Showing 36001 words to 39000 words out of 133935 words

Chapter 13 - Mijin Buzuwa Book One Complete Hausa Novel

27 Oct 2025

230

dauka kuma gani a kofan ku ya fada kawai.
Kofan mu na maimaita da mamaki nace may kazo yi a nan kuma ban sani ba yace idan zaki fito ki fito sai ya kashe wayan kawai.
Tsaki nayi na wurgar da wayan tare da fadin dan wahala kawai maryam dake zaune ta tsura min ido tana kallo na murmushi tayi tace.
Uhm wani lucky guy din ne yazo haka ake ja mashi aji kuma abinda wasu ke nema ido rufe a zo gurin su anzo kike wanan masifa haka ?
Nace sister kin faye bin kwakwafi wanan fa ba masoyi na bane zuwa kawai yayi ya bata min lokaci na ina zaune kalau.
Don Allah ko may ya kawo shi kije ki saurare shi ba dadi mutum yazo wurin don ka ka wullakanta shi haka muje in zaba maki kayan da zaki saka in maki rakiya.
Dole na mike muka tafi dakina ita da kanta ta zaba mi wani dogon riga mai ruwan ganye da dan karamin gyale shi sai da na shirya tsab a cikin rigan tabi jikina ta feshe da turararuka masu kamshi muka rufo kofan muka fito tare.
Yana zaune a cikin motar shi riga da wandon shadace mai guntun hannu rigar ma iya ciya dinkin yake light green kayan su matukar karban jikin shi da dinkin .
Wurin dirkekiyar motar shi da ke fake a kofan can dan nesa kadan damu muka nufa ko ganin maryam ya hana shi fada ban sani ba sai cewan da yayi.
Ita ko maryam tunane take a ranta ina tasan fuskan nan nashi ne ya katse mu da cewa kin san ina waje zaki shanyani a wanan wurin naku mai kazantar tsiya haka ?
Nayi dan dariya tare da cewa cikin wayance abinda yafa da nace ga kawata maryam tazo gaida kai don ma ita ta matsa min in fito yanzun haka.
Anyway maryam ga yayan mu Abdulsamad Abdulrahim nan ku gaisa tace dama nace kamar nasan fuskan nan ai tace ina wuni yayan mu anzo lafiya yaya iyali.
Yace lafiya kalau yaya karatu koda yake exam kukeyi yanzu ko yana wani kauda kai yana basarwa .
Tace karatu Alhamdullahi mun kusa cin ma karshen shi da yardan Allah ai a huta gajiya dama nace barin zo mu gaisa ne kawai yace to na gode kwarai da alama kin fi kawar taki kirki sosai.
Dariya tayi tace a a wallahi ai kirkin khadija na daban ne wallahi tana da kiki matuka shiyasa ma nake jin dadin zama da ita wallahi.
Baki ya tabe ta juya ta tafi tana mashi a huta gajiya ta nufi hanyan shiga hostel din namu sai lokacin na sauke ajiyan zuciya bayan tafiyan ta.
Katse ni yayi da fadin tsaye zaki min sai kace wanda tazo tadi da buduruwar shi haka bude kofan motar shi yayi na zagaya na shiga sai naji ya rufe motar.
Shiru daga ni harshi ba wanda ya iya magana a lokacin sai ma gyara kwanciya yayi a motar bansan lokacin da nace dashi baka da lafiya ne Yaya Samad.
Shiru yayi kamar baiji ni ba sai can yace may kika gani a tare da ni nace yau na ganka so weak ne ba miskilancin nan naka yasa na gane bakajin dadi ko baka cikin good mode.
Wai ke aljana ce ko may dazun kin fada min magana akan ahalina ya zama gaskiya yanzu kuma waya fada maki banjin dadin jikina ?
Nace yanayin ka ya nuna min haka sai ya dago da sauri ya na kallo na nima kallon shi nake yi sai dai ba zan iya jimirin kallon nashi ba a lokacin saboda kwarjin shi da ya cika min fuska a lokaci daya dukar da kaina nayi kasa ina wasa da yan tsun hannu na.
Yau ina bakin naki ya shiga nace ko don Yusuf ne dama kike da bakin a gaban shi nace da sauri ko daya wallahi gani nayi yau kana bukatan kulawa don baka cikin hayacin ka sosai.
Don jikina ya bani baka da lafiya sai naga ya koma ya kwanta kamar yadda yake da farko ya fadi a kasalance cewa kaina kamar zai rabe biyu nake jin shi khadija.
