Showing 15001 words to 18000 words out of 115235 words
ya shiga gidan ya gaida matan gidan ya kare a dakin kakarsa ya tarar da yan matan family din sunzo suna da wani get-together da suka shirya sannan suyi maganar tsari bikin Abidah guda daga cikin jikokin gidan.
A kaidar sa baya sakar musu fuska ko kad'an domin suna da rainin hankali sosai, duk da shi basa yi masa neman ma ya kula su suke amma shi sam baya tsayawa shirmen su, da gaske suka shakkar shiga shirgin sa hakan yasa yana shigowa shashen suka dinga yayewa da d'aya d'aya.
Dan tsiririn tsaki yaja sanda suka gama ficewa ya zauna yana muzurai a dole baya son raini shi. Mutane da yawa na fad'a masa yadda yake abubuwan sa kadai ya tabbatar da shi din jini ne na sarauta amma shi sam be san ma yana yi ba ma.
Ya dan jima a wajen nata kafin ya tafi yana jin zai dan dade kafin ya sake waiwayo su duba da tafiyar dake gaban sa akan aikin sa.
***Yana zaune a gate din gidan yana dakon shigowar Abba Babban, a kan idon sa ya dawo ya tashi da sauri ya tare shi ya bud'e masa kofar mota.
"Sannu da zuwa Abba."
"Yawwa Ibrahim, kaine yau a gate din kenan."
" Wallahi kuwa Abba, sannu da dawowa, ya aiki?"
" Alhamdulillah mun gode Allah, ya naka aikin?"
" Alhamdulillah." Yace yana tuna abinda ya faru dashi.
" Allah ya taimaka ya bada sa'a."
" Amin Abba." Yace yana bin sa rik'e da jakar sa a baya.
" Mika jakar ciki bari na fara gano Gaji."
Yace yana bin hanyar da zata kaishi bangaren Gajin, da sauri Khalil din ya kai masa jakar ya dawo ya zauna yana jiran ya fito. Ya dan jima a wajen Gajin kafin ya fito sai dai ganin Khalil ya saka shi mamaki, abunka da Babba nan da nan ya gane akwai wani abu.
" Ya akayi Khalil? Kana son gani na ne?"
" Eh Abba." Yace yana sosa kansa
" Haba ko da naji, toh zan turo a kiraka kaji?"
" Toh Abba Nagode." Girgiza kai Abban yayi ya wuce bangaren sa. Maimakon ya koma gida sai yayi zaman sa anan yana jiran kiran Abban. Yana zaune kuwa yaga fitowar Sadik ya tashi da sauri ya tare shi
"Yawwa wai kazo in ji Abba."
Rik'e hannun sa yayi suka koma yana jin wani iri a ransa, bakin sa dauke da addu'a ya shiga falon ya tarar Abban ya chanja kaya yana zaune da alama abinci ya gama ci. A chan gefe ya zauna yana jin kunya.
"Yawwa ina jin ka Ibrahim, ya akayi?"
Shiru yayi yana tsara yadda ya kamata ya ce, sai da ya dau sakanni yana hado maganar kafin yace
"Dama Abba akan maganar Fatima ne."
"Uhum ina jinka. Ya akayi?"
"Dama... Dama so nake dama a bani dama kamar yadda tsarin gidan nan yake."
Murmushi Abba yayi cikin jin dadi yace
"Masha ALLAH naji dadin wannan abu matuka, Allah ya tabbatar mana da alkhairi kaji? Allah yayi muku albarka."
" Amin Abba." Yace a ciki-ciki farin ciki na kamashi,
" Kaje ku daidaita idan Allah yayi mu haka muke so, an riga an zama daya ai in sha Allah babu wata matsala."
" Nagode Sosai Abba, Allah ya kara girma."
" Amin." Yace yana chanja tasha a tv, shiru Khalil din yayi kafin ya mike
" A huta lafiya Abba."
" Yawwa Ibrahim."
Yana fita ya daka tsalle a wajen yace
"Yes!!"
Da sauri ya bar wajen yana jin kamar ya same ta ya gama ne, zai nuna wa fakirin saurayin ta cewa dan gida yafi bare.
