Showing 108001 words to 111000 words out of 173829 words
ya dawo dasu
"Wai bazaku fitoba sai an kabbara?"
Juyowa duk sukayi, tashi ashraf yayi shima yya jera da sadeeq kanshi qasa suka fito suma.
Haka suka dunguma suka nufi massalaci dake kusada gidan don gabatar da zuhr.
A 6angaren saudart ma kasa hada ido tayi dasu, haka dai ta kaisu sama ta nunamusu toilet don daura alwalla kafin su fito kau ta shimfidamasu sallaya.
Suna fitowa itama tashiga ta dauro nata alwallar ta fito itama ta shimfida wata sallayar abaya ta tada nata sallar.
Koda tagama suma tuni sun gama saidai ta kasa dagowa daga sunkuyen da kanta yake don ba qaramin kunyarsu takejiba sai mutsu mutsu take cikin hijab.
Duk sun lura da yanayin datake ciki amma suka basar suka shiga janta da fira.
A kunyace take amsa masu wanda yawanci amsar murmushi ne don jitake kamar ta nutse don kunya.
Ahankali ummy ta dauko maganar aurensu inda take nusar daita cewa karta yarda ta cuci kanta, karta yarda tayi za6in da zai cutar daita, tasan komai kuma bazata ta6a ganin baqinta ba idan suka rabu da ashraf, hakan bazai chanza kasancewarta diyarta ba.
Itadai saudart bata iya dago kanta ba bare ta amsa, jitake kamar ta nutse don kunya.
Bayan sallar duk suka fito daga massalacin suna tafe suna fira cikin raha da jindadi.
"I can't still believe A.A dana ne, d'an aminina kuma my in-law"
Duk murmushi sukayi yayinda ashraf yaqara sunkuyar da kanshi qasa yanajin kunyar yadda daddy ke riqe da hannunshi.
Tunda akace shine dan Alhaji auwal yaketa nan nan dashi don kusadashi ma ya tsaya wurin sahun sallah.
Shikau ashraf jinshi yake so uncomfortable, yakasa koda hada idanu dashi jiyake kamar ya 6ace ya huta.
"Kai alhaji yaushe ka ta6a ganin father-in-law da son-in-law na haka? Ina kunyar?" Inji abba yana dariya.
"Ku kuka santa, ni nan dana ne kuma aboki ko son?" Yafada yana kallon ashraf dake sinne kai kamar wata amaryar qauye
Jiyayi kamar ya nutse hakan yasashi qara sunkuye kai
Dariya duk aka dauka kawu ibrahim yace
"Atoh da alama shi bemanta da ita kunyarba"
"Hmm bawani jinin fulanawa ne dake yawo ajikinshi kawai ba komai ba"
Haka dai suka shigo gidan suna hira cikin raha da dariya shikau ashraf kanshi a qasa yake biye dasu sadeeq abayanshi sai faman danne dariyarshi.
Wannan karon saida duk suka dan ta6a abin motsa baki ana fira cikin raha da dariya idan ka cire ashraf da saudart da suka kasa dago kansu sai sadeeq dake gefen ashraf shima yanna tsokanar ashraf qasa qasa.
Sau biyu idanun saudart na hadewa dana ashraf duk dagowarta hakan yasa bata qara dagowaba.
Saida komai ya lafa sannan suka fara gabatar da abinda ya tarasu tun farko, anan kawu ibrahim yafara bada labarin asalin aurensu A.A da dalilinshi na qirqirar auren duk don ya dau fansa akan abinda yake zargin daddy dashi be 6oyemasu komaiba har zuwa yanzu dasuke zaune.
Shiru falon ya dauka, mammaki ne sosai yacika saudart don ko da wasa bata ta6a kawowa ranta Ashraf nada wata manufa gameda aurensu ba, she thought kawai irin mutanen nan ne da basu yarda suyi taimako batareda wani abu in exchange ba don ko rashin mutuncin dayakema daddy gani take kawai saboda giyar kudi dake dibanshi ne don tasan wasu mutanen kudi na maidasu rude brats. Ashe shi revenge yake taking.
