Showing 69001 words to 72000 words out of 115235 words
Chapter 24 - Halin Girma Hausa Novel Complete
love me or else..." Ya rad'a mata a kunne
"Me zance toh?"
"Abinda nayi ta ce miki, I love you Zahraah, Iman, Fatima, Baby, sweetheart duk dai."
"Ni dai... Ni bansan me.zance na."
"Kice I love you baby, ki hada da hot kiss a nan." Ya turo bakin sa gaba, hannun ta tasa akan bakin ya dan cije ta, tayi saurin janye hannun ya maida shi baya.
"Oya ina jinki, say it, inaso naji muryar ki tana fad'a "
Shiru tayi kunya na kamata, kunyar sa take ji sosai ta yaya zata fara furta masa wani I love you right in front of him, ai da kunya tunda ba sabawa tayi ba, gashi har da wani hot kiss shi ko kunyar nan ma babu. Rufe idonsa yayi ya sake turo mata fuskar tasa
" I'm all ears."
Minti kad'an yaji shiru ya bud'e idon, lokacin har sun sauya zuwa wani abu daban, saurin dauke kanta tayi tana turo baki. Kamar daga sama taji hannun sa a cikin rigarta, ta juyo da sauri tana rik'e hannun
" Dan Allah tsaya zan fada, wallahi zan fad'a."
" Oya ina ji, don't waste my time."
" I lo...ve... You." Tace a rarrabe
" Ban yarda ba, ki fad'a kai tsaye daga chan k'asan zuciyar ki, in a romantic way., Kice I love you Muhammad. "
" I love you Muhammad. "
Tace da sauri kamar wadda tayi gudu ko tsere. Murmushi yayi mata ganin yadda ta fitar da maganar, yana son komai nata, har kunyar ma, ya san in dai suna tare toh har wanka ma sai ta yi masa wataran, zai koya mata komai, yadda yasan yana so rayuwar auren su ta kasance.
Zaka rantse wani babban laifin ta aikata ganin yadda take jujjuyar da fuskar ta gefe, zaunar da ita yayi ya fita, tashi tayi da sauri ta haye gadon ta kwanta, shigowa yayi dauke da cups akan tray da vacuum flasks dake dauke da black tea, dorawa yayi akan table ya zuba ya mika mata, sannan ya zauna a gaban table din ya shiga kurbar nasa da zafin sa. First time na shan black tea dinta kenan amma sai taji yayi mata dadi sosai, sai dai bata shanye ba ta ajiye a gefen nasa ta dawo ta sake zama, sai kuma ta tashi ta nufi toilet din ta daurayo bakin ta, ta fito ta haye gadon ta kwanta. Kallon ta yake har ta gama ta rufe idon ta, sai da ya gama shan tea din tas, ya wanko bakin sa sannan ya kashe hasken dakin ya barshi k'asa k'asa, ya kwanta rigingine yana kallon sama, yana tunanin yadda zai bulowa al'amarin Lailah don baya son a samu matsala, gashi har lokacin bashi da wata hujja da zai kare kansa. Ganin zai cigaba da bata lokaci wajen tunanin abinda bashi da iko akai yaga gwanda kawai yayi abinda zai karu ya kuma samu dumbin lada, duk da yasan duk gudun sa take amma ba zai iya hakura ba.
Ji tayi an matso ta sosai, tsoron ta ya karu zuwa sanda taji yana jujjuyata, kuka ta saka masa bil hakki da gaskiya dan tayi masifar tsorata da abinda ya faru,
"Dan Allah kayi hakuri."
