Showing 66001 words to 69000 words out of 133935 words
isa dajin mai kama da gari da baifi yan gidaje a kirga ba sai da suka huta kafin su samu ganin bokan don ranan suke son su koma Akure su shiga motan dare su koma abuja.
Bayan ta gama fadin abinda take son yai mata nan boka ya fara surukule shi ya dago yana kallon ta na dan lokaci.
Sai duk suka tsargu da irin kallon da yake masu wanda ke nuna akwai magana kai ya girgiza sanan yace aikin ta akwai dan wahala a cikin sa.
Don yanzu haka mijin ta yana tare da wata yarinya sai dai bai hango soyayya tsakanin su ba amma akwai aure har da haihuwa a ciki.
Kirjin ta ta doka tana fadin ta shiga uku ita samad zaiwa kishiya wacece zai aura har su haihu ?
Sam ta mace da Fati ma mallakin mijin ta ne har da diya shi boka Allah bai bashi ikon tsafin shi ya hasko ni ba nan tasa ai mata aikin da za a raba tsakanin shi da ko wacece .
Akuma fitar da ranshi ga ko wace mace a rayuwan shi sai ita kadai ya kara yin saddabarun shi na bokayen da suka gwane da tsafi yace ya ga wata mace sai dai baiga gaban ta sai bayan ta kamar tana son shiga rayuwar mijin ta amma dai bari ya mata aiki akan wace ta baiyana in yaso daga baya aikin da zaiyi zai gusar da waccan matar da yaga bayanta din.
Tace tana son koda kashewa ne a kashe mata wace aka gani ko a haukatata gaba daya kowa ya huta.
Yace an gama sai dai aikin ta na da tsada sosai tace kada yaji komai indai aikin zaiyi kyau nan ya shiga hada mata irin nashi surukulle da bayanun yadda zatai amfani dashi ba tare da kuskure ba.
Yace ba mijin ta ba wata mace da zai duba a duniya muddin tayi abinda ya fada mata daidai suka kama hanya komawa gida bayan ta cika shi da kudi.
Sam bata san Abdul kwana biyu zaiyi a kaduna ba lokacin da Abdul ya iso gida ya neme ta sai cewa sukayi ta tafi unguwane.
Har ya shiga ya huta ya dan kwanta bata dawo ba ran shi ne ya baci sosai da ita yaji yana son fita don haka ya shirya ya fito dan yasan kafin ya dawo ta dawo gida a lokacin.
Sai dai abinda ke bashi mamaki baifi ganin motocin shi duka dayayi ba a gidan yana tambayan kan shi da wace mota nafisa ta fita ?
Yana fita batare da sanin inda zai tafi ba har ya yanke shawaran zuwa wurin Yusuf sai ya fasa don ya san yanzu shima hutawa yake a gidan shi kada yaje ya damay shi.
Sai kawai ya yanke shawaran ya leka khadija don ya kwana biyu da ganin ta hanyar hostel din mu ya dauka sai da ya iso ya kira waya gashi abakin hostel.
Nace da yamman nan yace na koma ne nace gani fitowa yaja iska ya kashe wayan na fito ina tako dadaya wanda ni ban san inayi ba ma.
Na karaso wurin motar cikin yar murya na nace dashi sannu da zuwa baki maraba da zuwa na bane ko may ?
Murmushi nayi tare da fadin naga baka fita a wanan lokacin ne kawai har ina da lokacin fitane na daban da ban sani ba yace shigo mota mana.
Ina shiga sai kawai ya tayar da motar nace da sauri sata na zakayi ko may ?
Bai bani amsa ba yaci gaba da kallon titi may zan sata anan, nace mutum, dariya yayi yace kan nan naki kuwa zaiyi kudi sosai nace ai kafin ka sai da nawa ka fara sayar da na buzuwar ka ita bakuwar haure,
Kuff naji yake ma bakina dan bugu da sauri na dafe bakin nace saboda buzuwa ka dukar min baki ?
Yace ban san hadinki da wanan buzuwar ba nace halinta halinta bai mun bane don tana da ji da kai da son wullakanta mutane.
Ita abi kyama ba a kyamace ta ba sai itace zata kyamace mutane matar tawa ce abin kyama khadija ?
