Showing 84001 words to 87000 words out of 173829 words

Chapter 29 - Auren Kwangila Book 1 Hausa Novel Complete

11 Dec 2024

1150

ina qaryata cikin kuka
'Ummy qarya take wlh, son yaya take da aure shikuma yaqi saurarenta shine tabiyo ta wannan hanyar tayaya za'ace anty saudart karuwa ce? Tayaya yaya zaiyi zina? Wannan sherrin editing ne'

Dagaman hannu ummy tayi sannan tace ma suzy ta tafi zata nemeta saita tashi ta tafi.

Zuwa nayi kusada ummy nayita mata rantse rantse cewa qaryane, sharri ne

Batace mani komai ba sai shirun datayi na wani lokaci sannan ta umarceni na kira aunty saudart.

Kira biyar nayimata lafiyayye amma bata dagaba hakan yasa ta kiraka tace kuzo.

Saigashi kuna zuwa kuka gasgata abin"

Ta qarashe tana kifa kanta a dining table din.

Tsitt wurin ya dauka bakajin komai sai kadawar a.c dake wajen

Idanunshi sun kada sosai kamar gauta yayinda numfashinshi ke fita da nauyi har kana iya hango yadda qirjinshi ke sama da qasa.


Motsin dataji yasata dagowa daga kifa kan datayi taga shine ya miqe.

Sosai yanayinshi ya tsoratata hakan yaqara bugun zuciyarta.

Juyawa yayi batareda yace komaiba ya fice daga dining din dama falon gabadaya yanufi parking space cikin wani irin taku nashi wanda ban ta6a ganiba saiyau.

Wayarshi yaciro yana dailing din number yana bude motar.

Ba'a dagaba harta tsinke hakan yasa yasake bugawa lokacin harya shiga motar ya tadata.

Sai a kira na uku aka daga, lokacin harya fara reverse

"Fuck you! Ina kake!" Yafada cikin wani irin murya

Bansan kome aka fadamashi ba saiya sake cewa
"Damn you! Nace where the hell are you before I straggled you to death!" Yafada tsakankanin haqora, qirjinshi sai sama da qasa yake alamun zuciya

Bansan kome akace ba sai gani nayi yayi tilli da wayar seat din baya sannan ya bama motar wuta yafice daga gidan kamar zai tashi sama...✍️


Ummin fasihu ce🧚🏻‍♀️

👰🏻🤵🏻AUREN KWANGILA🤵🏻👰🏻
(Contract marriage)





Allah ka yayemana wannan annobar (covid19)🤲

Allah ka ji6anci lamuranmu, karka barmu da kanmu🤲



Story written by Ashaanty love💖
(Ummin fasihu)




064




Tsit dakin yayi bakajin komai sai qarar a.c dake aiki.

"Kutt... amma anyi tsinnaniyar yarinya, ciki? How and when?" Inji sadeeq cikin tsananin 6acin rai


Cize le6enshi na qasa Ashraf yayi yana kalkada kafa daga inda yake zaune, shikadai yasan abinda yakeji acikin zuciyarshi.


"Lallai dolene akoyama yarinyarnan lesson, ni wlh nama manta da ita ashe tananan tana bibbiyarku, abu mafi daure kai anan shine ina tasan cewa auren contract kukayi? There is something fishy here" yafada yana zagaye dakin

"I can't believe ummy kallon mazinaci takemin a jiyan nan, kallon me lallata yanmata, ni... ni Ashraf" yafada cikin wani yanayi

"Dolene mu nunamata kuskurenta Ashraf wanda nan gaba ko wuqa akasamata a maqoshi bazata qara gigin yima wani qaxafi ba, qazafin zina ba qaramin abu bane musanmman ma akan Saudart kamilar mace... baiwar Allah, allah kadai yasan yadda zataji idan labarin nan ya risketa"

Shiru dakin yasake dauka kowa da kalar tunanin dayake.


Ringing din wayar sadeeq ne ta katse musu tunaninsu.

Zaro wayar yayi ya duba sannan ya dago ta kalli Ashraf daya lumshe idanunshi.

"Ashraf.. ummy ce" yafada yana maida kallon ga wayar kuma

Bude idanunshi yayi yazuba mashi kawai batareda yace komaiba.

Ganin kiran zai tsinke yasashi saurin dagawa yakara a kunne.

