Showing 93001 words to 96000 words out of 115235 words

Chapter 32 - Halin Girma Hausa Novel Complete

runtsa a tsakanin su, in da suka gama tabbatar da sace su akayi, kuka sosai Fulani take tana hango kalar tashin hankalin da muhammad zai shiga idan ya dawo. Zuwa safiya labari ya fara fita, bayan Maimartaba sunyi waya da gwamna, da wasu manyan jami'an tsaro, cikin kankanin lokaci labari ya baza lungu da sako na k'asar har ma da kasashen dake da makfwataka da k'asar.
  Ana zargin an sace matar dan sarkin Adamawa, jikan sarkin Kano babban jami'in sojoji Captain Muhammad Ahmad Santuraki haka gidajen jaridu suka dinga wallafawa a shafukansu, nan da nan mutane suka dauka kowa na kokarin tofa albarkacin bakin sa.

_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D'aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
2/17/22, 09:45 - Buhainat: Halin Girma
37

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

*******�?
Cikin matukar tashin hankali Abba ya shigo gidan, bayan abinda ya gani a shafin BBC HAUSA, ya saka shi matukat kaduwa, idan har suna nufin surukin sa kenan, toh kenan Iman aka sace? Innalillah wa inna ilaihi rajiun,tashin hankalin da ba'a saka maka rana. Sauri sauri yake yana kokarin isa bangaren Abba babba, kiran Mummy ya shigo wayar sa,

"Shikenan." Ya furta

"Sun samu labari kenan, ta tabbata da gaske ne."

Ya sake fad'a sai kuma ya daga wayar yana kokarin daidaita tashin hankalin da yake ciki.

"Hello Abban Iman, abinda nake gani a news gaskiya ne?"

"Labarin da nake samu yanzu kenan, yanzu muke shirin tafiya dan samun sahihancin labarin, ki kwantar da hankalin ki, in sha Allah babu wani abu da zai faru."

"Innalillah wa inna ilaihi rajiun." Ta furta tana sakin kuka

"Zan tawo yanxu.."

"Sai kin zo." Ya katse kiran da sauri yana shiga ciki, a tsaye ya tarar da Abban yana kaiwa da komowa, yana shiga Abba Musa da Abba Kabiru suka shigo, babu wata magana da suka tsaya yi suka fice da sauri, suka dauki hanyar gidan sarki, dan anan ne kawai zasu samu gaskiyar abinda suke so suji, da Abba Musa yace su kira Muhammad din amma kuma sai suka fasa suka ga gwara su je din kawai ba lallai shima ya iya daukar waya ba.
  Haka sukayi, cikin tsananin tashin hankali suka isa gidan, bayan sun gabatar da kansu aka shigar dasu har in da maimartaba yake, babu wasu mutane sai makusantan sa, suna jimamin abinda ya same su haka bakatatan, sannan lokaci zuwa lokaci suna communicating da chan police station din, duk da babu wani labari akai, dan duk wanda yayi aikin yayi masifar kwarewa wajen gudanar da plan din nasa dan be bar duk wata hanya da za'a neme shi ba, amma duk da haka ba zasu karaya ba, zasu yi iyakar kokarin su dan ganin an samu so cikin kankanin lokaci.
   Labarin da su Abba suka samu yayi masifar sake daga musu hankali dan har kwalla sai da Abba yayi ba tare da kowa ya lura, yadda ake bada labarin rashin imanin masu kidnapping din nan kawai yake tunawa, ga iman sam bata da hayaniya, zata cutu ainun a wajen su sai dai fatan Allah ya bayyana ta cikin aminci da koshin lafiya.
  Suna zaune jugum kowa yana tunanin yadda Moh zai idan ya dawo, ya ci karo da wannan mugun labarin duk uban tsaron da yake ganin ya zuba a gidan sa, lallai addu'a ce kawai mafita a wannan zamanin, dan a duk in da mutum yake ba wai ya tsira daga sharrin su bane.
   Haka kawai yaji kamar bashi da lafiya, duk daukin da yake na zuwa gida ya ganta bayan tsawon lokacin sai yaji kamar duk guzarin sa na barin sa. Tun a airport din yaga kamar ma'aikatan na kallon sa, kallon da ya kasa gane na menene, sai kawai ya kyale hakan a wani dalili nasu da suka sani. Daga nesa ya hango motocin sa, suna jiran isowar sa, dora jacket dinsa yayi a saman kafadar sa ya shiga takawa zuwa wajen su dan basu ganshi ba. Sai da ya kusa daf dasu sannan suka ankara, duk suka taho da sauri kowa na kokarin riga dan uwansa isa, kayan hannun sa suka karba, aka bud'e masa motar ya shiga ya zauna.

