Showing 21001 words to 24000 words out of 133935 words
Madam tace kash aike kinji matsalan ki ke da zaki bishi da lalama ki nuna mai ba wata mace sai ke a duniya daga baya sai mu sake shirya wa tace.
Madam idona ya rufe a lokacin da kishin ganin wanan yarinyar a kusa dashi amma da ya fahintar dani shi irin su ba su gaban shi shi yanzu wace mace zai kalla ta bashi sha,awa sai naji hankalina ya dan kwanta a lokacin.
Madam tace amma kin so ki bada mu wallahi kai kin ma dai kwafasa wallahi yanzu ke ko irin matan abujan nan ya lalubu maki har ki ta da hankalin ki haka mudake da wuka a hannun mu nama kawai muke jira.
Kawai yanzu idan ya dawo kije ki bashi hakkuri akan abinda kikai mai din don kada ya zarge wani abu a gare ki.
Kin ga zaki ji a bakin shi ko ita wanan yarinyar wacece a garesu kin dai san yadda zaki bugi cikin shi ai muji komai a saukake.
Tace zanyi kamar yadda kika ce din amma ba yanzu ba zan dai saka ido in gani idan suna tare ko basu tare sai musan abinda zamuyi daga baya.
Sun dauki lokaci suna maganan akaina ana ta kulla sheri da tugu akan mazajen su kafin suyi sallama madam tace zata kira zuwa gobe taji indan da wani matsala kuma.
Na gama shiga da komai daki na da taimakon wata yar gidan namu da ta dawo tagan ni da kaya ta tsaya taimaka min.
Kayan jikina na fara cirewa san nan na fara gyara kayan ina aje komai a inda nake bukatan shi na gama na zauna ina tunane a raina.
Bakomai nake tunane ba sai mijin buzuwa da Allah ya jefo a rayuwana a dan lokaci ya taimaka min yau gani da kudi a hannu na wanda yakai dubu dari ta dalilin mijin buxuwa da iyayyen shi duk na samay su.
Waya na dako a cikin handbag dina ina neman layin ya Amina don in fada mata abinda ya faru don komai ya faru dama nakan kirata in fada mata.
Kira uku ta daga wayan ina ji bata kusa da wayan ne a lokacin mun gaisa nake tambayan yaranta tace suna lafiya sun tafi islamiya.
Nace anty kin san wani abu da ya faru yau tace ina zan sani Khady nidake kaduna zaune kina abuja ke.
Nace anty yau na hadu da mijin buzuwa danaje sayayya tace kun sake haduwa kuma again nace wallahi anty wai duk wanan uban kayan da na sawo nazo biya sai ake ce min ai ya biya bayan da suka sauke ni ranan ya ba driver dubu hamsim ya bani.
Kai da gaske khadija nace wallahi anty kuma su suka kaini gida sai dai shi bai so su dauke ni ba sai abukin shi ne yace saboda mama ne suke min haka.
Dariya tayi tace to Allah ya saka da alheri ki dai bi a hankali inda duk kuka hadu don buzuwan nan ba imani ke gare ta tana iya komai akan mijin ta.
Ya Amina ni inama zan kara ganin shi kuma Allah dai ya tsaga rabona daga Aljihun shi wanan karon mutumin da ko yaushe take a cikin hade fuska banda gaisuwa may zai hada ni dashi kuma.
Daga haka muka kawar da zancen shi muka dauko na iyayyen take fada min cewa sunyi waya da baba yana fada mata kudin su na ritaya ya kusa fitowa kwanan nan.
Ihun jin dadi nayi don murnan iyayyen mu zasu fita acikin hali talaucin da suka shiga na ritayan da mahaifin namu yayi muke cikin halin kaka nakayi.
Tace ai zan riga ki ji idan kudin sun sauka don haka sai abinda kika samu daga baya nace ai ni indai daddy zai samu bukata na ya biya ke nan.
Yanzun ma shawara nakeyi inje banki gobe in tura mai kudin da mijin buzuwa ya bani don akwai kudaden da zasu isheni a hannu na tunda ina da abinci waddatace .
Tace haka akeso mutum idan ya samu ya tuna da iyayyen shi dama dako kin kyauta wallahi dama sallaman ki ya hanani tura mashi kudi wanan watan.