Kasha magani na tambaye shi da sauri yace ban sha ba wani magani kake sha yace panadol extra nakan sha wani lokaci.
Wayana na fara dannawa ina neman layin maryam ta dauka nace fito min da panadol extra din nan da goran ruwa don Allah yaya Samad bai jin dadin jikin shi tace to da sauri na kashe wayan.
Motar shiru ba a dauki lokaci ba sai ga maryam ta iso da maganin ta kwankwasa glass din motar ya bude mata karba nayi ina mata godiya tace babu komai mana Allah ya bashi lafiya.
Maida marfin motar nayi na rufe na fara kokarin bare mashi maganin tare da bude goran ruwan nace mai gashi ka sha.
Ya dago kanshi da kyat ya kalleni ya kalli maganin da ruwan da nake mika mai sai naga ya bude min bakin shi alaman in bashi da kaina .
Dan rankwafawa nayi ina saka mashi maganin a baki na kawo goran ruwan na bashi ya hadiye da kyat yana wani lumshe idonun shi yana bata fuska.
Komawa yayi ya kwanta tare da fadin thanks nace Allah ya baka lafiya amin yace da kyat ni dai komawa nayi na zauna na zuba mai ido.
Wasu irin jijiyoyi naga sun fito rada rada saman goshin nashi wanda ban taba kula ko yana dasu bane dama tsoro ne ya kamani kada wani abu yazo ya samay shi fa a nan wurina nawa ya samay ni kuma.
Shiru daga ni har shi ba wanda yayi magana a cikin mu har mintina na shudewa a hakan suna batun zama awa daya muna nan a hakan dashi kamar mai barci.
Abu daya ne yasa hankalina dan kwantawa ganin yana numfashin shi normal a lokacin yasa nayi shiru tare da zuba mashi ido kawai ina kallon ikon Allah.
Wayan shi dake aje a motan ne ke ringing ganin anata kira bai dauka ba yasa na daga kiran don ba suna batare da na saurari mai magana ba nace mai wayan bai da lafiya please.
Naji muryan mace tana fadin ke wacece da sauri ya dago ya kwace wayan a hannu na ya katse kiran yace akan may zaki daga min waya waya baki wanan damar da ikon daga min kira a wayana.
Zanyi magana yace get out tunda ka samu lafiya yanzu zaka iya ci min mutunci sai dai ka sani ba zan ce ma komai a yanzu ba don yanayin da kake ciki na bukatan natsuwa.
Get out i said na bude motar na fita ba tare da na juya na kalle shi ba naji ya tayar da motar ya jata da karfi yabar gurin nashige ciki abina.
Dakina na shiga na wurgar da sauran maganin saman katifana na fara kokarin cire kaya a jikina sai ga maryam ta shigo tace ashe kin dawo.
Eh ya tafi ya samu lafiya ai nace mata ina daura zanin a jikina na nike kayan na za saman jakkunan kayana dake gefe daya a dakin.
Shiko tunda ya kama hanya yake jin wani bacin rai da bakin ciki a ranshi yana fadin wanan aljanan yarinyar sai ta kasheni wata rana.
Yarinya yanzu ta sauke min bacin raina yanzu kuma ta kara sakani a wani anya ma mutnce kuwa dai , ?
Yana shiga gidan a hargitse ya samay su duk kan su Nafisa ta haukace masu daga ita sai dan buje a jikin ta tana fadin yaushe samad ya fara cin amana na haka ?
Yaushe samad ya canza ban sani ba nayi sakaci da yawa har na bari haka ya faru a yau da ban dauki mataki ba.
Haka ya shigo ya samay ta tana wanan sambatun a cikin yan uwanta da suke ririke da ita kamar sabuwar mahaukaciya.
Nan ya shigo baice da kowa kalaba cikin fushi ya shigo gidan don haka basu ga fuskan wani magana a gareshi ba.
Tayo cikin shi da zagi tana fadin macuci mayaudari sai Allah ya isar min a gare ka har zaka dauki waya kabawa wata mace ta fada min wai baka da lafiya a wurin ta.
Da karfi ya banbare hannun ta da ta rike mai wuyan rigar jikin shi ya fisge ya shige dakin shi a hasale.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Maryam kamar jirana take in gama debe kayan a jikina ina zama tace amma friend zurinfin cikin ki yayi maki yawa wallahi.