"Muje mana." Yace ganin yaki tada motar

"I'm sorry sir." Yace sannan ya tada motar suka bi bayan su sauran. Sake neman layin Musaddik yake a lokaci daya yana neman nata amma duk magana daya ce, switch off, kansa ne ya daure sosai ta yadda za'a ce basu da charge a wayar su kuma tun jiya, be san me yasa ba, sai kawai yaji kamar babu lafiya.

"Me ya faru?"

"Na'am?"

"Kaji ni ai, what's going on!"

"I'm very sorry sir, bamu san yadda akayi hakan ta faru ba, amma we are trying our best kuma gaba daya k'asar ma."

"Ban gane ba, me kake nufi?"

"Kayi hakuri sir, in sha Allah za'a gansu."

" Nace maka me ya faru? Me kake nufi?" Ya fad'a a tsawace yana tasowa kamar zai dake shi

"Kayi hakuri sir, ana neman Madam da driver ta da House help din, tun jiya basu daw...**

" What!!!" Ya fad'a da karfi

"We are very sorry sir!"

" Wannan zancen banza ne, zancen wofi, menene amfanin ku? Nace menene amfanin ku?"
Ya harzuko sai kawai ya taka birki suka tsaya

" Ta yaya akayi tun jiya basu dawo ba, kuma babu wanda zai kirani ya fad'a min? Tun jiya fa!"

" Ohhh... Innalillah wa inna ilaihi rajiun, what's going on, me yake faruwa?"