Haka dai mukai ta hira da ita daga karshe mukayi sallama na kashe wayan tare da mikewa na jona electric dina don in dafa dan abinda zanci da dare.
Kira, a na saka a wayana ina aiki ina bin kira a don ni gwanace a wurin iya hadda tun ina yar shekara sha hudu na sauke alkurani mai girma na sake maimaitawa yakai kashi uku yanzu don duk wanda yasan yaran minna ya sansu da ibada da kamun kai ga girmama na gaba dasu a duk inda suke.
Da wanan halin namu nake shiga ran mutane farat daya kowa tsakani na dashi gaisuwa ne na mutunci da sani girman wanda ya girmay mun.
Na gama na zuba a plate na dauko ledan ruwa guda cikin wanda na sayo na aje a dakin na zauna don in fara cin abincin sai ga kiran waya ya shigo min.
Binta ce ta kirani a lokacin na dauka kafin wayan ya tsunke hiran mukayi sosai ranan da ita har nake mamakin ko nawa ta sa awayan ta haka don da mun sake wanan hiran take dauko min wani.
Har take fada min yadda akayi ranan da zamu wuto da buzuwar yayan su tace bazata shiga mota dani ba mama ta dage daya zo mata da maganan kan lalai sai sun tafi dani.
Nace kin ko ga tunda muka kama hanya batai min magana ba nima ban masu ba daga ita har mijin ta.
Tace wanan ai dama shi miskili ne magana kamar aiki yake ganin sa a gare shi zai iya zama da kai kuyi awa daya baice uffan ba haka kuma matar shi anty fati itama take shiru shiru bata magana.
Nace aiyanzu sun samu mai magana a tsakanin su haka yasa ta samu daman musguna mata yadda take so ai.
Tace ke kin ko san halin wanan matar shu,uma ce wallahi ta karshi da farko da tazo boye halin ta tayi kamar wata mutumiyar kwarai da ita.
Sai daga bayane ta fitar da kalar ta kowa ya sani bata kaunan ko dan uwan yaya ta ganshi a gidan nan wallahi.
Nace wuri ta samu wallahi ni kar nake kallon ta don banga abin tsoro ba anan ku dai na fahince ku kuna bata girma ne don mijin ta yana da hali a cikin ku.
Tace ga tsiya nace eh mana haka din ne amma in bashi ba ta yaya zaku zauna wanan matar ta dinga raina maku hakali har tace wai idan tana wuri kada ayi dariya .
Tace ina ma kika sani khadija ai sai wani lokaci da mukaje hutu wurin su a abuja ba girma muka dawo gida kwanan mu biyar ko sati bamu kai ba matsi yai muna yawa a gidan.
Muka matsa ma yaya zamu dawo ga yan uwanta nan muna ganin yadda take ji dasu amma mu ko falo ta hana mu fito muka koma kamar wasu bare ba yan uwan maigidan ba.
Dariya nake mata sosai tace Allah ko magana mai karfi wai ba ai mata a gida tace ba kallo ba komai sai zagi da hattara ga anty Fati damu da ita duk muka koma daya.
Bayan mun dawo sai ga anty Fati ma ta dawo wai a kaduna zata zauna bata iya zama da buzuwa a abuja bata bari ko miji ta gani idan yana gida.
Nace ke ki bari don Allah ashe ba karamar shuuma bace tace baki santa bane Khady wanan fa ko kashe mutu tana iyawa fa.
Nace wanda Allah yabata ikon kashewa ba wani kan ai yafi karfin ta wallahi ba abinda zata iya wanda Allah bai tashi yi da bawan shi ba.
Ni don Allah har kin ban haushi da wanan maganan naki don ba a gidan ku nake ba wallahi da taga tsiya a guri na nifa irin matan barikin nan haushi irin su nake ji.
Zako kiji nata don bata da hali mai kyau ko kadan akan mijin ta zata iya yiwa mutum komai musan man ma ce ko waya tayi da wata ranan sai sunyi jidali sosai da ita ke ta zama mai kaya ko shi yanzu bai da yadda zaiyi da ita ne kawai wallahi.
Nace ya dai ga dama ne Binta idan ka ganshi ga mutum har mutum amma baida kuzari gun mace tir yayan ku ya zama mijin hajiya wallahi.
Haushin abinda na fadi taji da fada muka karasa wayan a rana na kashe ina mata dariyan shakiyanci na gama na wanke kayan na samu wuri na kwanta.