Sallama yafara yimata sannan ya gaisheta a ladabce.

Bansan kome tacemishi ba saiya dago ya kalli Ashraf da shima kallonshi yake yace

"Eh gashinan ummy"

Magana aka sakeyi tacan 6angaren sannan yace
"Insha allah ummy"

Katse wayar yayi ya maido kallonshi ga ashraf dake kallonshi haryanzu.

"Ka tashi mutafi"

"Ina?" Ya tambayeshi ahankali

"Ummy ke nemanmu tace takira wayarka ba'a dagawa" inji sadeeq yana nufan closet dinshi don zaro rigar dazai daura bisa singlet din jikinshi.

"Ban iyawa, bazan iya fuskantar ummy ba ahalin yanzu" yafada yana dafe kan dake saramashi

"Meyasa? Yanzu ne the right time dazamu fahimtar da ita komai tun kafin abu ya girmama, yau zatasan komai so stand up dalla" inji sadeeq yana dora shirt saman singlet din.

"Allah kadai yasan kallon datakemin yanzu, i swear sai suzy tayi nadamar zuwanta duniya" yaqarashe yana huci

"Ai fadi ma 6ata baki, she really need to learn the lesson of her life, tashi mutafi"

Jiki asanyaye ashraf yatashi, besan yadda zekuma qara facing din ummy bayan yagama sanin kallon datake mashi.





*************************************


Zaune suke gabanta qasan rug kamar dai jiya kowanne kanshi sunkuye.

"Ina kiranka baka dagaba" inji ummy tana kallon Ashraf daya kasa hada idanu da ita

"Am..sorry, na..barota a mota ne" yafada kanshi still a qasa

"Wacece wannan?" Tafada tana turomashi wani pics gabanshi.

Dagowa yadanyi yana kallon pics din.

Hotonshi ne da suzy tadan shige mashi ajiki tana dariya shikuma yadanyi murmushi

Bazai manta ranar dasukayi hoton ba, ranar suna school ba'a dade da gama sheqa ruwan sama ba, garin yayi shar mutane sun fito waje sai daukar pics suke.

Saukowa shima yayi hannunshi riqeda wani qaton littafi shima yatsaya yana kallon students din

"My.." yaji an kwala mashi kira abaya.

ko be juyoba yasan itace

Qarasowa tayi gabanshi tana haki, binta yayi da kallo yadda kayan jikinta suka dan jiqe gashi tawani tsuqe cikin jumpsuit (biri da wando) babu ko mayafi sai yar hular datasa akai.

"Please muma muyi hoton..please" tafada zata riqe hannunshi.

Dan zamewa yayi yana harararta

"Look at you, wai bakijin sanyi ne kam?" Ya tambaya yana binta da kallo cikin kishi

Itama kallon kanta tayi sannan ta kwa6e fuska

"Am sorry zan chanza yanzu, please mu dauka ko dayane"

"No" yafada firmly yana juyawa zai tafi.

Bunshi tayi tafara mishi magiyar ya bari ko dayane suyi, ganin bazata barshiba yasashi hqr ta tsaya ta fiddo wayarta ta matso jikinshi kadan, bece mata komaiba don aqagare yake tayi din yatafi.

"Please kayi murmushi mana wannan hade ran dukna menene?" Tafada a shagwa6e

Tsaki yaja sannan yadanyi yaqe ta daukesu sannan yadan tureta daga jikinshi yana cewa
"Ai shikenan ko? Am going to the library, see yah" yajuya yatafi.



"Nace wacece wannan?" Muryar ummy tasake maidoshi daga duniyar tunanin daya lula.

Ajiyar zuciya yasaki sannan ya bude bakinshi dakyar

"Tsohuwar budurwa ta ce"

Shiru dakin ya sake dauka.

Rintse idanunshi yayi snnan yacigaba dacewa

"A school muka hadu kuma muka fara soyyaya... saidai tafiyarmu batayi wani nisaba muka rabu don kwata kwata batada kamun kai, ga shigar datakeyi anyhow dukda ina nuna mata rashin dacewar haka amma bata dauka..."

Shiru yasakeyi idanunshi still rintse yana sauraron bugun zuciyarshi.

"Mun..mun rabune ranar dana..."

Shiru yasakeyi hoton yadda ya taddata suna musayar hot kiss dawani qaton arne a wani class na dawomashi a qwanya.