A cikin tsananin tashin hankali yayi maganar, zuwa lokacin idanun sa sun yi masifar kadawa, wani abu me karfi yazo ya tsaya masa a makoshi, ya dinga jin kamar ya kamasu yayi ta bugu har sai sun fada masa yadda akayi suka yi wannan sakacin.
   Basu wuce gida kai tsaye ba, station suka wuce yana ta kiraye kirayen waya cikin karfin hali, ashe tuni labarin ya kai wa shugaban su har ma da abokan tafiyar sa amma kowa yayi masa kus, ransa yayi masifar baci, ga wani irin tashin hankali da yake ciki, yana tsoron wani abu ya faru da ita, ba zai taba yafewa kansa ba, ba kuma zai yafewa duk wanda yake da hannu a wannan al'amarin ba.
     Duk bayanan da ya kamata ya samu ya samu a station, abu daya ne basu da tabbaci shine in da suke, dan duk babu waya a tare dasu,sannan an cire tracker din dake hade da motar ta daina aiki tun daga cikin school din anan ne last location din motar.
   Jiri ne yaji yana kokarin kayar dashi k'asa, da sauri aka bashi kujera ya zauna yana dafe kansa, wayar sa da take ta faman kara alamun kira ya zaro yana duba number din, Ammi ce tun dazu take son su yi magana be samu dama ba, yace zai kirata amma kuma yasan ta kasa hakuri ne, kowa ya shiga tashin hankali da dimuwa kasancewar kuma har an kwana amma babu wani labari.
    Daga wayar yayi muryar sa a chan ciki, ya gaida Ammin ta amsa cike da tausayawa tilon dan nata, tasan yana da karfin zuciya da kokarin maida komai ba komai ba a tsawon rayuwar sa bata ga wani abu da ya gigitashi ya firgita shi ba, amma tasan dole ne wannan tashin hankalin ba zai iya rik'e shi ba, ba zai iya shanye shi ba ace matar ka na hannun bata gari, ba kuma kasan abinda zai je ya dawo ba. Lallashi da ban baki ta dinga yi masa, tana so ko yaya ne ya kwantar da hankalin sa duk da tasan ba lallai ba, yaji ta ne kawai amma bashi da sukunin nan, yana cikin wasiwasi da tunanin wanda zai aikata masa wannan danyen aikin, idan kidnapping dinta akayi saboda ransom yasan tabbas zasu neme su a tsakanin kwana uku, amma kuma idan ba dan hakan bane fa? Tsoro ne ya kara kamashi, ya mike da k'yar cikin wasiwasin abinda zai je ya dawo, baya fatan wani abu daban ya bullo wanda be taba tunani ko hasashe ba, a tunanin sa duk wani me matsala dashi ba zai wuce gidan su ba, Kamal da mahaifiyar su, wambai da sauran masu goyon bayan Kamal din, bayan su, baya tunanin akwai wani da wata matsala ta hada su da har zai iya yi masa haka.
   Tunanin sa ne ya katse, yana tuna abinda yake cikin flash din nan da ya bawa Musaddik, yana bukatar sake dubawa ko zai samu wata amsa a cikin video din, amma kuma ya kalla yafi sau nawa, sai dai kamar akwai wani abu da yake missing, be san menene ba, amma kuma zai koma baya ya sake dubawa sosai.
Tunanin sa ne ya tsaya akan Kamal, dalilin da ya kaishi bangaren sa har ya ajiye masa wannan macijin robar, babu wani abu da ya dauka bayan wannan ajiyar da yayi,tashi yayi da sauri

"Tracker ce!"

Ya furta ba tare da yasan a fili yayi maganar ba.

"Me kake tunani?" Shugaban yan sandan yace shima yana tashi tsaye

"Kwanakin baya an ajiye min abu me kama da micijin robar irin na wasan yara a adamawa,ina kyautata zaton tracker ce a jiki, ya akayi nayi missing step din?"

"Wa kake tunani?"

" Bana tunanin kowa, amma koma waye ne, yana da alaka da wannan case din."

" Ina macijin robar."

" Yana gida!"

" Nan ko adamawa?"

" Yana nan..."

"Ok muna bukatar shi ko zai taimaka mana wajen binciken mu."

" Shikenan."

Hannu ya mik'a masa

" Sai naji daga gareku."

" In sha Allah zamuyi kokarin mu."

" Nagode." Ya juya ya fice yana ayyana yadda zai fara bibiyar su tamkar yadda suka dade suna bibiyar sa suma.

" Kamal...! I'm coming for you."

A waje ya tarar dasu Abba da wasu yan tsirarin makusantan fada, sai Musaddik da yake zaune daga gefe, wani kallo Moh yayi masa suna gaisawa dasu Abba suna jajantawa juna, sai ya taso ya iso wajen su, ya tsaya daga gefe suka gama gaisawa, tafiya Moh yace su Abba suyi saboda daren da ya fara yi sosai, sallama sukayi masa akan zasu dawo gobe jikin kowa a mace suka tafi gida.

" Ina ka shiga?" Ya jeho masa tambayar bayan ya raka su Abba da ido sanda suke barin station din

"Ina gida, bansan me yake faruwa ba saboda an dauke min waya a masallaci bayan mun idar da sallah jiya, sai Mom ce take fad'a min wai meenal ta gani a media shine...."

