Showing 114001 words to 115235 words out of 115235 words

Chapter 39 - Halin Girma Hausa Novel Complete

russuna ta mika masa, ya hada da hannun ta ya rik'e tayi yar kara

"Auw, sorry baby."

Ya saki hannun ta zame shi tana marairaice fuska kamar zatayi masa kuka.

"Sai na rama."

Ta koma ta kawo kayan abincin ta jera masa a wajen, ya mik'a mata hannu ta daga shi, ta noke tana durkusawa da nufin zuba masa, rigar ta da akayi wa dinkin V-shape daga wuyan ya kalla yana cije lips dinsa.

"Bismillah."

Tace tana dagowa, ga mamakin ta sai gani tayi ya zuba wa kirjin ta ido, kunya ce ta kamata ta daga da sauri, ya waske yana zamowa

"Kayan nan yayi miki kyau"

Kin kallon sa tayi, ya dauki spoon din ya fara cin abincin yana kunshe dariyar sa.

"Ya jikin naki?"

"Alhamdulillah, da sauki. Yasu su Ammi?"

"Lafiya lou, suna gaida ki, tace zata kira ma ta sake duba ki kafin muje."

" Ayya, na samu sauki ma ai."

" Naga alama ai, har wata kiba kika kara da kyau, musamman ta nan..."

Ya nuna chest dinta da idon sa, kau da kai tayi tana hararar sa

" Kai ko?"

" Me nayi? Daga fadar gaskia? Allah baki gani ba."

" Uhummm."

" Da gaske fa nake, komai masha Allah."

Murmushi kawai tayi, dan ta lura jan magana yake so yayi, aikuwa ya cigaba da yi zuzutawa kyaun da tayi. Ita ma kanta tasan tayi kara wani irin kyau na ban mamaki. Sai da ya gama tas ya shanye lemon kwakwar nan sannan ya kama hannun ta suka haye saman, su Ummimi suka zo suka tattare wajen suka gyara aka saka turaren wuta.




Manage muna biki ne
  
2/27/22, 23:33 - Buhainat: *Hafsat Rano*
      _Halin Girma_
            *45*

***Washegari suka tashi cikin farin ciki da annushuwa. Yana shiryawa a gaban mirror ya kalle ta ta cikin mirror din tana ajiye masa kayan da zai saka yace

"Maganar school dinki, transfer zamu nema zuwa adamawa."

Tsayawa tayi da abinda take ta kalle shi

"Komawa zamuyi chan?"

"Yes, zamu koma gida, zan ajiye aiki na, na karbi Bubu."

Wani gingirim taji maganar, ta tsaya a wajen sakato tana son ta fuskanci zancen. Gabanta yazo ya tsaya yana murmushi

"Kina mamaki?"

"A'ah, ban gane bane I'm confused."

Dariya ya saka

"Don't be, ki shirya you are soon to be the wife of his royal highness!"

Wani shock tayi cike da mamakin

"Zaka karbi mulki?"

"In sha Allah, shine burin Bubu, zan cika masa burin sa kamar yadda yake so."

Da baya ta koma ta zauna a gadon kanta na mata wani iri. Matar sarki fa? Ta Yaya zata iya? Taya zata fara? Bayan bata san komai cikin sha'anin irin wannan ba, dafa ta yayi ya mik'ar da ita tsaya yana mata dariya

"Look at you, bafa yaki bane, normal ne kawai."

"Bansan komai ba ai, ta yaya zan fara? I'm nervous."

" Karki damu kinji? Muna tare ai."

" Allah ya taimaka ya bamu sa'a, Allah ya bamu ikon yin adalci da aikata daidai."

" That's my queen, abinda zaki ce kenan kawai, nasan zaki iya, I trust you."

" Banda fasa kai."

" Da gaske nake, nasan zaki iya handling kowanne irin situation."

Murmushi tayi, sai kuma wani tunani ya fado mata,

" Shikenan sai ka kara aure?" Ta samu kanta da tambayar shi cikin sanyin murya

" Aure kuma?"

" Eh ba sarakuna basa auren mata daya ba, wasu ma har da kwarkwara suke yi."

" Eh toh..." Ya mike yana saka links a jikin rigar,

" Me?"

" Ban dai san nawa zan ba ni ma, amma nasan zan kara uku na cike kinga hudu kenan."