Ahankali tad'an dago idanu ta saci kallonshi taga kanshi na akasa don tunda akafara maganar yakasa kwakwarar motsi, jiyake kamar ya 6ace ya huta.
Sauke idanunta tayi ahankali abinda takeji gamedashi naqara hauhawa yayinda kwakwalwarta tashiga tariyomata cin mutunci dayaimata ita da daddy.
Daddy kau a 6angarenshi shima yayi mammaki amma daga baya kuma saiya saki murmushi yana kallon ashraf daya wani raku6e waje daya kamar wanda ruwa ya cinye.
"Allah sarki son, ba laifinka bane, rashin sanine kuma rashin sani yafi dare duhu, konine a matsayinka idan banyi fin hakaba to iya abinda zanyi kenan, besides nima da nawa laifin da banda kwadayi da bazan yarda da hakanba da na hango wani abu makamancin haka amma lokaxin idanuwana sun rufe nakasa hango komai, Am sorry for putting you through pain son"
Qara yin qasa ashraf yayi dakai yana jin wani matsanancin kunya jiyake kamar ya ruga aguje yabar gidan gabadaya.
"Muhammad?" Daddy yakirashi da ainahin sunanshi
Kasa dagowa ashraf yayi
"Look at me son, ko baka yafemin bane?"
Girgiza kai yayi ahankali still be dagoba.
"Come closer son"
Shiru yayi yakasa motsawa, kowa na falon shi yake kallo harda saudart dake kallonshi ta qasan ido tanajin wani daci daci a maqoshinta.
Ahankali ya rarrafo gefen daddy ya zauna kanshi sunkuye
"Ashraf?"
"Am...sorry daddy, please forgive...me" yafada ahankali still kanshi qasa.
"Ni bakamin komai ba,if am in your shoe i'll behave exactly the way you did, am sorry too, forgive me too"
Shiru dai kawai yayi still kanshi qasa.
Ganin babu mai niyyar sake magana acikinsu yasa kawu ibrahim gyaran murya ahankali sannan yace
"To alhamdullilah, godiya ga allah subhanahu wata'ala daya sa muka fuskanci juna sosai ayau wanda idan kukayi duba ga wannan abu zakuga tsararrene wanda ubangiji ya tsara domin koyarda kowanne cikinmu darasi.
Nafarko da Alhaji shamsu be nemi taimako a kamfanin A.A ba da haryanzu muna cikin duhu gameda abinda muke zarginshi akai na sanadin margayi.
Nabiyu da Ashraf be dage akan daukar fansaba da bamuyi wannan zaman ba na yau
Da alhaji bai aminta da aurennan ba da haryanzu muna acikin duhu
Saigashi abun kamar a film, abinda yafaru shekara da shekaru anzo an warwareshi yanzu bayan babu wanda yata6a kawowa ko a mafarki zamu sake haduwa a duniyarnan.
Dama ance kana naka Allah na nashi gashi sanaddiyar auren nan na contract tsohon zumuncinmu zai cigaba daga inda ya tsaya insha allah.
Don koda auren nan ko babu auren nan bazamu ta6a watsar da zumuncinmu ba a karo na biyu kuma muna fatan insha allah zumuncinmu yacigaba da dorewa har qarshen rayuwarmu har izuwa cikin aljanna insha allah"
Juyowa yayi yakalli saudart da kanta ke qasa yace
"Haqiqa 'yata kin kasance diya abar alfahari ga kowa'anne iyaye, abun kwatance ga alumma, ki kasance mai biyyaya da tarbiya ga girmama na gaba dake.