"Is ok." Yace yana yin gaba

" Menene kake shirin yi next?" Ya bishi yana tambayar shi

" Me zanyi? Bayan case din yana hannun da ya dace, sai mu zuba ido mu gani."
Yayi maganar kamar be damu da abinda ya farun ba, gid'a kai Musaddik yayi ya cigaba da bin bayan sa ganin yadda yake sauri kamar zai tashi sama. Har wajen mota ya rakashi, ya tsaya daga baya maimakon ya shiga kamar yadda suka saba, alamar ya akayi Moh yayi masa ganin ya toge daga baya be shigo ba

" A mota nazo, zamuyi waya Allah ya bayyana ta Allah ya rufa asiri."

" Ok."

Kawai yace ya zuke glass din motar sama, suka bar wajen.

"His acting strange, amma tun yaushe?"

Ya tambayi kansa yana mamakin yanayin Musaddik din, share zancen yayi kawai ya lumshe idon sa, kirjin sa na masa wani irin suya.
A harabar masarautar suka tsaida motocin, aka bud'e masa ya fito ya nufi ginin bangaren Takawa, yanayin tafiyar sa kadai zaka kalla ka gane tsantsar damuwar da tayi masa dabaibayi, har be san kalar tunanin da ya kamata yayi ba, a wanne hali take? Me taci me suke mata? Duk shin yake masa yawo akai, a daren yau ba sai gobe ba, zai fara aikin da yake ta jinkirtawa tsawon lokaci yana jiran right time kamar yadda yasha cewa, sai dai yanzu yana ji aransa shine right time din.
Tun da ya shigo Takawa yake kallon sa cike da tausayawa, akwai sauran dauriya da jarumta a tattare dashi duk kuwa da babu kaso mafi rinjaye na karsashin sa, amma karya kake daga kallon fuskar sa ka iya tantance abinda yake wakana a zuciyar sa. Hakan ya dade yana bashi nasara akan duk mutanen da basa son shi, dan be basu kofar da zasu gano lagon sa ba, kuskuren sa daya, da yake kyautata zaton shi ya basu damar cutar dashi, shine yadda ya kasa boye son da yake mata, har ya zama musu wani tsani na ganin sun kaishi k'asa.
Ya jima da sanin Kilishi bata son ko ganin wulgawar shi, haka Kamal yana cikin jerin mutanen da zasu iya yin komai don ganin bayan sa, sai kuma wambai da wasu mukarrabn fadar, sai dai asalin kiyayar ba tashi bace, ta mahaifiyar shi ce da suke ganin an auro ta daga gari irin na kano, suna ganin kamar hakan zai saka kanawa su zama sune zasu mulke su. Sai dai idan ka tattara duk wadannan mutanen toh zaka samu basu da wata alaka da iman din, balle idan sun cutar da ita su amfana da wani abu, hakan ya saka kansa ya sake chunkushewa, ya rasa kalar tunanin da zai.
Zubewa yayi agaban Takawar, sai a lokacin yaji kamar an zare duk wani karfin zuciyar sa, yaji bashi da sauran katabus, yaji komai masa ya saki, sai ya dinga jin sa tamkar wani karamin yaron da aka dake shi aka kuma hanashi kuka.

"Karka yi kokarin shanye bacin ran da kake ciki muhammadu, ka fitar da komai zaka ji sauki."

Jan jikin sa yayi zuwa gaban Takawan, ya kwantar da kansa a saman cinyar sa.
Ya jima sosai a haka, kafin ya fara jin nutsuwa na saukar masa, sai a lokacin ya dago, ya zauna daidai.

"Sannu, babu abinda zai faru in sha Allah, zasu dawo lafiya lou."

"In Sha Allah."