Gabanta ne yayi mummunar faduwa, ta dinga kokarin karanta gaskiyar sa ta hanyar kallon fuskar sa. He looks serious, sai taji wani kuka na taso mata, tayi kokarin dannewa tana kokarin barin dakin gaba daya, riko ta yayi da sauri ya dawo da ita yana dariya

"Kishi?"

"Zanje k'asa na dauko abu ne." Tace tana avoiding kallon fuskar sa dan ji take kamar ta fashe da kuka

"I love this new side of you Baby, yayi miki kyau."

Haushi ne ya sake turnuke ta, wato shi wasa ma ya mayar da abun, fusge jikinta tayi, tayi gaba da sauri ta bar masa dakin, tana fita hawayen da take da rikewa suka zubo, shikenan ace a karaamin shekarun ta zata fara zama da kishiyoyi ba ma kishiya ba, har ga Allah bata da hayaniya da fitinar da zata iya zama dasu, ga hayaniyar gidan sarauta da shegen makirci wanda take tsoro tun farkon fari da ta gano waye ta aura. Tsaye take jikin staircase bata sauka ba, ya fito ya tadda ta a wajen, sai ta waske tana kokarin sauka ya chapko ta.

"Babu in da zaki sai mun karasa maganar mu."

"Ni fa babu komai, abu zan dauko a k'asa."

"Ba in da zaki." Ya juya da ita zuwa ciki, ya zauna ya dora ta a saman cinyarsa.

"Ashe dai ana kishi na haka."

"Nifa ba kishi nake ba, tambaya kawai nayi kuma ka bani ansa ai."

"Bari kiji, kinga bamu ne muke da ikon tsarama kanmu rayuwa ba, idan ma ka tsara tsarin Allah daban ne. Bani da sha'awar kara aure amma bansan me gobe zata haifar ba, karki damu let's pray for the best kinji? Muhammad dinki yana sonki sosai, wannan kawai ya isheki ki mikar da kafarki kamar kin hau jirgin sama mai ya kare."

Duka ta kai masa suka yi dariya a tare, a kalla dai ya fad'a mata iyakar gaskiyarsa, kuma hakan da yayi ba karamin burge ta yayi ba, taji ta kara son shi fiye da baya. Tare suka karasa shiryawa ya taimaka ya saka mata Alkyabba akan kayan ta, ya gyara mata sosai tayi kyau, ya ciro waya ya yi musu hoto me kyau, sannan suka fito, suka tarar da su Ummimi da sauran yan matan uku sun shirya tsaf suna jiran su, waje kuma fadawa ne suma a shirye an gyara motar. Hannun su sarke da juna suka sakko, duk suka zube suna kwasar gaisuwa, kafin su karasa an bud'e musu motar sai da ya bari ta fara shiga ta zauna sannan shima ya shiga. Sauran motocin su Ummimi suka shiga sai fada.
Sanda suka isa Takawa be riga ya fito zaman fada ba, sai suka wuce kai tsaye wajen sa, suka sameshi a wajen karatun sa tare da Fulani,a kunyace Iman ta gaishe su amma sai taga kamar basu damu ba, sun sake sosai kamar ba sarki ba, suka dan tsokani juna da muhammad kafin su barsu ita da Fulani zuwa bangaren ta, ba chan waje suka koma ba, wani corridor suka bi har chan din, tasha kallon haduwar wajen a hanyar su ta zuwa har suka dangana da chan sashen.
Har yamma likis suna gidan, bata sake ganin muhammad ba sai da yazo zasu tafi, ya shigo kamar bashi ba, hatta da takun sa sai data ga ya chanja ya zama irin na saraki masu ji da jini a jika, za'a ga hadadden young Sarki, ga kyau ga aji.
Sai da ya zauna fadawan suka fita sannan ya dube ta ya kashe mata ido ba tare da Fulani ta gani ba, murmushi tayi kawai ta saukar da kanta dan Fulani ta fad'a mata yadda tsarin sarautar yake, dole tayi takatsantsan da abubuwa masu yawan gaske, ta kuma ce nan zata dinga zuwa kullum tana ganin yadda abubuwan suke kafin tafiyar su.
Haka kuwa akayi, kullum sai sun fito da safe sai dare suke komawa kuma bata sake ganin shi wani lokacin ma sai dai su hadu a mota idan zasu tafi.

***Maganar Abba da Maman Iman ta





Rayuwa ta cigaba da garaw

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login