Ashe wanan guy din da ake nema ruwa a jallo dan uwan ki ne ban sani ba saurin kallon Maryam nayi nace ruwa a jallo ake nemas may yayi.
Tace tsadan ganin gare shi mana gashi dai matashi ne amma Allah ya kai shi ga babban matsayi nace wani matsayi ne gare shi wanda kike zuzutawa haka wai ?
Kai haba friend zakice baki san koshi waye ba kina tare dashi haka mutumin nan fa na hango tsatsan son ki a kwayar idon shi.
Nace baki hango gaskiya ba idon ki bai hango maki gaskiyan alamarin ba kuma koda kin hango ma bai taba zama gaskiyan magana.
Mutumin da gidan shi yafi karfin shi a karskashin mulkin ki mace yake wanda baida mutucin duban yan uwan shi tunda na fara magana ta kafe ni da idanuwan ta.
Shiru nayi don na farga na fara sakin layi dariya tayi tace min kin dakata kuma mana nace barni da abin haushi don Allah kwantawa nayi rigingine ina tune a raina sai kuma na bushe da dariya ni kadai.
Kallo na tayi tana mamakin abinda nakewa dariya haka ni kadai nace yau akwai bura uba a gida Samad tace akan may kuma nace ke dai bari.
Buzuwar matarshi ta bugo waya tana tambayan shi na dauki wayan nace mata gashi nan wuri na baida lafiya.
Ido ta zaro waje tace kika amsa kiran matar tashi khadija nace kwarai kuwa ina dariya nace zata gane shayi ruwa ne maryam.
Ba gani take ta mallake shi ba ba macen da ta isa tazo kusa da shi hatta uwar shi ta raba shi dasu duk yan uwa ganin su take muggaine bata yarda dasu ba.
Kirikiri ta hana matar shi zama a dakin ta dole yanzu saida ta koma gida take zaune ba ruwan shi da yaran da ya haifa da cikin shi.
Tace khadija kina nufin wanan guy din yana da iyali haka dama idan ka ganshi sai ka dauka ko auren farko baiyi ba a rayuwan shi.
Nace wa mai iyali ne da kike ganin shi wurin nan auren gata ya samu ga iyayyen su shine kuma bai iya riko ba saboda buzuwar matar shi.
Nace Wasa farin girki yanzu muka fara wasan da ita sai na manna mata karamin hauka a zuciyar ta tunda tace bata son hurdan shi da ko wace mace.
Haduwa goma zamuyi dashi sako goma zan tura mata muje zuwa indai nice ko wace mace da dabaranta ake haihuwan ta sai dai na wata yafi na wata kissan.
Khadija kin ko san kisan macen buzuwa macen buzuwa fa duk inda take shu,uma ce bata bari miji ya zauna da matar shi lafiya sai ita.
Nace maryam kin san ko matan minna ko waye su ba buzuwa ba ko tsakiyan matan maradi za a kaini na shirya mata indai akwai ayar Allah.
Zan bi dare in bi rana sai na nuna mata muma matan Nigeria akwai shu,umai cikin mu ai banda matsala tunda na san lagonta ta .
Allah ya bamu saa tace nace amin sai na girgiza kai nace bawai da manufar yaso ni har cikin ranshi nake wanan abin ba yi dai nake in nuna mata boka da malam karya ne.
Tace yanzu yaya kuka kare dashi nace korata yayi daga motar shi kai tsaye dariya ta kwashe dashi tace ai ba zaki kara ganin shi ba ko.
Nace gobe ma yayi nesa ki gan shi nan ai ni abin har mamaki nake ji wallahi tace don dai kince buzuwa ce matar shi amma da sai in ce wani namiji zai samay ki ya bari ki kufce mashi khadija.
Kyau Allah ya baki tsayi da gashi ga ilimi addini dana boko kin tara ranan da naji kina karatu wallahi har rudewa nayi na raya a raina da naje gida komawa zanyi makaranta ni ma na samu in sauke.
Tun ina karama fa na sauke maryam yanzun haka ban bar karatu ba don ina nan ne bana zuwa amma a gida ban wasa da karatu ko kadan kinga yayata malama ce sosai wallahi.
Tace ai naga alama tun haduwa na dake idan kuna waya da ita zata tana makaranta ko gata tana shiri fita makaranta may yafi wanan dadi ga mace.