"Sadda na.. naganta dawani suna.." sai yayi shiru yakasa idawa.

Ummy kallonshi take tunda yafara magana kuma haryanzu bata daina kallonshi ba

"Ummy na rantse ban ta6a zina ba, ko zanyi bazanyi da qazamiyar yarinyarnan ba, bansaniba.. bansan abinda aka fadamaki kenan ba, yes aurenmu da Saudart AUREN KWANGILA ne amma babu wata yarjejeniya makamanciyar wadda ta fadamaki a tsakaninmu da saudart, she's innocent.. hasalima..bada son ranta akayi auren ba, believe me ummy.. kinfi kowa sanin halin danki..."
Ya qarashe maganar muryarshi nadan rawa rawa.

"Ummy suzy shaidaniyace, sharri ta qullamasu saboda daga baya tadawoma ashraf yaqi sauraronta shiyasa ta buyomashi ta wannan hanyar, ummy ni aminin ashraf ne tare muke akoda yaushe, ko alokacin dasuke soyyayar ban ta6a ganin ya riqe koda dan qaramin yatsanta ba, hasalima bawani sonta yakeba duk ita taita cusa kanta gareshi" inji sadeeq

"Hakane ummy, nima nasan suzy farin sani, qawayenta kawai zaki kalla kisan ko ita wacece, tasha cusa kanta gareni don tasamu shiga awajen yaya akaro na biyu, tasha tazo taita rarrashina akan nabata number yaya amma naqiya, ga sa bikin su yayama saida suka fito qarara suka nuna baqincikinsu, magangannu kala2 babu wanda basu fadaba, ummy ko rantsuwa nayi bazanyi kaffaraba suzy qarya tashiryama yaya do n tasamu a liqamashi ita" inji baby itama fuskarta bayyane da 6acin rai.


Shiru dakin yasake dauka, kan ashraf haryanzu aqasa zuciyarshi na bugawa yanason jin wane hukunci ummy zata yanke.

Ajiyar zuciya ummy tasauke mai sauti sannan tace
"Kalleni Ashraf"

Shiru yayi yakasa dagowa, bejin zai iya dagowa su hada ido daita, wani irin nauyinta yakeji

"Nace ka kalleni"

Ahankali yadago ya kalleta saikuma yayi saurin kauda kai ganin ta kafeshi da ido.


"Nasani, nasan qarya take kuma sharri takemuku tun alokacin datake maganar, nasan cikinku babu wanda zai iya aikata abinda tace kun aikata, nidama ban zargeka ba ban kuma zargi daughter ba cos I trust you both"

Ajiyar zuciya ashraf yasauke mai sauti yanajin kamar ana lifting din wani qaton dutse a qirjinshi.


"Wacece saudart? Meya hadaku? Meye silar wannan auren naku na contract?"

Tambayar ummy tasauka a dodon kunnensu.

Kowannensu shiru yayi zuciyarsu na bugawa.

"Magana nike" tafada tana binsu da kallo.

"Ummy.."

"Shhhh.. barshi yayi magana, dashi nake ba kai ba, ka gayamin komai ashraf karka saki ka 6oyemin komai" tafada tana kallonshi.

Shiru falon yasake dauka, sai motsi yake da baki amma yakasa magana, yarasa ta inama zai fara.

"Saudart diyace ga SHAMSU KANKIYA...Tsohon aminin Abbu" yafada yana lumshe idanu.


Ware idanu Ummy tayi tana kallon Ashraf unbelievably

Bakinta na rawa tace "Shamsu qolo?"

Kada kai yayi zuciyarshi na suya.


"Nafara ganin appointment letter dinshi ne wattanin baya dasuka wuce, akan yanason rance don farfado da company dinshi dake neman collapsing... ina ganin sunan naga tabbas kamar nasanshi wani wuri, hakan yasa babi diddigin qundinshi ta internet anan naga shidinne bawani ba... nan take tsohon raunin dayaimana a zuciya ya motsa naji na tsaneshi fiyeda yadda na tsaneshi da, dafarko sai naso qin taimaka mashi amma sai wata idea ta fadomin, mezai hana inyi ramuwar gayya nima in dandana mashi abunda ya dandana mana?

