Showing 57001 words to 60000 words out of 133935 words

Chapter 20 - Mijin Buzuwa Book One Complete Hausa Novel

27 Oct 2025

273

yanzu sai dai abin bai wani yi nisa sosai ba.
Idan kuma bata bi alamarin a hankali ba zafin kishin da take nunawa ne zai sa komai ya iya faruwa da ita.
Hakalin ta ya tashi sosai wanan ne mutum na biyu daya fada mata haka malamin yace alamarin yarinyar yana da karfi sosai.
Don asiri baya kamata kai tsaye da zaran zamcen yakai ga iyayyen shi komai zai iya faruwa a tsakanin su a yadda bata zata ba.
Don haka sai kin natsu aiki zamuyi maki wanda zaki kama mijin ki a hannun ki indan shi ya kamu yadda muke so komai zai iya zo maki da sauki.
Amma koda zakici nasara akan hakan sai kin bi a sannu don yarinyar tafiki komai da kike tunanen kina dashi abune wanda sai an aiwatar dashi a sannu saboda mijin ki yana mata mugun son da bai san yana mata ba.
Nashiga uku tace malam tafini komai fa kace yace kwarai da gaske don gata nan a gaban mu kina gani ta shige maki gaba ko a wurin shi.
Kuka ta fara tana fadin don Allah malam kai min rai ka taimake ni ko nawane zan iya baka indai zaka min aikin da za a raba su hayatan hayatan ya ji bai kaunar ta ko kadan.
Gaba daya yanzu na daina gane kan shi ada komai yana min kai tsaye yanzu sai yaja min rai yake min abu da na dauka ko cikin dake gare ni ne yasa yake min hakan.
Yace magana dai guda ce ga yarinyar nan kina gani taurarin ta na da matukar haske sosai duk abinda ta sama gaba takan cin ma nasara a kan shi lokaci daya.
Yana nuna masu zanen da yayi a kasa wanda su basu fahintar abinda ya zana sai dai bayanin da yake masu wanda ke matukar tayar wa Nafisa da hankali.
Yace saukin abin daya ne yarinyar mijin ki baya gabanta don wani dalili nata amma shi yana kokarin cusa kanshi ko yaushe a wurin ta ne.
Tace da karfi shi samad din malam yace kwarai kuwa muddin muka ce zamuyi aiki na gagawa komai zai iya faruwa na fada maki.
Idan baki yarda ba zaki iya zuwa gurin wani kiji nasan duk wanda zai fada maki tsakani da Allah ba zai fada maki sabanin abinda na fada maki ba.
Tana share hawayen dake zubo mata take fadin malam yanzu may ye abin yi don ko yanzu da dabara na samu nazo nan din.
Wanan ba wani matsala bane aiki zamuyi mashi wanda hankalin shi zai fita a kan wata mace baki daya sai mu cus mashi kaunar ki ke kadai.
Ta gyara zama tana fadin in hakan zai samu malam shi nafi bukatan ai min a kan shi a raba shi da ko wace yar iska ce kison tayi min kutse a gidana.
Ya zayyana masu aikin da zai masu din ta yarda ta amince zata biya makam din abinda ya bukata a wurin ta suka biya shi ba tare da taji komai ba sukai mashi sallama.
Tun a mota take zazaga balai tana zaginshi da iyayyen shi Auta tana kara zugata da fadin wanan wata irin yarinyar ce da za a ce ta fiki komai har kyau ke nan malam yake nufi ko may.
Don banda kyau babu wani abu da Nafisa ke kadagi dashi don ba arabi ba boko haka take dip dinta bakauya kuma.
Koda ta dawo kaduna bata biya gidan su Abdul din ba bata mayi tunanen shiga gurin su ba don daukan su take a makiyan ta dama balle yanzu da sunan su ya fito ga zancen.
Kwanata uku a kaduna bayan Auta ta koma ta koma ta karbo abinda zasuyi amfani dashi idan ta koma sauran sai ya hada yace zai kira Auta ta karban mata don sai ya nemi abin hadi.
Haka ta shirya sai da zata wuce ne ta dan shiga tsatsaye ta gaida su hajiyan shi da sauran mutanen gidan ta juya suka tafi.

Almarina kuwa tunda na dawo sau daya muka hadu dashi koshi a tsatsaye don ina sauri zan tafi class karatu don muna da test din da zamuyi washe gari.