Nace kinga mu zama yakawo kakannin mu zama garin minna amma aslin mu yan wani gari ne da ake kira ka,oje tun ana hade da sokoto da Niger yanzun haka mu bamu san gida ba mu filani ne na asali wallahi.
Mahaifiyar mu ce kwarin minna amma saboda zama muka juye muka zama mutanen minna baki sanin mu baki ne idan ba mun fada ma ba.
Haba nature din ki yayi kama sosai da na fulani ashe ma ke ruwan su ne nace ada ke nan ina so zuwa garin mu sosai inga yan uwana wallahi.
Don ance har yanzu yan uwan mu suna garin don daddy din mu shi yasan gari har yakan je lokacin da bai tara iyali haka ba.
Tace ya kamata ku nemi gida su san ku fa nace muna da burin haka nida ya Amina ai sai dai kin san abin sai an shirya ne .

Dakin shi ya nufa ya fara cire kayan shi zuciyar shi yana mai soya yana jin kamar ya ganin a gaban shi ya shake ni don haushi da takaicina da yake ji.
Nafisa ce tazo dakin har lokacin a hasale take daidai ya fito daga wanka ta yi mai wani mugun kallo tace yau sai ka fada min gurin wace kaje har ta dauki wayan ka ta kirani dashi.
Baiyi magana ba sai kokarin saka jallabiyan da yake yi a jikin shi ta karaso tana ce mai wata yar iska yar kasada ke son shiga rayuwan ka Samad ?
Ido kawai ya tsura mata yana kallon ta batare da yayi mata magana ba ta sake maimaita tambayan shi samad ka fada min wa cece kaje wurin ta har ta dauki wayan ka ?
Ta karaso tana rike mai kwalar dogon rigan da ya a jikin shi yanzu kama hannuwan nata yayi ya murde ya wurgata saman goda ya nufi inda turaren shi suke ya dauko yana fesawa jikin shi.
Ta kara juyowa ta nufo shi a hasale tana cewa kunji kun gama iskancin ku shine ka dawo gidana kana min wankan tsarki anan.
Da mamaki yake kallon ta ya bude baki da kyar yace Nafisa yau ni kike wa zargin aikata zina da wata kace tace dole in maka samad may ye hadin ka da wata mace , ?
Yace dani mazanaci da akan ki zan fara tunda dashi kika gabatar min da soyayyan ki farkon haduwan mu dake.
Haushin maganan shi taji sai ko ta haushi da duka da yakusa tana ture shi tsayawa yayi yana kallon ta da mamaki.
Jayeta ya kara yi ya hakadata gefe ya fice daga dakin ta biyo shi tana zagi ta uwa ta uba ya shige dayan dakin ya kyale ta.
Yana shiga wayan shi na kara ya dauka Yusuf ne yake son fada mashi ya gama tsara masu tafiyan da zasuyi kaduna.
Yace sai dai abinda zamu saya wa yaran nake son mu dauko khadija ta zaba muna abinda ya dace dasu tunda mu ba zaben kayan yara muka iya ba.
Yusuf ya ambaci sunan shi a kasalance Yusuf din ya amsa mai yace don Allah ka rabani da wanan yarinyar dake batun tarwatsa min gida da rayuwa na.
Cikin mamaki Yusuf din yace tayi ma wani abune kuma ban sani ba yace may ne ma batai min ba yanzun haka in ka saurara zaka iya jiyo hargowan Nafisa akan khadija.
Da sauri Yusuf din yace dashi kai haba sun hadu ne komai ko ta samu labarin khadija din ne yace basu hadu ba sai dai yau kaddara ya hadasu a wayana.
Nan ya koro mai abinda ya faru yau din dariya sosai Yusuf ya kwashe dashi lokaci guda yace kai khadija akwai jan magana da rashin tsoro.
Yace ni yau taja min masifa da fushin Nafisa a gidan nan ban son wanan bakin kishin na Nafisa wallahi idan ya tashi bataji bata gani imagine wai har ni Nafisa ke ma zargin zina yau.
Intrested ashe yau tasan zaka iya kara aure ko wani lokaci ke nan wow i am impress da jin wanan labarin Allah yasa haka yasa ta fara gyara halin ta.
Rikici kake son jawo min Yusuf da ka hada ni wanan aljanan yarinyar mai shegen rigima wai dole sai itace zatai min wanan aikin ne ?
Kana son mu canza wata ce ya tambaya shi a cikin gatse yace No da sauri yace ta faye matsala ne wallahi.
Yace da matsalan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login