Ta hau bashi hakuri ganin ya dauki hanyar da yar kwakwalwarta ta gaza dauka balle ta gane karatun. Tsayawa yayi chak da abinda yake, ya soma lallashin ta cikin kalamai masu dadi da kwantar daa hankali, a hankali ta dinga samun nutsuwa har ta dawo da nutsuwar ta, ta saduda ta saddakar ta mika wuya, domin dama ance shi aure yakin mata ne, toh tabbas wannan yana daya daga cikin manya manyan yakin matan. Ba zata iya cewa ga kalar wahalar da tasha ba, duk da yayi matukar kokari wajen ganin bata sha wahala sosai ba, amma kuma dole ne, sai dai a hankali a hankali komai zai daidaita haka rayuwar take haka kuma kowa yayi har ya saba. Ita dai bata san sanda wani baccin wahala ya kwashe ta ba, a hakan ba tare da ta gyara ba, sai chan cikin dare ta farka ta zame jikin ta, ta wuce toilet ta gyara kanta sosai sannan ta dawo dakin ta kwanta tana shigewa jikin sa, sake rungume ta yayi tsam a jikinsa bacci ya sake awun gaba da ita.
Da yake tafiyar wuri zai saboda ogan sa da yake son gani, ya saka yana sallar asubah yayi mata sallama ya tafi, kamar ta hanashi tafiyar haka taji amma bata nuna ba, dan ta lura da muhimmancin tafiyar tasa shiyasa ma bata nuna damuwar ta ba, bayan gari yayi haske sosai Ammi ta aiko aka tafi da ita chan shashen ta, daga nan kuma aka kaita ta gaida Bubu, ya saka musu albarka sannan ya hada da nasiha akan rayuwar zaman aure wadda ba zaka taba iya gane ta ba sai ka shiga cikin ta.
Sai dare ta dawo bangaren ta, tayi wanka ta dauki waya da nufin kiranshi sai ga kiran nashi ya shigo, sunyi exchanging text message amma basuyi magana ba tun da ya tafi, whatspp yace ta hau ya kirata video call suka dade suna waya, kamar kar su rabu da k'yar suka hakura suka kwanta.
Kwana biyu da tafiyar sa, babu wani abu da suka samu daga ita har Muhammad din, duk da yace yana kokarin sa daga chan din ma amma sam hankalin ta ya gaza kwanciya, gaba daya bata cikin hayyacin ta kwata kwata dan ko sunyi waya korafin ta kenan.
Duk shirin da ya kamata Laila tayi taa gama, ta saddakar dole ne ya aure ta, dan bashi da wata hujja duk wata hujja ma bata bar mishi ba, shiyasa take shirin ta hankali kwance kuma shiri gagarumi dan biki zatayi na kece raini, ita kanta Kilishi sai ta zama yar kallo, amma kuma ita kanta tana son auren ya yi wu, dan rashin samun mafitar Muhammad din shi zai taimaka sosai wajen cikar burin ta, dan ta riga ta gama aikawa duk wasu manyan masarautar sakon abinda muhammad din yayi, ta kuma san ba zasu taba bari a zaba musu muhammad din a matsayin shugaba ba.
Ana gobe wa'adin da Bubu ya gindaya masa ya dawo, shi kansa ba a nutse yake ba amma yayi kokari sosai wajen kwantar mata da hankali. Takanas yaje ya samu Aji sukayi magana be baro wajen Ajin ba sai dare sosai, yayi tunanin ma zai tarar tayi bacci amma sai ya ganta a zaune tana jiranshi.
Tsokanar ta ya hau yi har sai da ya tabbatar ta manta, suka kwana cikin farin ciki sai dai asubah nayi duk jikinta yayi sanyi, duk abinda take yana kallon ta, ya kuma kara tabbatr da da gaske tana son shi tana kuma kishin shi sosai, sai dai bata son ta nuna kishin nata a fili, ta barshi a zuwan kawai tana tayashi ne. Da wuri ya shirya ya fice ta biyo shi har kofa kafin ya fita, ta rik'e shi sai hawaye, janta yayi zuwa falon ya rarrasheta ya samu da k'yar tayi shiru ya fice yana waya da Musaddik.
