Showing 72001 words to 75000 words out of 115235 words

Chapter 25 - Halin Girma Hausa Novel Complete

nufi daki na dauko system dinka da kayi amfani jiya, naci sa'a na sameta a bud'e, na saka flash din a jiki nayi copying komai a wayata sannan na tura maka, na kuma kiraka da nufin nace ka duba amma kuma har ta gama ringing baka daga ba, a lokacin babu irin tashin hankalin da ban shiga ba, na dinga kaiwa da komowa a tsakani ina fatan ka daga wayar ko kuma ka duba sakon kafin lokaci ya kure. Ganin shiru shiru babu alamar zaka daga, sai na yanke shawarar zuwa da kaina, har fadar dan ba zan iya jurewa ba, har na dauki abinda zan dauka na fito na kuma kira wadda zata rakani, sai ga kiran ka."

Zaune ya tashi ya jere da ita akan kujerar, yana cigaba da jujjuya envelope din, yana son gano wanda zai aiko da sakon, duk iya tunanin sa be samu amsa ba, sai ya ajiye a gefe ya rungumota jikin sa yana murmushi

"Thank you so much Baby, nagode sosai da kokarin ki."

"U welcome."

"Ashe dai Ashe ana so na tunda har ake kishi na."

"Kishi kuma?"

"Ehen menene? Kishi ne mana, hadda kuka fa daxu da zan tafi, kamar wanda zai tafi filing daga!"

Sai ya tuntsure da dariya yana gwada yadda ta riko shi, turo baki tayi tana tashi daga kusa dashi

"Tayaka jimamin abun nake fa, aiko ba zan kara tayaka ba."

" Fadi gaskiya dai, kinga za'a kwace miki handsome mijinki, hankali ya tashi."

" Na shiga uku."

" Ba haka bane? Kinga hanci zur har baka, yarinya taga handsome guy tace idan bani ba sai rijiyar kusugu."

" Allah kaiko?"

" Ai gaskiya ne, ki rantse ba kishi bane."

Shiru tayi ta kyale shi, ta lura yana da so wasa da tsokanar ta, is like kamar ma yafi jin dadin sakata a gaba yayi ta tsokana, amma ka ganshi da sauran mutane kamar bashi ba.

   Bayan yayi sallar la'asar ne ya sake chanja kaya ya fita, lokacin yaran sojojin sa sun iso, dama sunyi waya akan suna hanya, yazo ya baza su a kofar shashen sa in da babu shegen da zai sake gigin shigar masa, balle har wani abu ya faru, duk da ma ba wani zama zai ba, sati daya zasu kara ya tattara yayi tafiyar sa Kano daga nan kuma yana tunanin ma k'asar zai bari, ya rasa yadda zai da abokan aikin sa da suka ce sun shirya masa kayataccen bikin sword crossing gashi har date din ya wuce sun sake rescheduling wata ranar, dole ya yarda dan sun kashe kudi sun kuma gayyaci manyan mutane, shiyasa kawai ya hakura yace zasu zo, daga nan sai suje su ga mahaifiyar Iman din daga nan suyi tafiyar su Kano Adamawa sai an Baba ta gani. Akwai tafiyar da zasuyi akan wani babban assignment daga wajen aiki duk da ba'a saka rana ba, amma baya so tafiyar ta zo nan kusa, yafi so sai sun je sun dawo ma, amma zai sake tuntuba yaji, yaji kuma iya dadewar da za'a yi idan yaga za'a shiga rayuwar sa zai iya fadawa dan baya son abinda zai saka shi yin nisa da Iman din, musamamn ya barta a gidan su ita kadai, be yarda da kowa ba, haka nan be yarda da duk wanda ya aiko da flash din nan ba, akwai wani hidden bayani a k'asa, ya riga yasan gidan su, ya san abinda za'a iya da wanda ba za'a iya ba,be kuma san iya adadin mutanen da suke son ganin bayan sa ba, duk da ya nuna bashi da ra'ayin saurata ko kad'an, amma ya tabbatar da akwai wadanda suke tsoron sauyawar ra'ayin sa, wanda suke gudun wani abu ya faru ba abinda suke fata ko suka tsara ba.
   A wajen Bubu ya shantake dan tare sukayi har sallar magriba yayi masa tas akan abinda ya aikata dazun akan sakon gwamna, duk da yaji dadi a kasan ranshi amma be nuna masa ba, sai ma fad'a da yayi masa akan kar ya sake, ya amsa da toh ba zai sake ba, sannan suka cigaba da hirar su irin wadda suka dade basu yi irin ta ba.
  Ana magriba Ammi ta aiko kiran Iman din, ta tashi cikin rakiyar hadiman ta suka nufi wajen Ammin in da ta tarar da wasu baki wanda daga gani masu muhimmanci ne ga Ammin, gaishe su tayi a ladabce bayan ta gaida Ammin, sannan Ammi ta gabatar da ita a matsayin matar Muhammad suma ta gabatar dasu ga Iman din, matar gwamnan Adamawa ce da yarta wadda Iman din ta lura da girman kanta, dan tun shigowar Iman din ko daga kai batayi ta kalle ta ba, tana ta danna waya tana cin chewing gum. Share ta ita ma Iman din tayi, suka cigaba da zaman shiru bayan tashin Ammi da matar suka shiga ciki suka barsu. Wayarta ta kara a kunne, tana yatsine kafin tace