Saina amsa buqatarshi nabashi ranar dazamu hadu sannan nakoma naita bin diddiginshi daga kan iyalanshi zuwa abokan aikinshi dakuma abinda ya tara da abinda ake binshi bashi.

Saura kwana daya mu hadu na gayawa sadeeq plan dina, dafarko yaso hanani yacemin inbarshi da allah kawai mai yiwuwa sakkayar allah ce yake gani tun yanzu amma sainaqi saurararshi don alokacin *WUTAR FANSA🔥*(littafina ba gaba insha allah) ke ruruwa azuciyata, na nunamashi bansan zancenba acewata don indauki fansa yasa allah yaturoshi wajena..dakyar nayi convincing din sadeeq ya amince min shima.

Ranar farkon dayazo...."

Nan yashiga bata labarin zuwan Alhaji shamsu nafarko company dinshi da yadda suka kaya sai kuma zuwanshi da biyu da yadda ya gabatarmashi da sharaddinshi dakuma amsar daya bayar na zaije ya shawarta.

Yakuma gayamata zuwan da saudart tayi da abinda yafaru tsakaninsu wanda hakan yaqara 6atamashi rai dakuma qara jin lallai saiya aureta donya koyamusu hankali gabadaya.

Yabata labarin yadda alhaji yaita fadi tashi har yasamu saudart ta yarda dakuma yadda aurensu yakasance har izuwa zaman aurensu ya gangaro zuwa fara aikinta a companynshi da abubuwan dayaita mata na muzgunawa ya gangaro zuwa tafiyarsu spain da zamansu acan dakuma yadda ta taimaka mashi wajen kama mayaudaran mutanen dasukaso karyashi har zuwa lokacin dasuka dawomashi da kudinshi da niyyar kawo qarshen contract din da abinda yafaru aranar dukda ya 6oyemata kissing dinta dayayi sannan ya gangaro har zuwan da sadeeq yace yayi gidansu jiya da barazanar makashi kotu datayi.


Shiru yayi yana sauke numfashi ahankali saboda doguwar maganar dayayi.

Dakin yayi tsit babu mai ko motsi yadda kasan babu kowa ciki.

"Na aureta ne badon komaiba saidon in rama abinda yayimana ko fiyeda hakan, nabashi rancen ne bisa tsarin zanyi shige da fice yadda komai nashi zai lallace yakasance babu uwar kudi ba riba ga kuma uban bashi.

Nikuma lokacin sai in nuna bansan zancenba saiya biyani inhar yanason diyarshi, sonake ya talauce shima yakoma bayada komai shima ya dandana abinda ya dandana inyaso shima zuciyarshi ta buga ya fadi mattac..."


Tasss! Sautin dayaji a qunnenshi ya hanashi qarasawa.

Kafin ya tantance meyake faruwa tasake daukeshi dawani zazzafan marin a dayan kumatun

Dafe duka kumatun yayi ta dogo da sauri yana kallon ummy daka tsaye sai huci take idanunta sun chanza launi.

Toshe baki baby tayi da hannu biyu tana ware idanu, tashin hankali qarara a fuskarta.


"Da hankalinka?" Ummy ta fada tana nunashi da yatsa manuniya.

"Nace da hankalinka da iliminka ka aikata wannan abin da ko jahili bazai aikataba?"

Kasa koda motsi yayi daga tsugunnen dayake hannayenshi dafe da kunci yana kallonta

Yakasa yara yau ummy ta dora hannu akanshi da sunan duka abinda bazai iya tuna when last tayimashi va tsawon rayuwarshi

"Fansa haukane?! Aure? Aure ka maida abin wasa? Abun daukar fansa? Ka rusa rayuwar yarinya da future dinta duk akan fansa?" Ta tambaya cikin zaremashi idanu.

"Ummy don alla.." katseshi tayi ta hanyar qamtsamashi nashi qason marin

"Yimin shiru! Harda kai? Atunanina kafishi hankali ashe taron zamuce ta tadda muje?!"

Dafe kuncinshi shima yayi yana sadda kai qasa

"Kaiga sarkin zuciya? Mai zuciyar qarfe dabakasan kabar mutum da allah ba? Akan banzar daukar fansarka ka janyo wanda bata jiba bata ganiba kana neman lallatamata rayuwa?! Kana..."

