Showing 33001 words to 36000 words out of 115235 words

Chapter 12 - Halin Girma Hausa Novel Complete

ya dawo dasu gaba suka bada sauti kafin ya katse dariyar yana zama so serious.

" Abinda nake so kayi min, zaka ji daga bakin Musaddik, bana son kuskure ko kadan, komai Ina so ya tafi cikin tsari , Ina so gobe ka dauki hanyar Katsina, zan aiko maka da sako ka kaiwa Gimbiya Zeenatu, hakan zai sake goge shakku ko wani tunani akanka."

" Nagode ranka ya dade, nagode nagode."

" Karka damu, kai dai kayi abinda nace, bana son kuskure ko kadan!"

" Da yardar Allah zaka same ni da bin duk umarnin ka. "

Daga masa kai Moh yayi sannan yace

" Guy!"

" Yeah Captain!" Musaddik yace yana matsawa daga wajen da Bashir din yake

"Ka kula dashi sosai dan dan iskan kansa ne, duk da be isa ba, amma dai bana so a samu matsala har zuwa ranar daurin auren, watch him and report anything da be maka ba."

"Karka damu, babu ma abinda zai faru. "

" Yau nayi zaman fad'a, kamar nayi kuka wallahi, wannan yazo ya fadi yayi gaisuwa, wanna yazo ya ce makwafcin sa kaza, wannan suzo maganar aure, wannan ta kawo karar mijinta wannan ya kawo karar matar sa, maganar gado, kai abubuwan da mugun yawa, kamar na gudo nake ji, nasan iya zaman da zan Bubu ba zai raga min ba wallahi, har na fara ramewa. "

" Haka zaka hakura kayi abinda yake so, iyaye dole a bisu ayi musu yadda suke so. "

" Haka ne dama, shiyasa na matsu nayi auren nan nima na zama me yancin kaina, kasan aure fa yanci yake siyo ma da martaba ba komai Bubu zai dinga matsa min ba da zarar yaga nima na zama dan gari a harkar. "

" A harkar me? "

" Harkar auren mana, ina fita daga novice zai yanta ni, kwana kad'an kaji nima ana Daddy, Daddy! Wayyo I can't wait. "

" Kaifa yanzu baka da magana sai ta aure ko? Wannan sanyin ne ba komai ba. "

" Sanyi ai ya wuce kuma, ba zan kara yarda na sake wani sanyin a gauro ba wallahi, haba Malam ai an ji jiki kawai. "

" Dan air. " Musaddik yace yana dariya

" Yan air dai, Wa ma ya kaika ne? Gwara ni wallahi kowa yasan uztaz. "

" Nima haka ai. "

" Fadawa wanda be sani ba toh. "

" Toh ai idan har Moh uztaz ne toh tabbas ni sai da shehin malami, kai din? Ina dai tausayin yar mutane da zata shigo hannun tuzuru irin ka wallahi. "

" Naji karka bata min tunani, jeka zan neme ka anjima bacci zan."

" Hahaha, shikenan sai na jiki, angon Fatiti. "

" Musaddik.!!! " Ya furta da karfi

" Sorry sir, angon Fatima. "

" Zaka shigo hannu ne wallahi, sai na saka an samin kai frog jump. "

" Idan wannan ne ai na gaji da yi, a chanja wani punishment din dai Captain. "

Kashe kiran Moh yayi, yasan ya biye Musaddik sai su cinye lokacin suna abu daya, wurgi yayi da wayar gefe ya kwanta dan rama baccin da Bubu ya katse masa.
1/18/22, 19:54 - Buhainat: Halin Girma
     15

_*Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

_________________________

•••••••••�?

Kasa fitowa tayi, tana taraddadin yadda zasu karbe ta, ji tayi an bud'e kofar bangarenta, taji muryoyinsu a lokaci daya suna mata sannu da zuwa

"Yau ga Fatima,sannu da zuwa dota, sannu da zuwa."