Yazo min da provition mai yawa kamar ba gobe har sai danace kayan suyi min yawa yace naci da kawayena.
Sun tafi abisa alkawrin zamuyi waya amma har wani lokaci bai kirani ba Yusuf ma haka bai kira ba nikan haka yafi min nono fari.
Don dama neman mafita nake dashi kuma na samu yanzu sun sarara min ranan muna hira da maryam take tambaya na su.
Nace banji komai daga gare su ba na nuna mata ni basu gabana yanzu abinda ya kawo ni nakeyi.
Tace kai amna abin mamaki ne khadija ace sun share ki haka ba labarin komai daga wurin su ko yusuf ai ya kamata ace ya kira musan halin da suke ciki.
Ke kuma baki neme su ba halarci baice haka ba fa khadija shiru nayi mata don mu kawar da zancen su da ta dauko min ina zaune kalau.
Sai bayan da na kwanta sai kuma maganan ya damay ni a rai gaskiya maryam ta fada min ya kamata ka kula mai kula ka koba komai zai san ka damu dashi ai.
Ranan da kyat na samu nayi barci da tunanen su a raina sai dai ni ba zan iya kiran shi ba sai dai dan dama dama Yusuf din.
Washe gari haka na tashi da jin bakin rai a zuciyata sai dai kawai na danne abin a raina don na kudurta a raina ba zan taba kiranshi ba indai nice zakira inji ko lafiya suke.
Tunda dama ba wani soyayya ko wani abu ke tsakanin mu haka ba mai karfi kawai dai ya gaji danine shima ya hutar da kan shi.
Na share kawai kada maryam ta fahince ni na shirya muka nufi cikin school don daukan lectures na watsar da maganan su a raina kada in sa wa kaina damuwa a banza.
Alamarin gidan shi kuwa yanzu tun dawowan Nafisa daga kaduna sallon zaman su ya sauya don yana dan samun kulan daya kamata daga gareta duk da ba wani dadin yake ji ga hakan ba don baya samun sakewa har yanzu a gidan shi yadda yake so.
Shima Abdulsamad din ina a ranshi yakan so ya kirani yaji lafiyata sai dai yanzu duk lokacin shi na aiki ne dana Nafisa a haka har yayi tafiya tare suka ketara da nafisa zuwa wanan tafiyan.
Satin su biyu suka dawo Nigeria koda suka dawo abuja bai samu kafan kiran na ba don Nafisa ta mamaye komai a lokacin.
Yau suna tare da Yusuf a office din shi Yusuf ma wanda yayi tafiya yake tambayan shi labarina ya yamutsa fuska yana fadin wallahi banda labarin ta itama bata neme ni ba.
Yusuf yace haba kai ma kasan bazata nemay ka ai, amma hakan bai mun dadi ba wallahi dakace baka kirata ba waya ya dauko daga Aljihun shi ya fara neman layina a lokacin.
Ban shiga school ba ranan don na tashi da ciwon mara ina kwance a dakin mu ko karyawa ban yi ba har lokacin don haka ina cikin barci mai nauyi daya dauke ni naji kira a wayana.
Da kyat na lalubo wayan dake gefe na ina jan tsakin wanda ya tayar dani a wanan lokacin dana dan samu sa,ida na samu barci ya dauke ni.
Koda na dauko har kiran ya katse sunan Yusuf na gani akan wayan ban kai ga tunane ba wani kiran ya sake shigowa again.
Tunane nake a raina may kuma zai fada min yanzu mutanen da suka shareni kusan wata daya ke nan yanzu kuma zai kirani yace min may ?
Kamar in share shi kiran ya katse sai dai na danna recieve inji abinda zai fada min a lokacin na amsa da sallama cikin muryan barci da yanayin ciwo a tare dani.
Naji yace subbahanallahi khadija baki da lafiya ne may ya samay ki naji muryan ki a haka ?
Da sauri ya dago kai yana kallon Yusuf dake magana a waya yaji yace ayya sorry sannu ko kin je asibiti ne nace nasha magani ai ba sai naje asibiti ba.
Idon shi har lokacin yana akan Yusuf din yace may ke damun ta ne naji Yusuf din na fada mai wai banda lafiya ne a kwance nake ma.
Taje asibiti Yusuf yace tace ba sai taje asibiti ba wai karban wayan yayi daga hannun Yusuf din naji muryan shi yana fadin ki shirya yanzu gani nan zuwa nakai ki asibiti ya fada kai tsaye.