"Moha gani a part din Ammi fa."

"Wallahi tun dazu ma, zaka shigo?"

"Owk ina jiran ka."

Satar kallon ta Iman tayi suka hada ido, sai ta dauke kanta kamar bata gane me take magana akai ba. Suna zaune a haka har wajen minti talatin kafin kofar part din ta bud'e, ya shigo yana kokarin daidaita kallon sa akan Iman da take zaune ta dayan bangaren.

"Ina chan ina jiranki ashe kina nan kin ma manta dani ko?"

Yayi maganar yana zama a hannun kujerar da take kai

"Nazo gaida Ammi ne, sorry na maka text baka gani ba?"

"Sai yanzu na gani fa, shine nayo nan da sauri na."

Dariya tayi, ta dan taba shi alamun kai ko? Gyaran murya suka je, ya kalli wajen

"Samha! I'm so sorry na manta munyi magana kince kina nan, gaba daya hankali na yayi gaba wallahi,."

"Uhm ba komai, ai kana tare da Madam."

"Yes yes wallahi kin ganta, Baby ga Samha my classmate."

"Allah sarki sannu."

" Sannu." Tace a gajarce tana dauke kai

"Samha this is my wife, baki zo biki ba zamu ciki tara."

Yak'e tayi

"Bana k'asar time din, naga Amarya Allah ya sanya alkhairi, Laila ta fad'a min ai."

" Kin gama mu wuce?"

Yace yana bagarar da zancen jin ta sako maganar Laila

" Ai bance ma Ammi zan tafi ba."

" Owk bari na fad'a mata." Ya tashi shiga ciki, ya barsu su biyu, murmushi ne a fuskar Iman, a kalla taji dadi da yadda muhammad din yayi dan ta gane sarai so tayi ta kunsa mata haushi shine har da kiran sa a gabanta. Be dade da shiga ba ya dawo yace ta tashi su tafi, suka fice suka barta da bakin ciki. Suna fita ta dauki waya ta kira Laila

" Wai baki dawo ba?"

" Na kusa shigowa ki jirani."

" Ina nan ina jiran ki, ashe rabon zanga kayan bakin ciki, haka Muhammad yake rawar kafa akan yarinyar nan?"

" Me yayi?".

"Kinga yadda ya narke mata kamar bashi ba, kinsan dai tsaurin sa ko? Toh wallahi a gabanta kamar ruwan sanyi haka ya koma, ni kaina baki ga yadda ya amsa min a sake ba wallahi, kamar fa bashi ba."