Wata farar mata da a kalla zatayi sa'ar Mama ta fad'a tana riko hannun ta. Da wani irin yanayi take kallonsu su dukka, kowannen su kokari yake ya nuna mata kansa, mutum daya dage gefe tsaye ta harde hannayen ta a kirjin ta ta daga kai ta kalla, tun isowar su wajen ita kadai ce bata yi magana ba. Wani irin shock taji ta furta Mommy a tsakanin lips dinta, gyada mata kai matar tayi da sauri ta isa gareta ta rungume ta tana sakin kuka, bata chanja ba ko kad'an daga yadda take a hoton ta da take dashi tun na zamanin yan matantaka, duk da ganin ta da ita a zahiri kadan ne amma ko yaushe zuciyar ta na manne da hoton mahaifiyar ta.
   Tafi sukaji an saka daga bayan su, duk Kuma sai suka saka dariya har Iman din da kunya ta kamata ta sake shigewa jikin mahaifiyar ta tana jin wani irin son ta da kaunar ta.

"Muje ciki ko?" Babban namijin ya fad'a yana nuna musu hanya da hannun sa. Sakin Mom din tayi, matar farkon nan ta kama hannun ta zuwa ciki hanyar da ta ga sun fito dazun.
   A falo suka yada zango, kowa a cikin su kokari yake yaga ya nuna mata soyyayyar sa, da kallo kawai take binsu cikin mamakin dalilin da ya saka basa neman ta tsawon lokaci haka duk kuwa da soyayyar ta da ta hanga a tattare da family din. Tana da bukatar amsa saboda tasan yadda kowacce uwa take kulafucin danta musamman ita da aka dauke ta da karancin shekarun ta, tabbas a farko farko ta kan zo ta ganta tare da wani babban namiji duk kuwa da karancin shekaru basa barin ta tuna komai amma tabbas ta san anyi haka kuma Abba da kansa ya kara sanar da ita a wani lokaci da ta tambaye shi.
   Kamar an jeho su suka shigo su biyu, suka yo kanta da gudu macen ta rungume ta tana sakin ihu, namijin kuma ya durkusa a kusa da su yana dariyar farin ciki

"Welcome sister!" Yace bayan macen ta saketa ta zauna tana maida numfashi

"Welcome sis!"

Tayi saurin fad'a itama tana hararar sa

"Sannun ku."

Tace tana murmushi tana mamakin su,

"na riga shi ganin ki, na rigashi yi miki magana dan Allah ni kadai zaki so kinji? Dama kullum ina jin haushin bani da big sister sai wannan coconut head din , sai gashi na samu yanzu, I'm so happy wallahi, da k'yar na bari aka gama islamiyya yau wallahi."

"Amaani kin cika surutu wallahi, ai sai ki barta ta huta ko?"

" Tell her Mamma, wallahi kamar na bugeta yau din nan ta bani haushi."

" Kaifa ya sunan ka?" Ta tambaye shi

" Amaan." Amani tayi charaf ta rigashi fad'a sannan ta dora

"Nice hassana, shine husaini, na girme shi so nice babba."
  
Murmushi Iman tayi, so adorable yaran,

"Oya ku wuce kowa ya cire uniform dinsa kuzo muyi dinner, nasan Iman ta gama gajiya tana so ta huta"

Mamma tace tana mikewa

" Zayd, Ya Mubarak dinner na table."

" Ni sai nace gida gaskiya, I'm full."