Washe gari da wuri na fita don ban yarda in makara in ba wani dalili ya tsayar dani ba mai karfi shi kadai zai sani makara kawai.
Ban da yawan kawaye sai mutum biyu yan department din mu kosu shirin mu dasu don sun ga nafisu kawo wuta sosai a class din shine likewan su dani.
Banda wasa ga abinda ya kaini abujan daga school sai gidan mu sai ko idan wani dalili zai sa na fita a ranan zan fita.
Yau ya dawo a gajiye don daga wurin aiki ya wuce wuri wasan polo da suke yi don dan wasan ni ne sosai wanda yana daya daga cikin abinda ke kawo mashi kudi a lokacin bai dogara ga aikin shi ba yana buga buga irin na maza gida da waje shike sa yana samun mahaukacin kudin da yake riko.
Wanka yayi yana saka kaya a jikin shi ta shigo dakin dan juyawa yayi ya kalle ta ya kawar da kan shi yaci gaba da abinda yake yi.
Karaso wa tayi gare shi tana wani rangaji na daukan hankalin shi ta sake abinda yake so ya sauko mata har mazaunan ta.
Cike da sallo ta iso gare shi sai dai tsiyan shi da ita duk gayun ta bata damu da saka kamshi ba kuma har yanzu ba gwanewa tayi ba da iya kwalliya shine ma yake kokarin wurin gyara mata idan tayi wani kwaliyan zasu fita.
Gata da son karya sai dai ko bokon kasar su bata samu ba kuma babu na Allah a tare da ita abin ya taru yai mata yawa amma hakan bai hana shi son abin shi ba.
Rungumoshi tayi ta bayan shi ya sauke wani ajiyan zuciya yana dan murmushin jin dadin ganin ta tace yau ina ka shige haka ne ta dawo ta gaban shi suna fuskantar juna.
Bai ce komai ba yadan jajeyeta ya dauko turare yana fesa ma jikin shi tace har da daren ma sai an feshe jiki da turare ko fita zakayi ne haka ?
Sai lokacin yayi magana yace sai zan fita ne zan saka kamshi a jiki na ke baki son kamshine ashe yasa baki sakawa .
Taji zafin maganan amma ta daure don in da sabo ta saba da gorin saka kamshin da yake mata din ko yaushe kuma hakan bai sa ta saba da sakawa ba.
Tace muje kaci abinci yace na koshi ta dubeshi da sauri tace tare da fadin ban gane ba yace mun ci abinci da Yusuf kafin in dawo.
Juyawa yayi ya nufi saman gadon su yana jawo laptop din shi tasan idan ya fara dakilan laptop sai ranta ya baci kafin ya gama.
Idan tayi magana kuma yace business yake a ciki shi ko wani abin dariya tayi ya dago yana duban ta na lafiyan ki kalau kuwa ?
Sai yaji tace maganan turaren da kayi ne dai yaban dariya har na tuna da yarinyar da mama ta saka mu dauko ranan.
Bakaji wani irin kamshi tiraren da takeyi ba kamar tayi wanka dashi yace tasan kan ta ne yasa ta saka turaren haka don kada a raina ta.
Tace shi saka turare kuma har wani sanin kai ne dashi wai ma may ye alakan ta da mama ne data nace sai mu dauko ta wai ?
Yana bude laptop din yace sai yanzu kike son jin halakan su da mama da kishi ya rufe maki ido baki tsaya tambayan ta ba da farko.
Tace kayi hakkuri cikin yanayin tausasa harshe tace nasan ban kyauta ba kishin ganin ka kusa da wata mace nakeyi tundai irin wanan yarinyar dake cikin ganuwan kurciyan ta ga kyau kuma da gani tana kuri da ilimin ta.
Ina tsoron ka hango kyawon tane wallahi kazo kace zaka dauko min ita a gidan nan wata rana son ka nake har karshen zuciya ta ka sani.
Ya tsaya yana mata wani irin kallo yace don kina kishina sai ki min hauka mata nawa nake gani a rana da ina raayin mata ne zaki san lokacin da zan nemay su ne.
Har kina fada min cewa mahaifiya ta da biyu ta hadamu tafiya da yarinyar don in so ta kika haukace har kina fashe fashe a gida.