" Toh an fad'a miki haka ta barshi? Bari kawai na karaso muyi magana."

" Shikenan kiyi sauri please."

Suka ajiye wayar, jefar da tata Laila tayi a gefen ta, ta shiga jan tsaki a jere cikin bacin rai.


_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_*
_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107
2/7/22, 09:08 - Buhainat: Halin Girma
      29

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

******* �?

Tana daf da shigowa ta kira Samha tace ta wuce part dinta dan ba zata iya zuwa wajen Ammi ba, tashi tayi ta fita bayan ta saka wayarta a cikin purse dinta, taja kofar ta nufi wajen Laila din da ya kasance nata ita kadai kusa da na Kilishi. A waje suka hadu ita tana fitowa daga mota ita kuma tazo daidai bangaren, sallamar driver tayi yaran suka dauko mata kaya suka biyo ta, suka hadu suka rankaya ciki tare da Samha. Bayan sun zaune ne Lailan ta tuge mayafin kanta da yake dan yalolo da ta yane kan, ji taka kamar iska bata ratsa kan nata sosai shiyasa duk take jin ranta a jagule babu dadi, ga haushin abinda ya faru ga na karatun ta da take jin kamar ta rasa komai a yanxu.

"Kin ganki kuwa Queen, ya akayi haka?"

"Menene ma ba zaki gani ba, hmm wallahi bansan waye yayi min zagon k'asa ba, amma ko waye toh tabbas baya kaunata ko kad'an!"

" Kin binciki Hadimar nan? Ba kince ita kadai tasan da plan din ba."

Girgiza kai tayi

" Ba ita bace ba, someone very close to me ne, dan yadda ba kowa ke shiga part din nan ba, toh lallai wanda yake da direct access da part din ne."

" Lallai, gaskiya ko waye be kyauta mana ba, yanzu ya ake ciki?"

" Wai hakuri? Wallahi ban ba,kinsan yadda nake son Capt tun muna school haka shima kinsan kaunar da yake min ba kad'an bace, ba zan iya rayuwa da kowa ba sai shi, bayan haka kinsan matsala ta da Dr. Bryan Ford."

" Haka ne, toh shikenan yanzu menene next move dinki?"

" Har yanxu ban dawo daidai ba, I need time to recover nasan me zanyi."

" Shikenan, duk abinda zakiyi dai kiyi informing dina, zan baki shawara yadda ya kamata."

" I know I can count on you, Nagode Bestie!"

"DM!"

Tayi murmushi yana relaxing sosai akan kujerar, tana tunanin yadda zatayi amfani da Laila ta samu cikar burin ta!
Sai wajen tara sannan suka tafi, bayan Maman sun gama zantawa da Ammi, babbar aminiyar ta ce sama da kowa a kaf adamawa dan da ita ta fara sabawa lokacin da aure ya kawota, sannan yaransu ma tare suka taso ita tana da yara biyar compared to Ammi da take da guda daya tal...
Zuciyar ta fari kal sanda suka isa gida, ta san ko babu komai zata dinga samun duk information din da take so ta bakin Laila, tunda tayi masifar yarda da ita fiye da yadda ma ta yarda da uwarta mahaifiya. Bata da kirki ko kad'an idan har ka shiga gonar ta, amma kuma tana masifar ganin mutuncin Samha din, dan itace tafi mata kowa a yanzu, gani take ma babu me kaunar ta sai Samha din kawai. Ko Kilishi ta san ta Kamal kawai take yi ba tata ba, shiyasa itama bata wani sanar da ita idan zatayi abu sai dai daga baya, daga Samha sai amintacciyar hadimar ta guda daya wadda zata iya bada ranta fansa ga Laila din saboda tsabar biyayyar da take mata.
Wurgi tayi da tarkacen da ta debo daga mota tayi a saman gadon ta, ta kwanta tana kallon sama ba tare da ta cire dogon takalmin kafarta ba, murmushi take ita kadai duk kuwa da abinda Muhammad din yayi ya bakanta mata rai, amma kuma ta raina yarinyar da ya kira ta da matarsa, a shekaru ba wata babba bace haka ma wayewar rayuwar duniya sam bata cikin sahun amma kuma tana da nutsuwa a yanayin ta, da kuma iya handling abu dan yadda tayi da taji da wanda take waya ya matukar bata mamaki, kamar bata fahimci komai ba bayan sarai ta gane, kuma bata ko bi takanta ba ,ko ta tuhume shi ko ta chanja masa fuska sanda ya shigo, sai ma ta tarbi mijinta da fara'ar da ta mantar dashi komai da kowa.
Tashi tayi tsaye ta soma zagaye a tsakanin dakin tana jin kamar taje ta jawo ta da karfin gaske ta fidda ta daga gidan, duk yadda suka kai da wayewa amma ya tsallake su ya dauko wadda bata kai ko rabin ajin sa ba, adah Laila kawai take jin haushi amma yanzu na Laila ya daina damunta, dan tasan babu wani abu da zatayi sai da sanin ta, yarinya karama ce yanzu take neman zame mata ciwon ido.