Ya Mubarak yace yana gyara zama sosai. Kama hannun Iman Mamma tayi, suka wuce dining din tare da Zayd yana mata tambayoyi. Mommy na jinsu bata saka baki ba, dama kuma ita haka take da kara sosai, komai nasu Itace akai amma bata taba nuna musu iyaka akan nata, shiyasa suma duk wani abu da ya shafe ta toh sune a gaba gaba, sai ta koma gefe ta zama yar kallo. Bata da hayaniya kamar dai Iman koman ta a nutse takeyi musamman kuma abun da ya hadu da arziki sannan ga ilimi both boko da islamiyya. Kujera taja gefen Iman din da suka bar mata ta zauna daidai lokacin Amaan da Amaani suka dawo kowa ya sauya kayan sa zuwa na zaman gida. Amaani na kokarin fara surutun ta suka hada ido da Mommy, kallon da tayi mata kadai yasa taja bakin ta tayi shiru har suka gama babu wanda yayi magana.
   Falon suka dawo, a lokacin Ya Mubarak da Zayd suka yi musu sallama akan zasu dawo gobe kowa da family dinsa, har bakin mota Mommy ta rakasu ta dawo sai kawai ta wuce dakin ta, ta bar Mamma da yaran suna hira, ta lura da yadda Iman din ke jin kunya da rashin sabo amma kuma tasan wace Mamma ba zata taba barin ta ba har sai ta tabbata ta sake dasu, balle uwa uba iyayen magana su Amaani su kadai ma sun isheta.
   Kwanciya Mommy tayi farin cikin zuwan yarta na ratsa ta, wayar ta ta dauka ta kira number Abba, lokacin ya gama cin abinci kenan yana kokarin duba wasu papers dinsa a computer yaga kiran nata, tsaywa yayi da abinda yake yi ya daga.

"Nagode sosai IB, naga Iman fiye da yadda nayi tunanin ganin ta, hankali na ya kwanta dan na tabbatar da tarbiyyar ta, kayi ma maman tasu godiya dan Allah. "

" 'yaya amana ce a garemu da dole mu kula dasu da tarbiyyar su, domin dole ne Allah ya tambaye mu a ranar gobe kiyama, banyi komai ba face abinda ya zama wajibi na."

Ya fad'a yana jin chan kasa zuciyar sa da zata samu labarin abinda ya faru a zaman Iman din da Maman daku tabbas za'a iya samun matsala, abu daya ya hanata yin wani katabus akan maganar Iman din, tabbatar mata da yayi akan bata da matsalar komai, kuma tana hannu na gari.
    Sallama sukayi ta runtse idon ta, hasashen irin shirye shiryen bikin da zatayi kawai take, ba zata bari ta koma ba har sai tayi mata nata kalar gatan da zata tabbatar da ita din yar gata ce.
   Turo kofar akayi, ta daga kai ta kalli Iman din cikin rakiyar Mamma.

" Sai ki gudo ki bar mu? Gamu toh mun biyo ki."

" Na zata wajen Hajiya kuka yi ai."

" Munje chan din ma."

" Ok." Tace tana mikewa zaune.

" Bari na duba yaran chan, ina ga daga haka zan kwanta, sai da safe Iman."

Murmushi Iman tayi ta amsa sannan mummy tace

"Sai da safe Yaya."

Fita tayi ta ja musu kofa cike da farin cikin kwanan da ya da uwar zasuyi yau.

"Dawo kusa dani."

Dawowa tayi ta zauna daf da Mummy din, ta jawota ta dora kanta a saman cinyar ta, cikin tattausan lafazi tace

"Kin girma sosai Iman, nayi mamakin yadda kika kara chanjawa akan last da Dr. Ya tura min hoton ki, amma kuma naga baki da walwala sosai, ko rashin sabo ne? Ko kuma hakan halitta ne?"

Murmushi tayi me sauti, nutsuwa ta saukar mata, taji da gaske she's safe fiye da yadda ta taba ji a rayuwa ta, a hankali ta furta

"Babu komai Mummy."

"Shikenan, ki kwanta idan kika huta duk maganar da zamuyi sai muyi kinji?"

Ta shafa kanta tana murmushin. Daga kan ta tayi ta ajiye a saman gadon ta fita daga dakin. Wajen kayan ta, ta nufa ta ciro wayar ta, tasan ya mata magana a WhatsApp bata samu sukunin dubawa ba. Misscalls ta gani ta whatspp call sai messages dinsa da ya turo mata. Sakon ta fara dubawa ta,tabi kowanne tayi reply ta bar daya da yake tambayar ta size din undies dinta kunya na kamata. Godiyar kudin da ya bata tayi masa hade da addu'a tana turawa sai gashi yazo online, maimakon ya amsa sai taga yana kiranta, kasa dagawa tayi kunyar tambayar da yayi mata na dawo mata