Nace naji sauki ba sai kazo ba na kashe wayan wayan ya kalla tare da mikewa tsaye yana rufe file din dake gaban shi ya fara tafiya.
Yisuf dake zaune ya mike juyowa yayi yana fadin ka zauna ka karasa aikin barin je na ganta in dawo Yusuf yace amma kana ganin zata saurare ka idan kaje kai kadai.
Wani kallo yayiwa Yusuf din kamar zaiyi magana sai kuma ya juya ya fita Yusuf ta girgiza kai yana murmushi halin abikin nashi na bashi mamaki ace mutum haka da girman kai.
Nikan ina kashe wayan naja tsuki nace mayaudari kawai naja filo na gyara kwanciya na barcin da ban koma ba kenan idona a rufe nake tunane nace yanzu na tabbatar da karkashin mace yake.
Wata kila matan shi tasamu labari ne ta hana shi kula kowa yanzu ya dawo zai yaudare ni kuma ya bata min lokacina a banza.
Dama ban sa zancen ko kadan a raina ba balle ya damay ni in ma junin shi iya yaudaran mata ne ya bata masu lokaci Allah ba zai bashi saa ba anan naja tsuki na gyara kwanciyana.
Na samu barci ya fara dauka na naji wayan shi ya shigo min na duba na bar wayan nata ruri har ya katse kira uku yai min ban daga ba .
Ranshi ne ya baci sosai yana shirin juyawa sai ga maryam kamar daga sama ta dawo don hankalin ta bai kwanta a yadda ta barni ta dawo ta dubani.
Sai ganin shi tayi yana shirin juyawa da sauri ta karsa wurin shi tana gaidashi tare da fadin wallahi tana ciki bata da lafiya ne tun jiya nima yanzu na dawo in dubatane.
Yace shi yakawo ni yazu asibiti nake son zuwa da ita a ranta tace boye min khadija ke nan rayi ashe suna waya dashi shine take boye min.
Taji yace nakira wayan ta taki ta ga bayan yanzu Yusuf ya gama waya da ita ta fada mai bata da lafiya tace barin shiga in fito maka da ita nasan fushi take daku.
Fushi ya tambaya da mamaki dariya tayi tace ina zuwa don Allah ta wuce ya bita da kallo har tabace yana mamakin kalamin ta wai fushi take da ku fushi akan may ?
Tana shiga dakina ta nufa ta samay ni a kwance zama tayi a gefe na tana min sannu tare da fadin ga mutumin ki nan a bakin get yana jiran ki wai kuje asibiti yanzu.
Wani kallo mai kama da harara na watsa mata nace rabu da mayaudari nine zai kai asibiti akan may zai zo min a yanzu da bana son ganin shi.
Haba khadija kin san uzurin da ya tsayar dasu basu nemay ki ba tunda har yanzu ya iya zuwa da jin baki da lafiya ai ya kamata ki saurare shi.
Haba maryam abinda kika sani ne nafi jin dadin zaman da nake yanzu babu takuran kowa a kaina akan may kuma kike son in kara fadawa tarkon mayaudari irin wanan mutumin da matar shi tafi karfin shi kuma.
Kada kice haka khadija ko ba komai ya nuna kulawan shi a kan ki yanzu ina laifin wanda ya nuna maka haka a lokacin da kake cikin halin ciwo.
Don Allah ki tashi ki daure badon ni ba sai don Allah ki tafi ki ganshi ko ba komai zakiji abinda ya tsayar dasu kwanaki mai tsawo haka baki ji su ba.
Allah da kika hadani dashi ne zai sa in tafi badon wani abu ba can nasa, don ina son inyi nisa da shuumancin su yanzu tace daure kiwa Allah da kika ce zato kike yanzu kila ma ba matar shi bace ta hana ya kulaki.
Kalaman ta yayi tasiri sosai a raina koba komai ina son jin abinda ya hana injisu kwana biyu don ban sin jawa kaina wulakanci ko kadan.
Ita ta taimaka min na shirya atamfa na daura don yanayin da nake ciki tare muka fito zuwa ida yake zaune a motar shi.
Yana yi yana kallon agogon hannunshi can ya ga fitowan mu tare da maryam ina tafiya da kyat yanayin ina jin jikin nawa sosai.
Har muka karaso bai dauke idon shi a kan mu ba yi hakkuri mun barka kana jira wallahi barci na samu tanayi yanzu na tayar da ita.