Kasancewar ranar ne ranar da Bubu ya shirya ranar da zai sauka ya bawa muhammad mulkin duk da shi Muhamamd din bashi da masaniya, sai ya zama na gaba daya masarautar ta cika sosai da manyan mutane, tun a daren jiya wasu suka iso. Hakan ya jawo bubu ya shiga busy sosai, sai da suka hadu da muhammad din a masallaci yace ya same shi karfe takwas na safe a bangarensa. Shiyasa ya shirya ya fita da wuri, ya kuma same shi yana shiryawa,. Kai tsaye Bubun ya tambaye shi idan yana da wata magana akan abinda ake tuhumar sa? Kai tsaye yace bashi da wata hujja da zai kare kansa, amma yasan be aikata abinda ake zargin sa ba, shiru Bubu yayi dan yadda maganar ta karade ko ina har kunyar fita yake a yau, sallamar sa yayi kawai ba tare da yace komai ba.
Fitowar Bubu ya saka kowa nutsuwa, fadar tayi tsit bayan ya zauna, wanda suka sanshi suna kallon shi zasu gane ransa a bace yake,limamin babban masallacin Masarautar ya saka aka kira masa shi gaba, ya matso gaba, Bubun ya bada umarnin za'a daura auren Muhammad da Laila. Nan da nan fad'ar ta dauki hayaniya, kowa na kokarin tofa albarkacin bakin sa!
*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*
*_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_*
_SO DA ZUCIYA_
*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_
*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_
*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_
*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_
*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k
*_Zaku tura kudin a_*
6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*
*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇
08184017082
*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇
09134848107
2/3/22, 21:11 - Buhainat: Halin Girma
28
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
******* �?
Jan kafa ta dinga yi har zuwa wajen da jakar ta ke ajiye, ta hau zazzage ta ko Allah zai sa taga wayar ta, tun da tazo gidan bata sake ganin wayar ta ba, gashi tana matukar bukatar tayi magana da Mama, ji taka kamar mutuwa zatayi saboda azabar wahalar da take ciki. Bata ga wayar ba, sai yan kayan ta da Bashir din ya dauko mata daga wanchan gidan da yafi mata nan sau dubu duk kuwa da rashin haduwar gidan amma chan a kalla zata samu yancin ta, ba kamar nan da take xaune karkashin matar Bashir din ba.
Kwanciya tayi a tsakiyar dakin, tana cigaba da rera kukan ta, har zuwa lokacin da taji ana taba kofar, kafin ta bud'e ta zuro kanta
"Uban me kike wai har yanxu baki fito kin yi ayyukan ki ba?"
Ta tsinkayi muryar ta har cikin kwakwalwarta, matsawa tayi amma bata tashi ba, shigowa tayi a fusace ta mik'ar da ita, ta k'wala ihu cikin azaba tace.
"Dan girman Allah kiyi hakuri bani da lafiya."
Da sauri ta saketa, ta ja baya tana kare mata kallo
"Kutmar U! Ni Bash zai munafunta? Kan bala'i amma wallahi sai na yi masa rashin mutunci, dan wulakanci duk yadda nake kaff-kaffa amma sai da ya zagayo ya taba yarinyar na? Ni xai zawo wa raini!"
Kamar wadda ake hankadawa ta fice da sauri, Zeenat na jinta tun daga kofar ta fara k'wala masa kira, baya kasan da ta barshi haka kuma baya sama ya riga yasan abinda ya aikata shiyasa ya bar gidan. Sake dawowa tayi dakin ta tashi Zeenat din tsaye da karfi
" Tunda har kin iya kwana da miji sai ki fito kiyi aiki, babu wani langabewa da zakiyi wallahi sai kin min aiki."
"Dan Allah kiyi hakuri wallahi zazzabi nake ji, jikina duk ciwo yake."
"Hehehe..." Ta saki shewa tana mata kallon banza gami da tafa hannu
"Idan kinga na kyale ki sai dai idan mashasharar mutuwa naga kina yi, amma wallahi tunda kika kwana da miji sai kinyi min aiki."