Da watace taga yadda Ashraf ke wulaqanta mata iyaye da ko kallo nashi iyayen bazasu ishetaba amma ke kin kauda kai kin rungumi iyayenshi da danginshi kamar naki, kin kawo haske a rayuwarsu gabadaya kin ajiye komai kin taimakeshi a lokacin da yake buqatar taimako kuma ke kadaice keda ikon yin haka alokacin batareda kinyi la'akari da abubbuwan dayaimiki kuma yake kan yimaki alokacin, gaskiya you have a good heart kuma allah ne kadai zai iya saka maki, kin jure abubuwa dayawa saboda farantama mahaifinki rai haqiqa ke yar aljanna ce insha allah"
Dan dakatawa yayi yana kallonta kafin kuma ya cigaba dacewa
"Saudart you've endure enough, kin juri abubuwa dadama akan wannan auren bazamu tilastaki da cigaba da zaman cutuwa ba.
You have a choice, aurennan zai dorene bisa ga kalar amsar da kika bada, karki cuci kanki daughter, ada kin amince ne saboda daddynki yanzu kuma nobody is forcing you, your fate is in your hand kuma munaso ki sane ko da aurennan ko babushi babu abinda zai canza alaqarmu daku don haka choose wisely daughter"
Shiru dakin ya dauka all eyes on Saudart while ashraf kanshi a sunkuye zuciyarshi na bugu abnormally.
"Daughter? Ni mahaifiyar ashraf ce amma dana ji abinda yafaru the first thing dayazo bakina shine yabani takardarki don nasan you've suffered enough, ba don su kawu ibrahim sunsa bakiba akan abari aji ta bakinki da wlh bazamuzo nan ba saida takardarki, ni na haifi ashraf kuma nasan halinshi idan ya tsani abu don haka karki cuci kanki don farantawa kowa saudart, ki tuna this is your life bana kowaba, idan kin cigaba da zama dashi don wani to kanki kika cuta, just pour what's in your heart daughter, fear nothing"
Shiru dakin yasake dauka saudart ko motsawa batayiba shima ashraf haka saidai kowanne bugun zuciyarshi ya chanza sosai.
"Saudart?" Kawu ibrahim ya kira sunanta ahankali.
Ahankali ta dago kanta ta kalleshi saikuma ta maida kanta qasa
"Zaki cigaba da zama da Ashraf a matsayinshi na mijinki daga auren contract zuwa auren gaske na har abada koko ya sawwaqe maki Allah ya hada kowa da abinda yafimishi alhairi? Remember your fate is in your hand" yaqarashe a tausashe.
Tsit falon ya dauka kowa idanunshi akanta, zuciyoyin kowa na qara bugu musanmman na goganku😄 sadeeq kau harda share zufar daya tsatsafo mashi a goshi😆
Motsi tafara yi da baki amma maganar taki fitowa kallo daya zakamata kasan bata cikin nutsuwa.
Dafa kafadarta ummy tayi ahankali tace "keep calm daughter, just pour your mind"
Lumshe idanu tayi tana sauke ajiyar zuciya yayinda komai daya faru daga haduwarsu da ashraf har kawo yanzu yashiga yawo a kwanyarta.
Ahankali ta rufe idanunta ta bude bakinta dakyar tace...✍
Kusani a prayers fans👏
Ummin fasihu🧚🏻♀️
👰🏻🤵🏻AUREN KWANGILA🤵🏻👰🏻
(Contract marriage)
Story written by Ashaanty love💖
(Ummin fasihu)
079
Ahankali ta rufe idanunta ta bude bakinta dakyar tace
"Allah yasa hakan shiyafi alkhairi" tafada cikin sanyi sosai
Tsiit falon ya dauka na wucin gadi don kasa gane inda maganarta ta dosa sukayi.
Kawu ibrahim ne yayi karfin halin cewa
"Me hakan ke nufi daughter?"
Shiru tayi kanta aqasa takasa cewa komai.