***Sabon yadi ne me saukin kudi sosai, dinkin ma irin dan 1500 din nan ne, a rayuwar sa be taba hasashen saka ire-iren kayan da yake sakawa a yanzu ba, wani kallo Musaddik yake masa yana jin kamar ya kamashi yayi ta bugu.
"Yanzu Moh irin kayan da zaka saka kenan zaka ganin sirikin ka?"
"Wait and see." Yace yana kawo wata leda a kusa dashi, ya wurga masa yana cigaba da kallon kansa a mudubi
"Ka chanja mu tafi idan yaso muyi sallar magriba a hanya sai mu karasa."
"Na saka me?" Musaddik yace da sauri yana bud'e ledar.
"Wait what! Kana nufin ni zan saka wannan kayan."
"Mu nawa ne a dakin nan?"
"You must be kidding me, haba haba an fad'a ma kowa ma irin ka ne."
"Allah su zaka saka mu tafi, kayi sauri karka batan lokaci I'm dying to see my love."
"Aiko sai dai ka tafi kai kadai wannan karyar ba dani ba."
"Da wa toh? Wa nake dashi bayan kai? Kasan da ace ban samu kanta ba dole kaima ka tattaro ka dawo sabon shagon nan dana zauna mu zauna tare. Allah dai ya taimake ka wallahi."
" Ai wallahi babu yarinyar da ta isa nayi mata irin wannan son, the whole you, Captain Muhammad Ahmad Santuraki, dan ga sarki jikin sarki sannan kuma babban soja, ko da yake fa dama ance ku sojoji baku iya soyayya ba, musamman idan allurar ku ta motsa."
Daina abinda yake yayi ya matso kusa dashi
" Idan bansa an saka min kai frog jump ba, kace ba suna na Muhammad ba."
Dariya maganar ta bawa Musaddik,
" Ni zaka saka frog jump?"
" Sosai, ka cigaba da batan lokaci kaga."
Tashi Musaddik yayi ya sake daga kayan, kafin ya fara sawa yana cigaba da mita.
" Kanka akeji wallahi." Moh yace yana cire agogon hannun sa.
" Ka cire watch dinka please, anything da zai sa ta zama suspicious, I don't care idan kowa na gidan su yasan ni waye, amma ita? Da marikiyarta will be the last da zasu sani, surprise ne me kyau nake son basu dukka, sai dai kowanne da yadda surprise din zai zo masa."
" Wicked soul." Musaddik yace yana jefar ta watch dinsa akan mirrow
" What ever!" Yace yana yin gaba yabi bayan sa yana jin dadin kayan jikin sa, babu nauyi shawai shawai amma kuma ba zai yarda Moh din yasan ya ji dadin kayan ba.
A daidai shagon aka daajiye su, yace su je chan in da suka saba jiran sa su jirashi zai kirasu. Duk da basu so ba amma haka suka tafi suka barsu, Musaddik ya dinga jan tsaki suna tafiya a k'asa har suka isa kofar gidan. Wayar sa ya ciro ya kira ta, tayi ta ringing bata daga ba,
" Bata daga ba."
" Da ka kirata tun kafin muzo ai."
" Wannan ba matsala bace, bari kaga."
Ya kwankwasa gate din kafin ya dan tura shi suka shiga, dai-dai lokacin Khalil ya taho zai fita sukayi kichibis, wani kallo ya bisu dashi irin na sama da k'asan nan, kafin ya tuntsure da dariya sosai, hakan yayi bala'in bata ran Musaddik da dama chan baya daukar nonsense.
" Malam lafiya zaka kalle mu kayi dariya?"
" Lafiyar kenan, sai dai kun makara, dan gida ya shiga ya fita ya gama tabbatar da komai akansa, sai abi wani sarkin dan an riga an gama magana kuma su din ba kananan mutane bane da zasu sauya maganar su."
" Kana nufin?" Musaddik yace a zafafe
" Ina nufin kamar yadda na fada mishi ne a baya, Iman matata ce an riga an gama magana rana kawai ake jira a saka mana."
Wani kallo Moh yayi masa da ya saka Khalil shan jinin jikin sa, amma sai ya dake ya cigaba da gaggayawa musu magana. Muhammad be ce komai ba har ya gama, ya juya ya fice ya barsu a tsaye kamar mutum mutumi.