***Suna shiga part dinsu tun daga kofa ya daga ta sama, ta saki siririn ihu tana kankame shi, da gaske taji tsoro dan bata yi tunani ba, sai ji tayi anyi sama da ita, kin ajiyeta yayi sai da ya kai karshen falon sannan ya zaunar da ita ya bita ya zauna a gefenta yana dariya

"Kin fiyaa tsoro Allah!"

"Ai it was unexpected shiyasa."

"Ba wani, tsoro dai kawai, ki yarda, you have to be strong, kinsan dai ance a wife of a soldier is a soldier!"

" Wasa suke suma wallahi." Ta saka dariya

" Haka dai aka ce." Yayi dariyar shima


"Yawwa... Dazu na gani a WhatsApp wai anyi calling off strike?"

" I can't say, bari na kira naji, amma zaki koma ne? Ko a samu wata school din daban?"

" Duk yadda akayi yayi."

" Owk toh bari naji." Yace yana ciro wayar sa daga aljihu, yayi dialing number wani lecturer abokin sa, suka gaisa sannan ya tambaye shi, baa gama daidaitawa ba amma dai akwai yiwuwar komawar nan kusa. Ajiye wayar yayi ya fad'a mata yadda sukayi

"Matsalar k'asar nan kenan, yanzu fisabilillahi fiye da 9month ana strike amma gwamnati tayi shiru? Shikenan karatun yara ya lalace akan wani dalili mara tushe, it's so unfortunate gaskiya."

"Wallahi har sai mutum ma ya gaji da zaman, babu dadi sam."

"Dole ai, Allah ya kyauta."

"Amin." Tace sai sukaayi shiru, chan kuma yace

"Bari muga idan basu daidaita ba, kawai sai mu chanja ko Base ne, ko kuma wata private uni din na Kano."

"Owk Allah ya zaba mana mafi alkhairi."

" Amin Matata!"

*** Tare suka shiga ciki bayan sun kammala duk abinda ya kamata su kammala a falon, zama yayi ya kunna system ya shiga aiki ita kuma ta wuce toilet dan ta watsa ruwa tazo ta kwanta. Sharp sharp tayi wankan ta fito sanye da rigar da ta cire , be kalle ta ba, har ta isa gaban wardrobe ta dauki wata mara nauyi iyakar ta kasan guiwa, dan duk sauran kayan da take dasu anan ba zata iya kwanciya dasu ba, idan ma ta saka tasan shi, zai iya yin karfa karfa ya hanata yayi amfani da damar yayi mata wayo. A gajiye take jin ta yau din ba wai don tayi wani aiki ba, bata san dalili ba gaba daya jikin ta ciwo yake mata, wankan da tayi take saka ran zai dan saka taji dama-dama.
Kallon ta yayi bayan ta sako rigar, yayi mata alamar tazo, ta taho ta zauna agefen sa, ya cigaba da aikin da yake na hada kan wasu takardu masu muhimmanci sosai, yana lura da ita yadda jikinta yayi sanyi sosai, jawo ta yayi bayan ya dan matsar da system din, ya kwantar da kanta a jikin shi