Kasa idawa tayi ta juya kawai ta dafe kanta kasancewar ta mai zuciya idan ranta yayi mugun 6aci maganama gagararta yake.


Ganin hakan yasashi saurin rarrafowa yana riqemata qafa.

"Ummy am sorry, am soo sorry"

Fizge kafarta tayi da karfi taja baya.

"You're not but you will be, kutashi kufita! Kutashi nace!!"
Tafada tsakankanin abinda ya toshemata maqoshi.

Saurin tashi sadeeq yayi amma ashraf ko gezau

"Kutafi nace kuma kai.."

Ta nuna ashraf

"Gobe kamar yanzu inason ganinka anan gidan da takardar saudart, banaso ko igiya daya ta rage atsakaninku"

Agigice ya dago yana kallonta yayinda zuciyarshi tayi wani mugun bugawa.

"Kaji nagayamaka! Ke tashi kitafi dakinki!"

Ta dakama baby tsawa.

Dagudu ta tashi tayi sama aguje.

Itama bin bayanta tayi tahaye sama batareda tasake kallonsu ba.

Dafe kanshi ashraf yayi cikin tashin hankali wanda tunda yake beta6a shigaba yayinda zuciyarshi ke bada wani hucin zafi kamar a oven....✍️


*WAYE ASHRAF?*

Ummin fasihu ce🧚🏻‍♀️

👰🏻🤵🏻AUREN KWANGILA🤵🏻👰🏻
(Contract marriage)


Allah ka yayemana wannan annobar (covid19)🤲

Allah ka ji6anci lamurranmu, karka barmu da kanmu🤲







Story written by Ashaanty love💖
(Ummin fasihu)



065




*WANENE ASHRAF?*




*AUWAL MUHAMMAD* Haifaffen garin wudil ne dake jahar kano.

Su shidda ne awajen iyayensu *MUHAMMAD JARIRI* wanda akafi sani da *MAMMAN* da matarshi *AMEENATU*

Yayansu shidda, maza hudu mata biyu.

Auwal shine d'a nafarko, sai ibrahim dake bimishi sai Nuradeen, sai Jamila, sai Zaharadini sai auta Halimatu wanda watanta uku a duniya ta rasu.


*MALLAM MAMMAN* manomine wanda ya riqe noma amatsayin sana'arshi, yanada rufin asiri daidai gwargwado don cikin noman yake samun abinci dazasuci harkuma su sayar.


Duk cikin yaranshi babu wanda yayi boko don lokacin ba'a wani bama karatun boko muhinmmanci ba.
Iyakarsu makarantar allo sai suwuce gona idan sun tashi don taimakawa babansu.


Jamila nada shekaru sha shidda akayimata aure dawani d'an abokin Mallam Mamman dake qauyen kakumi.

Auwal tun tasowarshi yakasance yaro mai hazaqa da zuciyar nema, duk yafi sauran yan uwanshi kazar kazar da qoqarin aiki.

Shiyasa sukafi shaquwa da Mallam Mamman don sosai yake taimakamashi a gona.


Auwal da kingin yan uwanshi sunada hadin kai ga girmama na gaba dasu suk qarantar taxarar dake tsakaninsu kau, hakan yasa zaman lfy, girmama juna da hadin kai ya wanzu a ahalin.


Koda sukadan qara tasawa sai suka amshi ragamar nomar yakasance mallam mamman ya sakarmusu komai yakoma yana hutawa.


Haka rayuwa tacigaba da kasancewa a wannan ahalin har watarana wani abokin mallam mamman dake zaune cikin garin kano yakawo mashi ziyara.

Anan su Auwal suka taddasu lokacin sun dawo daga gona, saida suka gaishesu sannan suka shiga cikin gidan.

Bayan sun shige ne abokin mallam mamman wato *MALLAM SANI* yayima mallam mamman tayin mezai hana yabashi daya daga cikin yaran yabishi kano ya hadashi da d'anshi sudinga aikin tuqin dayake.

Dafarko mallam be yarda ba, dakyar mallam sani yashawo kanshi yace zai shawarta.


Sai bayan isha'i sun zaune tsakar gida kamar yadda suka saba, samarin na zagaye da tray din abinci sunaci yayinda iyayen ke gefe.

Anan ne mallam mamman ya tada maganar da abokinshi sani yazomashi daita.