" I have no option than to show him my real identify, idan yaso duk abinda ya biyo baya yayi kuka da kansa ba da kowa ba, karfe nawa ne appointment dinsa?"
" Da safe ne, goma kamar."
" Owk Allah ya kaimu."
" Amin." Musaddik ya amsa ransa na sake baci akan abinda Khalil din yayi musu
HALIN GIRMA
Hafsat Rano
WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_*
*ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA*
*_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_*
*GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi*
*JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE*
*_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_*
*_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_*
*_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_*
*_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_*
*_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_*
*DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL*
2👉🏾400
3👉🏾500
4👉🏾700
5👉🏾1000
*Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU*
09134848107
_*HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽
#team zafafa biyar .
___________
1/6/22, 17:52 - Buhainat: 08
*zafafa biyar na kudine,tuntubi wadan nan numbers din don samun naki copy din ki karanta cikin aminci*
08184017082
Ko
09134848107
*_follow us @ instagram_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1h9y2qgfg67x5&utm_content=nj79azb
Or facebook
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
___________________________
Dan kwantar da kujarar yayi kana ya miqe sosai Samanta yana jin yadda gajiya take bin jikinsa,don gaba daya wunin yau bai shirya fita ba,ya shirya zama ya huta sosai a gida,saboda satin gaba daya cikin aiki ya yisu,babu dare babu raba,har inda ma a tsarinsa babu schedule na zuwansa sai daya ratso masa a sannan din.
hannayensa saman kansa yayin da idanuwansa suke a rufe,yayi nisa a tunaninsa sosai,busy busy ne dashi irin wanda mutane da yawa ke mamakinsa,sam bai bawa kansa hutu ba.
a qalla ya kusa minti ashirin a zaune a haka,wanda hakanan yaji zaman yayi masa dadi,ko ba komai ya dan samu break na wasu mintuna.
Dan waiwayawa yayi gefansa,a sannan ya hango tahowar professor shi da wasu mutane hudu,saiya miqe ya gyara zamansa,ya kuma kunna motar yana jiran qarasowarsa.
yana jin sanda ya shiga yana sallama da mutanen,suka maida murfin motar suka rufe masa,don haka saiya tashi motar,dai dai sanda professor ya furta
"alhamdulillah"yana sauke ajiyar numfashi.
A nutse yake tuqin har suka fita daga airport din,a hankali professor rashid yace
"lawan....ko ka sake koyon sabon salon tuqi ne?"raba idanu samir yayi hagunsa da damansa,saiya lanqwashe murya yace
"eh alhaji"dan jim professor yayi sannan yace
"to yayi kyau"daga haka bai sake cewa komai ba,zaman shuru yaci gaba da ratsawa a tsakaninsu.
"Daka sani ai baka wahalar da kanka ba samir....."yaji abban nashi ya fada bayan tsahon wani lokaci,ya ganeshi kenan,qyaleshi yayi kamar bai gane ba,qaramin murmushi ya subuce a kuncinsa,jerarrun fararen haqoransa suka bayyan,har yayi kamar bazaice komai ba sai kuma ya tanka
"yau daya dai abba....ai nima na samu ladan yau din"wayar hannunsa professor ya ajjiye,ya tsurawa gaban motar idanu,kamar anan fuskar samir din take,baisan me yasa a kullum shi da tilon dan nasa komai nasu yasha banban ba,komai nasu ba iri daya bane,abinda yake sam ba cikin tsari da burinsa ba,ya jima da sanin cewa ba haka yakeso ya kasance ba,ba haka tsarinsa yaso ya zama ba,to amma duk ta inda yake tunanin zai gyarota babu wani sauran dama data rage masa,don haka a maimakon yayi magana,saiya buge da hade yatsunsa waje daya,yana maida tunaninsa wani waje daban.
Duk sanda yayi tafiya irin wannan ya dawo iyalansa dama ma'aikatan gidan kan cika da murna,kamar yanzun,da samir ke biye dashi dauke da wata qawatacciyar qaramar jaka mai zubin akwati,yana biye da professor har zuwa cikin qawataccen falon gidan,mai yalwa da kuma burgewa,wanda ya wadata da dukkan wani nau'in kayan alatun rayuwa.
mutum uku ne ke dakonsa zaune cikin falon,biyu daga cikinsun matasan yammata ne,daya tafi daya tsaho da haske,kamar yadda daya tafi daya shekaru da basu wani taka kara sun karya ba,don dukkansu ba zasu gaza shekara sha tara da ashirin ba.