"Goodnight sweet dreams." Ya rankwafo yayi mata peck a kunci, lumshe idon ta tayi bacci na cin karfin ta sosai. Be san iya adadin awoyin da ya dauka a wajen ba, ya dade sosai har sai da ya fara jin bishi-bishi, sannan ya rufe system din, ya gyarata a hankali sannan ya tashi yana mika, alwala yayi yazo yayi sallah raka'ah biyu, ya lura da ko shafa'i da wutri da ta saba yau bata yi ba, be san wanne irin bacci take ji haka ba, dan har ya gama aikin sa ya tashi ko motsawa batayi ba. Taimaka mata yayi zuwa gadon ya kwantar da ita ya lullube mata iya kafarta, sannan ya kwanta bayan ya rage kayan jikin sa ya rage daga shi sai boxer kawai.
Cikin dare sosai taji ishirwa, irin wadda bata taba jin irin ta ba, tashi tayi ta lallaba ta fito bayan ta duba fridge din dakin ta tuna babu ruwa a ciki, ta manta kuma bata kawo ba dan bata bar kowa cikin masu aikin sun taba shigar mata dakin ba, iyakar su falo shima dan babu yadda zatayi ne amma ko yaushe suna BQ sai wani abu me muhimmanci sannan take kiran su.
A kitchen ta samu ruwan, tasha sannan ta dauko karamin katan na ruwan ta taho dashi. Falon yayi dim amma kuma akwai dan haske kadan da ya hasko ta corridor din kitchen da yake a kunne, kafarta take sawa a hankali tana tafiyar har ta kai tsakiyar falon, da yake falo ne katon gaske da sai kayi tafiya tsakanin kitchen da corridor din bedrooms din, motsi taji kad'an kad'an, tana matsowa yana karuwa har ta kusa kai wa corridor din abinda ta gani a wajen ya sakata daskarewa a wajen. Chak ta tsaya ta kwalla wata irin kara da ta tashi Moh daga bacci, ya mike a firgice yana kiran sunan ta, sai kuma yayi hanyar fita daga dakin da sassarfa kirjin sa na bugawa da karfi!




BIYAN BASHI ⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️😂😂😂😂😂
2/7/22, 19:06 - Buhainat: Halin Girma
      29

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

******* �?

Tana daf da shigowa ta kira Samha tace ta wuce part dinta dan ba zata iya zuwa wajen Ammi ba, tashi tayi ta fita bayan ta saka wayarta a cikin purse dinta, taja kofar ta nufi wajen Laila din da ya kasance nata ita kadai kusa da na Kilishi. A waje suka hadu ita tana fitowa daga mota ita kuma tazo daidai bangaren, sallamar driver tayi yaran suka dauko mata kaya suka biyo ta, suka hadu suka rankaya ciki tare da Samha. Bayan sun zaune ne Lailan ta tuge mayafin kanta da yake dan yalolo da ta yane kan, ji taka kamar iska bata ratsa kan nata sosai shiyasa duk take jin ranta a jagule babu dadi, ga haushin abinda ya faru ga na karatun ta da take jin kamar ta rasa komai a yanxu.

"Kin ganki kuwa Queen, ya akayi haka?"

"Menene ma ba zaki gani ba, hmm wallahi bansan waye yayi min zagon k'asa ba, amma ko waye toh tabbas baya kaunata ko kad'an!"

" Kin binciki Hadimar nan? Ba kince ita kadai tasan da plan din ba."

Girgiza kai tayi

" Ba ita bace ba, someone very close to me ne, dan yadda ba kowa ke shiga part din nan ba, toh lallai wanda yake da direct access da part din ne."

" Lallai, gaskiya ko waye be kyauta mana ba, yanzu ya ake

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login