Kwantowa tayi a jikin shi ta dan shafi kan shi tace kai min afuwa don Allah haka ba zai sake faruwa ba a tsakanin mu.
Yaji hakkurin da ta bashi har cikin ranshi yace ki rage kishin nan nake don ni din mijin mace hudu ne watarana.
Da sauri ta rufe mai baki tana fadin don Allah ka daina fadin haka don kana sa zuciya ta tana bugawa da wanan zancen kishiyar da kake min.
Yace idan lokaci yayi ai yi zanyi sai dai ki tausasa zuciyar nan naki bakiga mahaifina matan shi hudu ba kin sani ko in gado shi nima ?
Kuka ta soma mashi tana fitar da hawayen munafunci a idon ta dariya yayi mata yace akan kishiya kike wanan kukan haka fati fa ba kishiyar ki bace kin ga ai ko yanzu kina da ita ke nan.
A bar maganan Fati tace don ni kaina ma kunya nakeji ace wai ita din kishiya ta ce balle kai ace matar ka ce Fati ta sunna.
Ohh kin fison indan zai ne ma yanzu in nemo wace idon ta ya bude sosai don itace ta dace dani tace ba haka nake nufi ba don Allah mu bar zancen kishiyan nan haka na.
Tambayan ka nayi cewa wacece wanan yarinyar ne sai ka dauko min wani dogon zance kuma akan kishiya ?
Yace nima ban san ta ba a gurin mama wanan zuwan da nayi na fara gani ta koma waye dai ita nasan alakar ta da mama mai muhinmaci ne sosai.
Shiru tayi tana nazarin maganan shi daga karshe dai data ga ya fara aikin shi ta kwanta tana ci gaba da tunane kala kala a zuciyar ta.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Bayan mun gama waya da ita naji raina ya baci sai a lokacin na gode ma Allah da ban goge number shi ba a wayana kira nayi har sau biyu bai daga ba sai na tura mashi sako masu zafi na kashe wayan.
Don nasan zai gani da safe in ma kwanciya yayi a lokacin haka yasa na danji zafin da nake ji ya rage min da kyat barci ya dauke ni a ranan.
Har na rufe ido sai nayi wayana yana kara na dauka a zatona shine yaga sakona ya kira wayan sai dai ba number daya kirani daya kira dashi bane.
Nace ummhumm ina jin ka naji ance haka ake karba kiran wanda baka sani ba na sheda muryan Yusuf din nace yayana kaine a na dauka wani ne.
Yace nice injin ruwa bai saki jin zazzabi ba dariya nayi nace ai na watsa ruwan zafi a jikina yace good dama na kiraki ne don mutumin ki ya karbi number ki a hannu na nasan zai iya kiranki kada ki biye ma halinshi don Allah don bansan abinda zai kiraki ya fada maki ba koda yake yace akan maganan hajiya mama zai kiraki yaji don Allah , , ,
Na katse shi da fadin ai ya kirani ko har munyi tsiyan shi ya dauka kowa nema yake a gare shi ko yaushe ni kuma na wanke shi tass.
Da karfi naji yace haba don Allah nace wallahi na kwashe komai na fada mai har text din da na tura mai mai zafi yace amma baki kyauta ba wallahi.
Nace saboda may zai mun hadi yace khadija kin san kuwa kece mukee son kizama weapon din mu wurin yakan buzuwa nan gaba.
Don Allah ki dinga sausautar harshen ki gare shi nace wa ni ni ina ruwa da shi da zan zama muku makami a gare shi da buzuwan shi.
Dariya yayi yace ke ko ke dashi khadija ke da komai da zaki yakar muna buzuwa don kin cancanci yin hakan.
Ni din yayana yace kwarai kuwa kauna na sai dai idan mun hadu zan maki bayani yadda zaki gane nace to shike nan tunda haka ka fada yace bani na fada ba umurni nima aka bani kan hakan .
Yace sai dai idan mun hadu din zan maki bayanin komai nace Allah ya kaimu ina saurarenka da haka muka yi sallama dashi ya barni da tulin tunane a zuciyana.
Da safe zarah ce take buga min kofa jin bugun kofan na tashi na bude daki tana tsaye kofan dakin nawa ganin tana son shigowa na bata hanya ta shiga daga ciki.
Tambaya na tayi ko da safe zan fita nace ai kemakin sani yanzu haka shiri nakeyi kada