Daga wata kujera kuma mai mazaunin mutum biyu,macace xaune itama wadda ta mallaki shekaru ɗai ɗai har shekara hamsin,saidai idan har kai mai kallo xa'a qyaleka kayi mata ƙiyasin shekaru,to ba shakka zaka ce dauka cewa bata wuce shekara talatin da biyar ba.
Tun a kallon farko xaka bata sunan HAMSHAQIYA saboda ta cancanci sunan,fara ce sol,shekarunta sam basu boye hasken fatarta ba,tana da matsakaicin kyau wanda ya cakuda da tarin ado da qawar da take qawata kanta dashi kullum kwanan duniya,kallon farko zai gaya maka ta saba da ado ya zame mata jiki,salon irin abun nan da hausawa suke cewa WANKA YABI JIKI,tun daba hannayenta zuwa wuyanta kayan ado ne na mata,fuskarta wadace take da murmushi kamar bakinta zai yage,idanunta qur bisa saman fuskar wadan nan halittu guda biyu,wato samir da professor,tana dubansu da wani irin kallo me nauyi da zurfi.
Dukkaninsu suka miqe kowanne fuskarsa na nuna tsantsar farinciki,daya daga cikin matasan yammatan nan wadda da alama batakai shekarun daya ba ita ta tako da sauri zuwa inda professor yake
"Abba.....sannu da dawowa"ta fada da 'yar siga ta shagwaba,da alama kuma hakan habit dinta ne,tana dora kanta saman kafadarsa,kamar marayan daya samu tallafi,murmushi ya saka yadan dora kansa saman kanta
"barka kadai auta....na sameku lafiya?"
"lafiya qalau abba,saidai munyi missing dinka"murmushin yakuma saki
"gani na dawo ai jauhar,duk wata kewa ta qare ko?"kai ta gyada,sai dayar itama ta matso,tasa hannu kadan tana gyara eye glasses dinta,fuskarta itama murmushinne kwance
"barka da zuwa abba"
"barka kadai lelen abba.....na sameku lafiya?"
"lafiya lau abba ya hanya?"
"alhmdlh,ya karatu?"saida ta saki wani ni'imtacce murmushi,tana jin wani dadi na ratsata,ta daga idanun a hankali ta maida gashi,samir.......wanda har yanzu yake tsaye a bayan abban nasu tamkar wani dogari,hannayensa zube cikin aljihun wandonsa yana kallon dukkan abinda ke faruwa, inside him yana jin tsaiwarsa a wajen cikin abubuwan da suke gundurarsa nan da nan,ya qagu duka a gama wadan nan gaishe gaishen.
dauke idanunta tayi ta maida kan abban,a duniya tana jin dadi tana alfahari abban nasu ya tambayeta karatunta,tana jin wani qwarin gwiwa yana shigarta aduk sanda ya tambayeta wani abu daya danganci karatunta,takanji burinta kwadayinta da qwarim gwiwarta yana daduwa
"alhmdlh abba....komai lafiya"
"ma sha Allah"ya fada yana maida dubansa xuwa gareta,har yanzu bata matsa daga inda take tsaye ba,amma hankalinta idanuwanta da hankalinta dukka yana kansu
"sarautar mata.......yada tsaiwa a nan?"murmushi ta saki
"to ai naga hankalinka duka yana kan yaranka,kaga gwara na barku ku gama tukunna.....barka da dawowa"
"barka kadai.....na sameku lafiya?"