Bai yi magana ba sai kallona yayi yana fadin shiga mota mu tafi nace basai naje asibiti ba na sha magani naji sauki ina magana da kyat cikin daure fuska.
Shiga muje nace maki da sauri maryam ta riko min hannu ta nufi gefen mai zaman banza tana bude min motar tare da fadin sai kun dawo Allah ya sauwaka.
Sai da na zauna da kyau ya tayar da motan muka hau dogon titin da zai kaimu cikin gari sai da mukai nisa kaina da duke na dafe goshina da hannu na daya naji yace.
May damun ki ne haka ban bashi amsa ba sai gyara zama da nayi ina cije baki don dan motsawan da nayi maran yana min ciwo yanzu.
May damun ki ya sake maimaitawa shiru nayi can nadan sauke nufashi nace da kyar banda lafiya ne kawai tare da dan dafe mara na.
Au ko abin ne yazo maki na manta yanzu kike cikin time din period din ki ko hararan shi nayi tare da kawar da kai ina cewa a raina kaji min mutum da bin didigi haka ?
Kwana nawa yakeyi halan sake dago kai nayi na kalle shi kamar bashi yake maganan ba nayi saurin kawar da kaina daga kallon shi.
Yace bakiji bane kwana nawa kike dauka kina period din nace ya fada tare da dan kallo na nace ban sani ba kada ka wuce hurumin da ba naka ba mana na fada ina kwantar da kaina.
Murmushi yayi yace haka kike ce ko nace na fada din ni banga dalilin tambayana haka ba kai ba likita ba wani sai nayi shiru.
Yace go ahead you say your words out, shiru nayi tare da kawar da kaina gareshi gaba daya ya sake fadin you free to say komai zaki iya fada don ance fushi kike damu.
Da sauri na jiyo ina kallon shi nace fushi fa akan may zanyi fushi daku in ba ina son sama kaina nauyin da bai hauni ba ?
Murmushi yayi da sai ka saurara zakaji shi yace kwana biyu bamu kasan ne daga ni har Yusuf na fita da madam dina ne mun tafi check up ciki ke bata matsala.
Don Allah malam ni ban tambaye ka ba in zaku iya ma ku tare a can ba damuwa na bane wanan ciki kuma Allah ya bata lafiya ya sauketa lafiya amma mi ya hadani da tafiyan ku kuma.
Kwana yasha muka shiga wani clinic inda yasa na fito muka shiga guri ya sama min na zauna ya nufi gurin tankan kati ba mu dade ba duk da mun samu mutane a gurin yace in taso mushiga gurin likita.
Mun shi likitan yare ne don turanci suke dashi sun gaisa naji likita na cewa kayi sabin aure ne ashe yace mashi eh yace madam ta kwana biyu bata shigo ciki ya zaunu ko yace eh a gadarance yake ma mashi magana yace ina son ka duba min ita tana fama da mesturalpain ne.
Yace ayya sorry madam yakamata ace ya rage maki ciwo yanzu da kiyi aure ya kamata ace kin rage jinshi haka indan zakiyi period don agana kawai matsalan hakan.
Nauyi kunya ya rufe ni a wurin na kasa daga kaina shima wayan shi yake dakila baibi ta kan likitan ba sai da likitan ya fara tambayana ina mashi bayanin ya dago yana kallo na.
Tashi nayi zuwa inda likitan yace in kwanta ya dan dadana cikin nawa na dan sake kara daidai kasan mara na daya tausa da dan karfi yace in tashi ya dawo ya zauna yana rubutu a wani farin takarda ya mika mai lokacin na dawo na zauna dakyat dafe da marana dake min tsananin ciwo sosai.
Bayan ya mika mai yayi mai bayanin anemi wanan maganin in sha zasuyi min allura kuma zan samu sauki da yardan Allah ya mika mai hannu tare da fada mai inda zamu kai takardan a duba ni.
Sai da muka gama komai muka fito yana min sannu muka dauki hanya wani shago ya tsaya yace min yana zuwa ya shiga ciki yadan jima sai gashi ya fito yaron shagon na binshi a baya dauke da wasu manyan ledoji biyu a hannun shi.
Ya saka bayan motar ya shiga muka tafi bayan ya mikawa yaron kudi yana mashi godiya kaina na duke yace sannu likita yace zaki samu sauki dan anjima kadan amma zaki barci sosai ki ci wani abu don kince

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login