Ba ita duk buzaye abin kyama ne gare mu yan Nigeria sai iri kune dake mai dasu mutane kawai baku kyaman su don su din ba abin yarda bane mazan su da matan su.
Sai mutum ya yarda dasu daga baya su zo su yaudare shi yaudara a wurin su ba abin kunya bane don su din basu da kunya ko kadan.
Shiru yayi yana tunane a ran shi bai bani amsan magana na ba nace kuma gasu da son raba mutum da yan uwan shi su cika gida da nasu yan uwan.
Ga kazatar tsiya da son mamaye komai ya koma nasu su kadai koda kuwa sun samu wasu mata ne a gidan shiru nayi don na dauka bai saurare na a lokacin.
Sai naji yace uhmm go on yaya kikai shiru ba labari kike bani ba nace au na dauka baka sauraro na ai gasu da dan banzan bin malamai da bokaye basu yarda da kowa ba sai kan su suna iya yiwa yan uwan su yankar baya su zauna da mijin yar uwar su.
Zasu iya ketarowa da auren su suzo su auri wani anan alhalin duna da mazan da suka baro a gida sai lokaci lokaci suke lekasu.
Kai bazaye muggan mutane ne sosai wallahi duk wayon ka zasu san yadda suka juya ka indai na miji ne ji nayi ya tsayar da motar da karfi yace bari inyi sallah please sai kici gaba da bani labarin ki.
Fita yayi a motar ya nufi wani gu sai yanzu na duba naga ashe massalaci ne a wurin shiga yayi a ciki na mayar da kaina akan sit din motar ina kallon mutanen da ke gurin.
Ya dan jima a ciki ya fito ya shiga motar ya kama hanya mun dan taba tafiya ba tare da nasan ida zamu nufa ba.
Yace bissimila cigaba da labarin ki nace labarin yai ma dadi ke nan kwarai kuwa ina jin dadin labarin sosai nace toba zan kara fada ba.
Don may ko don kar naji halin buzaye nace ba wanda baka sani ba a cikin wanan kai da ke da ita a gida may ya rage da baka sani ba.
Ina ga saura bani kuddi baba ko a yaye ka kafa ka wayi gari ka samu ta ketara kasan su da dukiyar ka.
Yace da taci rabon ta ashe idan ta iya ketara kasa da dukiyana duka eh tunda a banza kake samun kudin yace haka kike zato ashe ?
Ni ba ragon namiji bane ko da yaushe ina tsaye da kafana wurin neman na kaina zaune a office din nace mai.
Au haka kike dauka na ni ko a gidana nake ina neman na kai na nace gun buzuwa ke nan kai ya girgiza min.
Koda yake dama abinda kuke nema a wurin su na daban ne da sauri ya juyo yace may muke nema a gun su nayi shiru tare da kawar da kai gefe.
Fada min may muke name muka aure su nace su mana tunda irin su ne ku din jara, , , , shiru nayi karasa mana ina jin ki.
Hannu yakai yana kamo min baki nayi saurin rike hannun nashi a karo na farko dana taba taba jikin shi da sauri na sake hannun nashi.
Na kawar da kai na gefe hannun nashi ya duba a hankali sai naga ya sauke murmushi a fuskan shi yace how lucky you're ?
Ke ce mace ta uku da na taba hada jiki da ita a duniya nace nima ina regreting din hakan da nayi wallahi.
Shiru mukayi yaci gaba da tuki wani guri ya shiga da motar mai yawan ginene gine da sasa da yawa yace kin san wanan gurin tsoro ne ya kama ni dana kalli gurin sai na dauka ko hotel ne.
Kai na girgiza alaman tsoro ya kamani sai naji yace nan ne ma,aikatar mu wanda daga MD din mu sai ni a gurin.
Da sauri na kalle shi yace ko kina bukatan shiga kiga gurin da sauri na girgiza kaina nace a,a don Allah ka mayar dani hostel inda ka dauko ni.
Ai bamu gama ba don baki ban amsata ba da sauri nace tamay yace irin mu da kika fara fadi baki karasa ba nace maganar yawuce ai.
Yace a gunki ya wuce ni a wurina bai wuce ba sai naji karasan maganan ki ko mu kwana a nan da sauri na dago ina kallon shi don Allah dai kayi hakkuri ka mayar dani inda ka dauko.