Kuka Zeenat din take da gaske ba da wasa ba, kuma da gaske take zazzabin take ga wani irin ciwo da ta kasa gane wanne iri ne, a lokacin ne ta tuna wtaa rana ana ruwan sama, haka Mama ta tursasawa Iman wanke mata wasu kaya masu yawan gaske,sannan tana wankin tana girki duk kuma a bayan, har aka kare ruwan nan tana kaiwa da komowa ba tare da Maman ta tausaya mata ta duba halin da zata shiga ba, a lokacin ita tana kwance a daki tana karatun wani littafin hausa, sai bayan an gama ruwan ne ta fito ta sakawa cikinta abinci ta sake komawa.
Tulin kayan wanke-wanken da yake gabanta ta kalla, ta sake fashewa da wani sabon kukan, a hankali ta zauna a gefen dandamalin ta shiga wanke su tana yi tana kuka shabe-shabe.
Sai da ta gama komai ta gyara gidan tas sannan ta samu ta sakawa cikinta ruwan tea da take jin shi kadai zata iya sawa a cikin, ta koma daki ta kudundune tana jin sanda Hajiyar ta bar gidan cikin rakiyar kawayenta. Bayan kamar minti goma sha biyar da tafiyar ta, ta tashi ta dauki jakar hannun ta, da mayafi ta fito ta nufi hanyar gate din gidan, fatan ta kawai ta bar gidan idan har ta fita toh babu ita babu auren Bashir ko me za'a iya sai dai ayi amma ta gama auren. Har taje gate din bata ga kowa ba, haka babu me gadi a wajen tayi saurin isa kofar ta kama ta bud'e ta, sai taji ta a rufe, ta ja da dan ragowar karfin ta amma still ko motsi kofar batayi ba, tana haka ne sai taji alamun ana saka key ta waje, kafin ta iya barin wajen har Bashir ya shigo sanye da sabuwar shadda kunnen sa makale da waya yana magana yana dariya sai dayan hannun nasa rik'e da wayar ta da leda me tambarin sahad stores.
"Zan kiraka oga, nagode sosai." Ya katse kiran yana dubanta
"Ba dai guduwa zakiyi ba?"
"Ban sani ba." Tace tana matsawa gaba tana cigaba da kokarin bud'e kofar dan da ya shigo rufe tayi yayi
"Muje ciki kiji."
"Babu in da zani, na gama zama a bakin gidan nan, da muguntar matarka, wallahi gidan mu zani ba zan iya ba."
"Naji toh, amma kizo muje kinga na siyo miki chocolates masu kyau da gasasshiyar kaza, da yogurt."
"Da yake ka samu mayya ko? Toh ba zan koma ba wallahi."
Sai ta fashe da kuka da karfi, da sauri ya toshe mata baki, ya sungumeta tana ihu be ajiye ta ba sai da ya kaita dakin, sannan ya dire ta, gani yayi idan ya biye mata zata tara masa mutane. Yana ajiyeta ya zauna a gefe yana bud'e ledojin
" Nasan kinsha wahala jiyan nan, taso kisha fresh yogurt din nan zaki ji dadi."
Banza tayi masa ta cigaab da gursheken kukan ta. Ci ya hau yi yana kallon ta, yana jin da zata yarda da ya sake zuwa karaye, amma yasan yadda ta sha wahalar nan zai yi wuya ta amince masa, yaga kiran Hajiya wajen sau goma amma be daga ko daya ba, dan yasan kwanan zancen yanzu ma sai da ya tabbatar ta bar gidan sannan ya shigo, da ace Zeenat din zata amince masa da lafiya lou, shiyasa ma ya tsaya yayi mata siyayyar yasanta da shegen kwadayi, amma sai yaga ko kallo be isheta ba daga shi har kayan hannun nasa. Sai da ya kusan cinyewa sannan ya tuna ya rage mata, ya mike zai fita ta tsare shi
" Bani wayata."
"Hauka nake? Kije ki kira min ruwa kenan, ai kinga na baki wayar nan ko? Toh nasan me na taka in da ko kinje sai kin dawo da kafarki."