Nan take Auwal yanuna ra'ayinshi nason bin mallam sani don sosai yake sha'awar fita wani wurin nema.

Da farko mallam yaqi yara don ganin duk yafisu himma da qoqarin noma gashi shine babba amma ganin babu mai ra'ayin zuwa cikin qannen yasa ya yarda shima saida Auwal yadan sha wuya wajen shawo kanshi.



Cikin dan qanqanin lokaci suka shirya, ranar da mallam sani zai koma kanon yabiyo suka wuce da Auwal din.



Acan kanon mallam sani ya hada auwal da danshi mai suna Lawal wanda shima tsarar Auwal dinne suna daukan kayan gwari a mota suna kaiwa garruruwa.


Tun Auwal nabin Lawal a mota amatsayin karen mota har shima ya qware da tuqi shima aka bashi mota.


Alhamdulillah yana samu bakin gwargwado don duk qarshen wata idan zai ziyarci wudil yana zuwa masu da alhairi bakin gwargwado.

Suma su Nura suna itakar qoqarinsu a harkar nomansu idan kuma auwal yashigo garin yazo hutu wanda duk yawanci kwana hudu yakeyi haka zasu hadu sutafi gonar gabadaya.


Cikin dan qanqanin lokaci Auwal yayi suna, masu bada mottoci haya suka sanshi saboda gaskiyarshi da riqon amana.
Tun yana daukan kayan gwari har yakoma daukan kayan smuggeling irinsu shinkafa, man olga dadai sauransu.


Sosai yake samu da wannan sana'ar dob harya gyaramasu gidansu dake wudil dukda ba rusheshiba yayi akayi saboba saidai duk ya gyagyarashi an chanza sabon rufi na kwano sa6anin ba karare saikuma shafe da akayima gidan both qasa da bango.


A 6angaren qannenshi kau suma suna samun cigaba sosai don Ibrahim yabude dan shago yana siyarda kayan masarufi wanda yake hadawa da noma.

Nura kuwa yakama kiwo na dabbobi daban2 wanda shima hakan be hanashi nomanba.

Shikuma Zaharadini daga baya Auwal yatafi dashi kanon don sudinga aikin tare.


Auwal cikim tafiye tafiyenshi ba tuqin mota watarana yaje garin yola ya hadu dawata kyakyawar bafulatana mai suna *FATIMA* wanda ke kawo tallar nono da wara a inda suke sauke kaya.


Wasa wasa suka shaqu dajuna soyyaya tashiga tsakaninsu, ya kasance dik sadda yashigo garin suna tare kofar qaton shagon dasuke sauke kayan suna fira kamar karsu rabu hartakai yafison daukan kayan yola don haduwa da sahibarshi.


Ahaka suka qulla shekara daya suna soyyaya .

Awani dawowa hutu dasukayi wudil mallam mamman da yafara tsufa ya tarasu ya nemi kowannensu ya fidda mata yayi aure musanmman Auwal da Ibrahim kasancewar sune manya.

Anan ibrahim ya bayyana cewa shi dama akwai wacce yakeso mai suna *Raliya*, yarinya nitsatsiya babu wanda besantaba a garin wudil.

Sosai sukaji dadin za6in nashi nan aka maido akalar tambaya akan Auwal.

Shima beyi qasa a gwiwa ba ya bayyanamasu soyyayar dake tsakaninsu da Fatima yar yola.

Dafarko Aminatu (inna) taso taqiya acewarta saidai yasamu mata ansn cikin wudil ta aura amma daga baya ta amince bayan mallam mamman ya fahimtar daita shi aure rabone kuma matar mutum qabarinsa.


Nanfa magana takaiga manya, suma can 6angaren fatima sunso qiyawa amma daga baya sai suka amince aka saka rana lokaci daya dana Auwal da Ibrahim din.




Gaggarumin biki akayi a garin wudil.

Mallam mamman baqi yaqi rufuwa ana bikin yara har biyu yan gaban goshi.

Jamila itama ta halarci bikin alokacin 'ya'yanta uku.

Sosai akasha shagalin biki inda anan qauyen aka kawo fatima saida sukayi sati sannan suka koma cikin garin kanon awani madaidaicin gida daya kama haya.



Kwanci tashi asarar mai rai.
Haka Auwal yacigaba da harkarsa ta tuqi Allah na sanyamashi albarka yana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login