***Babu wanda batan Iman be girgiza ba, hatta Mama da take ikirarin bata son ta sai da taji babu dadi, gidan ya cika duk kowa ya zo suna zaman jajantawa juna, zeenat dama ko da Habib ya kaita gidan su Bashir din achan suka same shi, yace su dawo zai zo da daddare sai su tafi, haka suka sake kwaso kafa suka dawo gashi shiru be zo ba har washegari sai kuma wannan bakin labarin.
Mummy da Mamma sun zo a ranar suma, suka sauka a gidan Iman din, kana kallon su kasan suna cikin tashin hankali, kowa baya cikin nutsuwar sa musamman Abba, da mahaifiyar ta wanda suka fi kowa kusanci da ita idan ka cire mijinta. Shi ba zaka taba gane ainahin yanayin da yake ciki ba. Tunda ya shigo gidan ya shige daki ya kulle kansa, ya dauko system din sa ya jona ta, yayi playing video din nan yana son ganin wani abu. Ya dade sosai a dakin, har ma suka manta da ya shigo gidan, ba laifi gidan da mutane wanda suka zo daga chan gidan sarki, sai su Ya Maryam da yan uwa dai na kusa. Duk suna jiran tsammani.

***Sosai take galabaita saboda aman da take ta faman yi, babu wani abu da yake zama a cikin ta komai taci sai ta dawo dashi, zuwa lokacin ta gama galabaita dan ko tashi bata iyayi komai sai dai Ummimi tayi mata. Sau biyu yana fad'a musu cewa gimbiya ta bata da lafiya amma suka yi biris da ita, suka kyaleta a cikin wahalar suna sane da labarin yadda ake neman su babu dare babu rana, duk wani moves din da jami'an tsaron suke suna sane dashi.
Sigari ya zuka ya fezar, sannan ya karbi sabbin layukan da ya saka aka kawo masa wajen guda hamsin, daya ya dauka, ya mik'a hannu ya dauki yar karamar waya a gefen sa ya saka, ya hau kai yayi murmushi ya shiga text message ya saka number Moh, ya rubuta

_"Ba kudi muke bukata ba, rayuwar ka muke bukata a matsayin fansa ga rayuka biyu masu muhimmanci a wajen ka, matar ka da cikin da take dauke dashi." _

Yana tura wa ya balla sim din, ya kyalkyale da mahaukaciyar dariya.

_" Let the game begins Captain MAS!" _




_ZAFAFA2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D'aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107



8
2/19/22, 19:58 - Buhainat: Halin Girma
38

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

****
Zaune yake a office din commissioner of police lokacin da message din ya shigo wayar, karantawa yayi yana kai karshe ya mike tsaye da sauri.

"Ya akayi?" CP ya tambaya shi yana kallon yana yin sa

"Akwai matsala..." Sai ya mik'a masa wayar ya soma zagaye a cikin office din cikin tsananin tashin hankali, idan har akwai ciki a jikin Iman toh lallai tana cikin halin tashin hankali, yasan yadda ciki musamman a watannin farko yadda yake wahalar wa yawa yawan mata suna shan wahala kafin ciki yayi kwari wasu kamar zasu rasa ransu saboda tsabar wahala. Ya take ciki yanzu? Me take ci?

"Akwai wani da kake da matsala dashi banda matsala ta cikin gida?"

CP ya tambaye shi bayan ya maimaita karanta sakon fiye da sau goma, har ya gano abu daya a cikin sakon, akwai kiyayye me zafin gaske tsakanin duk wanda ya turo sakon, duk wanda yake son ranka ba karamin kiyayye yake maka.
  Girgiza kai yayi ba tare da yayi magana ba,

"Idan ka gamsu da maganganun da mukayi, lallai muna da bukatar Kamal a binciken mu, domin idan har ka tattara bayanan baya da na yanzu zaka gane akwai wani abu da yake a boye a bayan dukkan cases din, case din ka da Laila, evidence din da ya wanke ka, sannan matar ka, zai iya yiwuwa wani ne da yake son ta tun ba yanzu ba, ko kuma wanda yake da matsala da kai ne amma shi da kansa yake son daukar fansa shiyasa har yayi kokarin wanke ka a baya, duk wannan tunani na ne, ban ce ya zama gaskiya ba, amma ina ji a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login