Matsar da ita yayi ya fice yaje ya dora ruwa, yayi zafi ya juyo mata a wani babban bawo ya kai mata toilet ya dawo ya sake sungumarta tana dukansa da komai ya kaita, ya danna ta ciki ta dinga ihu tana tashi amma sai da ya daddanne ta har ta hakura ta zauna, sannan ya fito ya barta a ciki, ya nufi gate ya samu me gadi ya dawo ya ja masa kashedi akan kar ya kuskura ya barta ta fita sannan ya fice daga gidan da baya saka ran dawowar shi sai dare yayi sosai saboda Hajjajun sa da yasan ta tama zata kare masa tanadi tsaf dan ba abinda ta tsana kamar tarayya ita da wani akan abu guda!
***Tana zaune ya dawo daga sallar, ya chanja kayan jikin sa zuw doguwar jallabiya maroon colour me kyau, bata kai masa har k'asa ba, tashi tayi suka hadu a hanya sannan suka karasa tsakiyar falon, ta wuce zuwa dining area din ta dauko warmers din ta dawo ta jere su a k'asan bayan ta ciro table mat ta shinfid'a akan carpet din
"Me yasa zaki bawa kanki wahala bayan duk wannan aikin kina da wadanda zasuyi."
"Ban iya zama haka nan babu aiki ba wallahi, ni nama sallame su tun dazu nace su je zan neme su."
Jinjina kai yayi yana yaba mata, tashi yayi ya tayata suka karasa sakko da sauran kayan, sannan yayi serving nasu a plate daya, da spoon daya, debowa yayi ya nufo bakin ta yace
"Oya, it's my duty bud'e bakin ki."
Dariya ta saka ta bud'e bakin a kunyace ya saka mata, sannan shima ya diba ya ci dadin girkin ya ratsa shi, lumshe idon sa yayi ya bud'e yana ware su akanta
"Da gaske kice kika yi abincin nan?"
"Da gaske!"
"Wow... Alhamdulillah Ya Allah, I'm blessed ta ko ina, Allah nagode maka, abincin nan yayi dadi sosai,Allah yayi miki albarka."
"Amin."
Ta amsa tana jin dadi sosai, babu abinda mace take so irin idan tayi abu a yaba, tana fatan ya dore har gaba, hakan yana karawa mace karfin guiwa wajen kyautata ma mijinta. Cikin nishadi suka gama cin abincin, ya sake tayata suka tattare kayan zuwa kan dining din, in da masu aikin zasu kwashe daga nan zuwa kitchen. Falon suka dawo suka zauna, ya matso kusa da ita ya ajiye kansa a saman kafarta, yace
"Ina jinki, bani labarin yadda akayi."
Dan muskutawa tayi ya gyara shima, tayi murmushi me sauti ya maida mata yana jan kunnensa
"Na matsu naji!"
"Abinda ya faru bayan ka fita, na dawo daki na zauna ina tunanin mafita, duk tunanin da zanyi nayi babu wani abu da nake ganin zamu iya rik'e shi a matsayin hujja, duk da haka ban karaya ba, inaji da yakinin Allah ba zai bata nasara ba, hakan ya saka ni tashi na dauro alwala, nazo nayi nafila, na sake rokon Allah akan ya taimaka ya bayyana gaskiya, bayan na idar ne kawai nayi deciding bari na shiga kitchen na ga abinda yake wakana, domin a rayuwa ta kitchen na daya daga cikin wuraren da ya zama tamkar daki na, domin nayi masa sabon gaske. Na tarar da ma'aikata da yawa suna ta hada-hadar hada girki, shine na karbi aikin namu, nace su ji da nasu. Muna aikin ne sako ya iso, a cikin envelope din nan..."
Ta nuna masa tana mika masa
" Flash ne a ciki, wai inji wata mata sanye da nikaf tace a bani, a haka sakon yazo."
Jujjuya envelope din yake a hannun sa, tambarin gidan ne a jikin envelope din, wanda ba kowa ne yake samun ta ba sai jinin gidan... Cigaba tayi
"Shine nazo na saka a jikin Tv, abinda na gani ya saka ni rawar jiki, nayi sauri na