"alhmdlh"ta fada taba jifansa da wani murmushin,saita tako a hankali ta raba ta gefansa,idanunta saman fuskar samir,suna hada idanu ya kauda kansa ya miqa mata jakar professor dake riqe a hannunsa,hannu ta miqa zata amsa tana cewa
"ka kyauta samir"ya fahimci abinda take nufi,saiya saki qaramin murmushi yana juyawa kadan zai fita
"ya da haka son...ka bari daddy ya kintsa muci abincin rana tare mana"ta furta cikin nuna zallar kulawa,kansa ya girgiza yana sosa kan mashi da tsinin key din mota,shida yakeson tsallakewa fadan professor,yayi imanin idan ya zauna suci abin tare zai tono laifin da shi yaketa qoqarin bunnewa ne
"akwai abubuwa da yawa dana bari,zanje na rage wasu,bazan jima yau a waje ba zan dawo gida" sanda yake maganar shima professor ya nufi hanyar da zata sadashi da sassansa da suka qunshi bedrooms manya guda biyu,da.katafaren falo guda daya
"da zaki daina wahalar da kanki wajen tsaidashi,ki barshi ya tafi kawai, saboda haka yakeso,hakan ya tsarawa kansa kamar ko yaushe" sarai samir yasan magana ce mai harshen damo yayi masa,sai data waiwayo ya kalli samir
"ohk....saika dawo,Allah ya tsare" kansa ya gyada sannan ya juya zai fice,itama ta rufawa professor baya.
"ya saraki"kiran da aka masa shine abu na biyu daya shiga kunnensa daga hirar professor da matarshi,sai yaja tunga ya tsaya sannan ya waiwayo a hankali sanda take tasowa a shagwabe ta riskeshi.
Idanuwan najwa tar bisa fuskar jawahir sanda take nufar yayan nasu,saita sanya hannunta ta cire airpiece guda daya cikin biyun dake maqale a kunneta,tana jin wani abu na tokare zuciyarta,ta tsani taga tana magana dashi sam,tana son taji yanzun me zatace da shi ne.
"ya saraki.....please,alqawarinmu fa" ajiyar zuciya yayi hade da lumshe idanu,lokaci guda kuma ya furzar da iska daga bakinsa,baice komai ba saiya cusa hannunsa cikin aljihunsa ya fiddo sabbin 'yan dari biyar biyar masu dama ya miqa mata,wani dan tsalle ta saki bayan ta amshu kudin
"thank you so much,am proud of you my yaya"murmushi kawai ya bita dashi sannan ya taka ya fice.
kudin na hannunta tana juyasu,fuskarta a wadace da murmushi ta koma kujerar data tashi akai ta zauna,duk abun nan da ake idanun najwa a kanta,tana binta da wani kallo da zai nuna maka zallar tkaici da haushinta daya cika mata zuciya,sam jawahir batasa me take ba tana irga kudinta hankali kwance,ganin cewa da gaske jawahir batasan tana yi ba,lissafin kudinta kawai take,saita miqa hannu ta fusge kudin a tare tana furta
"banza"da qarfi,hakan yaja mata hankalin jawahir din yadda takeso,dubanta take baki bude
"me na miki ya najwa"
"banza"ta sake maimaitawa tana hararta,idanuwanta kamar zasu fado akan jawahir din
"wai me na miki?"
"ke wai.me yasa baki da zuciya,kuma baki da kishin kanki?,na meye zaki tambayesa kudi,momi ba zata baki bane da ba zaki tambayeta ba?"sosai jawahir ta bata fuska tana kallon najwan,ranta a dan bace
"amma shi da momyn ai duk daya ne ko?,kuma ko ita ai taga ina tambayarsa,kuma bata ce komai ba"baki najwa ta tabe
'bakya ganewa,kuma ba zaki taba ganewa ba....."
"nidai koma meye bani kudina"ta furta tana miqa mata hannu
"naqi na bayar din"najwa ta fada tana cusa kudin a gefan cinyarta,sai jawahir din ta sake gimtse fuska sosai
"kinga ki bani kudina ya najwa,ko momy tace ki daina shiga harkata ko?"
"idan kina da qarfi ki danne ni ki qwata,sarai dai kinsan babu abinda zanyi da kudin nan.....".
A hankali ta buda qofa ta dawo ta cikin falon,idauwanta ya sauka a kansu sanda jawahir ke sake maimaita wa najwan ta bata kudinta
"lafiyanku?"momyn ta jefa musu tambayarsu,wanda banda tayi magana babu wanda yaga fitowarta cikinsu
"momy....ya saraki na tambaya kudin ankon yasmin tun rannan,to ya bani shine ya najwa ta karba ta hanani,tana masifar wai don me zan