_" Baby menene size din B da P?"_

Haka ya rubuto mata fa, kin dagawa tayi har ta katse ya sake kira ta kara bari ta katse,

_" Please dan Allah ki daga, kwana nawa banji muryarki ba? Sam na manta zan iya kiran ki ta whatspp call sai daxu, please ki taimaka ki daga inaso naji muryar ki wallahi."_

_" Ni dai muyi chatting."_

_" Ni dai ki daga, zan sake kira. "_

Kafin tayi reply sai ga kiran sa, ta daga da k'yar tanayin nesa da wayar. Ajiyar zuciya ya sauke da karfi

" Kin iya rigima wallahi, haka kawai sai anyi punishing dina ko? "

" Um um. "

"Toh naji, ya hanya? Ya me ya faru?"

Cikin zumudi tace

" Ina cikin farin ciki yau, komai ya tafi yadda ya kamata, kowa so na yake kamar zai goya ni. "

"Mum fa? "

" She's just like me, kamar ni take har I don't care attitude dinta, amma deep down she's super happy, na gani a idon ta. "

Dariya ya saka

" Alhamdulillah, nayi miki murna sosai sosai, Alhamdulillah. "

" Nagode sosai. "

" Yau kwana zakuyi nasan da Mum kuna magana. "

" Anya? Kila ko sai an kwana biyu. "

" Bari ki gani dai. "

" Uhum tohm shikenan. "

" Baki min replying dayan chat din ba, abinda na tambaye ki. "

Dauke wuta tayi gaba daya kamar bata ji ba, ya sake maimaitawa yana rik'e dariyar sa, ya gano kunya taji tunda taki daga wayar sa, bata san halin sa ba lallai, rage murya yayi sosai yace

" Dan Allah ki fad'a min Aunty zata yi min fad'a gobe idan nace ban tambaye ki ba, dan Allah. " Shiru tayi masa

" Please ki fad'a min, ko da yake ma zan iya chanka ai, bari muga... zasu kai size..."

" Innalillahi. " Tace tana zare wayar gaba daya ta kashe ta. Tuntsurewa yayi da dariya kamar zai fado daga gado, yayi saurin komawa chat din ya hau rubuta mata

"Sorry matar Muhammad, daga wasa sai ki yanke min waya? Toh ai ban gama jin muryar ki ba wallahi."

Tick daya ya gani alamar ta ma kashe datan gaba daya, gwada kiran ta yayi aikuwa yaji switch off.

Tsaki taja ta wurgar da wayar , ta rasa me yasa me maxa sam basu da ta ido, zata dade kuwa bata yi waya dashi ba. Samun kanta tayi da yin murmushi sai kuma ta hade fuska ta sake jan tsaki. Ya ma bata haushi gaba daya.

Har ta gama shiryawa ta jona wayar a charge amma bata kunna ba har lokacin Mum din bata shigo ba, gefen gadon ta kwanta cikin lallausan zanin gadon da yake kamshi sak irin kamshin da mummy din take, tana rufe idon ta, ta shigo rik'e da cup a hannun ta.

" Iman, kinyi bacci?"

" A ah." Tace tana mikewa zaune

" Yawwa ungo karbi kisha, fresh milk ce nayi miki warming dinta."

Karba tayi, tayi godiya ta kafa kai ta shanye tas, ta tashi da cup din rik'e a hannun ta

" Ajiye shi anan zan kira azo a fita dashi."

A saman fridge din jikin kofar ta ajiye ta dawo ta zauna tana so abinda tasha ya dan yi settling a cikin ta.

"Zo ki tayani duba wannan kayan."

Tayi maganar tana bud'e profile dinsu a cikin system din, gefenta Iman ta zauna suka hau duba wasu jewelries, duk wanda Iman din tace yayi kyau sai tayi starring dinsu, sai da suka gama tsaf sannan suka dawo kan wanda akayi starring din suka sake fidda guda biyar masu kyau sosai, biyu gold biyu azurfa sai daya fashion ne daga wani babban company, a take mummy tayi payment din da komai sannan tace Iman din taje ta kwanta zata karasa wani aiki.  
    Tana kwanciya bacci ya dauke ta  dama ta gama kurewa sosai tana lura da Mummy din bata so ta matsa daga kusa da ita ne. Cikin bacci tayi juyi ta jita a bayan ta, daga nan bata sake farkawa ba sai da aka kira sallah.