Maimakon yayi abinda na nace sai naga ya gyara set din motar ya kwantar dashi tare da sa hannayen shi yayi matashi dashi yakai kwance.
Muna wurin shiru ba wanda yai magana a cikin mu sai tsukin da nake ja can yace a kasalance kada ki kara jamin tsuki a mota yanzu na fitar dake na wuce.
Kayi hakkuri don Allah ka maidani hostel ina da exam next tomorrow ban son in fadi wani mutum ne ya dun faro inda muke yana haska toci a hannun shi.
Ni dake zaune nake iya ganin mitumin dake tafe nace ga wani nan yana zuwa gurin nan fa bai damu da abinda nace ba yana kwance abinshi yadda yake.
Har mutumin ya karaso ko ya sheda motar shine sai naga ya dan tsaya daga nesa damu yana fadin barka da dare yallabai an wuni lafiya cikin harshen turanci.
Ya dago yana amsa mashi da lafiya kawai sai mutumin ya juya ya koma ciki ban san na firgice ba sai bayan wucewan mutumin yace lafiya kika shige min a jiki haka ?
Ko kina son jin abinda buzuwa ke ji ne ajikina ta leke min da sauri nayi kokarin jaye jikina dana dan manna da nashi sai naji ya riko ni.
Ta yadda har muke iyajin saukar numfashin junan mu a lokacin ka sake ni don Allah wai may kake nufi da nine haka wai ?
Fada min amsan tambayana mubar aurin nan kada masu gadin nan su dauke ni dan iska nace sake ni in fada ma to yace sai kin fada jin irin rikon da yaimin yana kara manna ni a jikin shi nace jarabbabu irin su mana.
Sake ni yayi ya daga bai ce komai ba ya tayar da motar muka bar gurin sai da naga mun hau titin da zai sada mu da hostel din mu hankalina ya kwanta dashi.
Don yadda a lokaci daya naga canjin yanayi a gare shi ya firgitani ainun sai da muka dauki hanyar hostel din yace ki shirya shiga cikin jarababbun mutane daga yanzu.
Ban iya magana ba bukata na shine inga kafata a kasa yanzu a wani shago ya tsaya ya shiga har ya dan dade sai gashi ya fito ina hangen shi tun daga nesa na raya a raina Allah yayi halitan namiji a nan .
Baya ya bude aka saka mai kayan a ciki ya sallami yaron ya shiga muka tafi bakin hostel din mu ya tsaya bai bude motar ba niko a kage nake da in fita daga motar.
Yace zan yi tafiya may yuyuwa baza mu hadu ba sai idan na dawo Allah ya tsare hanya nace dashi tare da kallon shi ya bude min motar.
Kina level nawa yanzu a karatun ki nace two a takaice yace yayi nisa da yawa gaskiya nace ai ni ke yi ba wani ba ban ga amfanin karatun ba a guna amma ai naga su Binta da zainab sunayi suma ?
Wanan matsalar su ne ni nawa matsalar na sani bata wani ba su ya shafa wanan bani ba amma kai mugu ne ko ?
Zaki iya ba kan ki amsa idan kin so ko wani kalar nake ya bude min motar tare da miko min ledojin dake bayan motar ina karba na fice ina fadin mugu kawai da karfi.
Girgiza kan shi yayi ya tayar da motar ya tafi sai da ya fara tafiyane tunanen Nafisa ya zo mashi a rai yana tunanen ko ina taje dazun ya dawo bai samay ta a gida ba.
Ya iso gidan ya shiga a falo ya samu su Hadiye zaine suna hira suna ciye ciye gaishe suke da dawowa yace Nafisa ta dawo sukace bata dawo ba ya shige ya barsu a gurin zaune.
Ya shiga ran shi a bace ya dubi lokaci yaga tara da wani abu na dare goma saura kadan wanka ya shiga yana tunanen Nafisa a ranshi har ya fito ya kwanta shiru ba Nafisa.
Ni na fado mashi a rai jarababu irin ku murmushi ya danyi yana rufe idon shi kamshin turen oud dina yake tunowa daya shaka.
Ya lumshe idon shi tare da gyara kwanciyar shi yana lumshe ido yaji dadin kasancewa mu a tare yau hiran da nake mai na buzaye ne ya dawo mashi a rai.
Ba abinda na raga daga halin da yasan Nafisa dashi zai iya cewa kila wani ya fada min kadan daga cikin halinta daya fahinta.
