number yar ki in karba a gurin ta yace da sauri nace a a din Allah ni dai kada ka kirata naji sauki.
Dole na bashi layin daddy din don naga yana niyar kashe wayan bayan na bashine ya kashe wayan bai fi minti goma ba sai ga daddy ya shigo gidan yana fadin ina khadijan take ne wai ashe bata da lafiya bamu sani ba.
Sai da wanan yaron ya kirani yanzu yake fada min khadija bata da lafiya a kaita asibiti wai zai turo da kudi kamar shine ya haife ta.
Mama tace ni tunda jiya da ta dawo na ganta kwance ban san may ke damun ta ba, har dakina daddy ya shigo ya samay ni kwance sai dai ba barci nake yi ba.
Zama yayi saman tsohowar kujeran dake falon yana fuskanta na yaga yar raman da nayi yace baby na may ke damun ki ne yanzu wanan mutumin ya kirani wai baki da lafiya.
Sai dai ban san ida ma yasamo lambata ba ya kira nace niyace in bashi na