***Gaba yayo ya bar su a chan su karasa siyayyar abinda zasu siya dan yaga abin nasu bana kare bane, a Kano ya dira domin su karasa abinda zasu karasa da Bashir saboda yadda lokacin yazo sosai. A gidan sa ya same shi, suka jira Musaddik ya karaso suka fita zuwa wata unguwa da tafi kama da a kirata da unguwar talakawa kai tsaye, tunda suka shigo layin Moh ya tabbatar da zai samu yadda yake so, lallai Musaddik mugu ne na gaske, idan ba haka ba ya rasa unguwar da zai samo ya siya gida sai irin wannan unguwar. A daidai wani kofar gida karamin gaske suka tsaya, suka fito a tare wanda zasu gani yana tsaye yana jiran su, yana ganin su ya karaso bakin sa cike da murna ya gaishe su, sannan ya bud'e musu gidan yace su shigo.
   Siminti ne gaba daya tsakar gidan sabo yana ta kamshi, bashi da girma tsakar gidan sosai dan be fi yaci tabarma days da rabi ba, a gefe yar karamar rijiya ce saboda rashin ruwan unguwar.
   Dakunan guda biyu da suka kasance falle-falle ya bud'e musu suka shiga nan ma ko ina an masa fenti yana ta kamshi, babu abinda ba'a saka ba hatta karamin gado da kujeru an saka,da yar karamar tv babu batun fridge ko cooker gas balle azo maganar su AC da sauran kayan more rayuwa, kitchen din babu komai dama sunyi da nufin daga gida sai a kawo mata kayan kitchen suyi amfani dashi. Kitchen din karamin gaske ne dan mutum biyu ba zasu iya aiki a ciki ba saboda kankantar sa, balle a samu sukunin cika shi da kaya.
   Fitowa sukayi ya rufe gidan yana sake washe baki

"Ranka ya dade gidan yayi ko?"

"Yayi sosai yadda nake so, sai ka sanar musu ba sai an kawo kayan gida ba ,iya kitchen ya isa shima karsu matsawa kansu duk abinda babu zaka saka musu."

"An gama ranka ya dade, sai maganar lefe."

"Ana gobe daurin aure za'a kai, an gama hada komai ina tunani."

" Nagode Allah ya kara arziki."

Be amsa ba, yayi gaba ya fad'a motar yana kallon tsarin gidan, murmushi ne ya kwace masa, ya girgiza kansa yana ayyana yadda zuciyar Mama zata buga ko kuma ta kusan bugawa,yayi alkawarin shayar da ita mamaki irin wanda bata taba tunani ko hasashe ba.

  Kai tsaye wajen gym suka wuce, ya kwana biyu be motsa jikin sa ba, yana bukatar hakan saboda tafiyar da sukayi be samu lokaci ba. Dariyar shakiyanci Musaddik ya dinga yi masa, ya tsaya daga abinda yake yana hararar sa

"wai dariyar menene haka? Uhum?"

" Naga yadda ka dage kake ta faman daga karafu nan nan ne wallahi, kar dai ka illata musu yarinya wallahi, kasan dai kai din tsohon tuzuru ne da yaki auruwa. "

Robar ruwan da ya gama sha ya jefe shi dashi, ya goce ta fadi kasa yana sake tuntsurewa

" Ka kiyaye ni wallahi. "

" Anki din, daga fadar gaskiya?"

" Zan kamaka ne, naga kafarka a gida na wallahi. "

" Gidanmu dai. "

Towel ya ja ya goge gumin fuskar sa, ya biye wa Musaddik zai dauke hankalin sa ne ga abinda yake shirin yi. Wayar sa ya dauka akan dan table din wajen yayi dialing number ta, sai da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login