Sai dai abinda ya tuno inda nace suna barin mazan su a gida su zo duniya su auri wani mijin na daban sunayi suna zuwa ziyarar mazan nasu.
May wanan maganan yake nufi kodai shiyasa Nafisa take yawan ziyaran gida akai akai bai sani ba da sauri ya kawar da wanan zancen kada zargi abinda bashi ba yashiga zuciyar shi.
To wai ma ina Nafisa taje ne uban may tafitayi da tun safe har wanan lokacin bai ta dawo ba yaja tsuki yace zan gwada ma Nafisa matsayin ta na mace a gidan nan.
Goma, sha daya shabiyu saura ya mike zubur hankali a tashe ya mike yana zura riga a jikin shi ya sauko zuwa kasa komai na falon a kashe yake .
Su hadiye sun shige dakunan kwanan su kayan da sukaci abinci gurin babu kowa a wurin tsuki yaja ya fita waje ya nufi gurin maigadi yana tambayan shi ko yaushe nafisa tafita a gidan.
Maigadi yace rabon shi da ita tun shekarajiya da kawar ta tazo suka fita komawa yayi ciki yana tunanen tun shekaran jiya da kenan Nafisa dama bata gidan tun lokacin da shima yayi tafiya ko may ?
Kamar zai tayar dasu hadiye ya tambaye su sai kuma ya fasa ya koma ya kwanta suna barin mazan su a gida su je wani guri su kara aure suna yi suna ziyarar su.
Abinda ya fado mashi a rai ke nan karfe daya agogon da ya kalla ya nuna mai da sauri ya mike zaune biyu saura na dare yaji ana buga gidan maigadi ya bude kofa motar ta shigo sai ganin nafisa yayi ta fito daga motar ta dan tsaya suna magana da ta cikin motan.
Ta shigo gidan a gajiye take kafafuwan ta har sun dan kunbura saboda zaman motan da tayi mai tsawo dakin su hadiye ta fara zuwa.
Ta samu suna barcin su hankali kwance ta ta da ita a cikin magagin barci tace kin dawo da yare tace na dawo bata gane komai a guta ba ta juya zata shige tace Alhaji ma ya dawo dazu da safe.
Dam taji gaban ta ya fadi da sauri ta fita zuwa dakinta ta kayan sihirin da ta dawo take kokari boyewa a wardrobe din ta sai taga an kuna wutan dakin ta.
A fusace ta juyo sai ganin Abdulsamad tayi tsaye yana kallon ta da sauri ta kara gare shi sai yayi saurin juyawa ya fice daga dakin .
Boye kayan ta karasa yi ta rufa mai baya ta murda kofan dakin a rufe taji shi gam ta juya zuwa dakin ta ciki da fargaba da tsoro a ranta.
Washe gari ta samay alokacin ya gama shiri zai fita yana daura agogo a hannun shi yana gani ta ya daure fuska tankar bai taba dariya ba a rayuwan shi.
Rudewa tayi tama rasa may ta fada mashi can dai tace Samad kayi hakkuri na san ban kyauta ba na fita ba da sani ka ba.
Jakar laptop din shi ya dauka zai wuce ta zube kasa gaban shi tana fadi ka yafe min gurin buki naje shine naka wanan lokacin ban dawo ba.
Nasan nayi laifi fita in dade baka nan amma kayi hakkuri haka ba zai sake faruwa ba insha Allahu.
Yace don gani saunar na miji ki fita gida na kwana da kwanaki yanzu kizo kice inyi hakkuri haka kai tsaye bayan kin gama yawon gantalin ki a can.
Kin kwaso kafan ki kin dawo min gida ki koma inda kika fito zai fi maki sauki na baki minti awa daya ki fice a gidan nan da kowa naki.
Samad kayi hakkuri ka yafe min ba zan sake ba yace rufa min baki munafuka wace bata san ciwon kan ta da darajan aure.
Ya sure jakkar shi ya fice a dakin da kyat ta iya mikewa tsaye daidai lokacin ya dawo yana fadin fita min daga daki zan rufe abina ne .
Ta bishi da kallon mamaki a kofan tana tsaye ya rufo dakin shi karo na farko a gidan abin ya mata zafi saidai cikin ranta tana fadin yi