"Kinga saudart ki bude baki kiyi magana, this is something serious" inji Abba
Shiru tayi har lokacin kanta aqasa sai idanunta dake forming din hawaye.
"Saudart kin yarda xaki cigaba da zama da Ashraf a matsayin matarshi ta sunna na har abada?" Inji daddy yana kallonta keenly trying very hard to read her mind
Gyada kai tayi ahankali batareda ta dagoba.
"Ba maganar kurame zakiyi ba, open your mouth" inji abba
Ahankali ta bude bakinta trying very hard to control her emotion
"Eh abba, na....amince"
Shiru falon yadauka kowa na kallonta unbelievable
Babu wanda amsarta beyi shocking ba don basu ta6a tsammanin wannan amsarba.
Ashraf kau kasa gasgata kunnuwanshi yayi, amsarta kawai ke eoching a kunnuwanshi jiyake kamar amafarki.
"Karya kike saudart! This is not coming direct from your heart" inji ummy cikin dan daga murya
Kasa dagowa saudart tayi bare ta lalubo amsarda zata bata.
Yes, amsarnan is not directly from her heart don babu abinda zuciyarta ke muradi kamar rabuwa da ashraf, she hate him and today she hate him more, jin cewa duk abubuwan dayake musu fansa ne yaqara dagula mata lissafi yasata jin bazata ta6a yafemashi ba, yasata jin qara tsanarshi a zuciyarta.
Ta tsaneshi ta tsaneshi saidai wannan kalmar saidai ta tsaya a cikin zuciyarta, jitake inama tana iya furtawa, tasan furtawan kawai zai rabata dashi har abada amma kash! Bazata iyaba.
Ada babu abinda take buqata irin wannan damar, damarda xata rabata dashi na har abada, kullum cikin addu'a take allah ya kawo rabuwarsu, yarabata da wannan mutumin da babu digon sonshi ko diss a zuciyarta, saigashi damar tazo amma wani abu yayimata katanga da samun cikar burinta, tana ji tana gani zata amince da abinda xuciyarta bataso, xata zauna zanan cutuwa, xata za6i rayuwar qunci da baqinciki.
"Saudart look at me!" Ummy ta umarceta.
Saida tayi iyakar qoqarinta na ganin ta maida hawayen dake maqale a idanunta tundaxu taqi basu damar sauka don tasan sune zasu fallasa asirin zuciyarta sannan ta dago tana kallon ummin
"Tell me, wake tilastaki yanzu? Ni da ke munsan ba gaskiya kike fadi ba"
Ahankali tashiga girgiza kanta trying so hard to control herself
"Ummy babu mai tilastani, this is coming directly from my heart.."
"Karya kike" ummy ta katseta
"Saudart kinsan abinda kike shirin yi kuwa? You are depriving yourself your right" tafada wholeheartedly
"No ummy, inayin abinda kuka sanine, kunce infadi ra'ayina batareda nayi considering din komai ba and that's exactly what am doing, it's my choice ummy" tafada calmly yayinda zuciyarta ke fadin akasin haka
Shiru ummy tayi tana kallonta kawai, kallo ne na mammaki chakude da tausayi, tasan karya take, gashinan tana hango hakan acikin idanunta, meyasa zata za6i quntatawa kanta, meyasa xata za6i zaman cutuwa? Zaman da babu digon so aciki?
Shidai ashraf haryanzu yakasa dagowa kuma haryanzu jinshi yake kamar a mafarki, kai mafarki ma ne, yarinyar da ta tsaneshi, batada wani buri daya wuce rabuwa dashi zata amincewa cigaba da zama dashi na har abada? This is a dream, mafarkin da bazaiso ya farkaba yanzu.
Sadeeq ma was totally shocked, kallonta kawai shima yake yana son hango bakin gaskiyarta ta cikin idanuwanta.
"Saudart?" Kawu ibrahim ya kirata.
Ahankali ta dago kanta daga sunkuyen dayake ta kalleshi sai kuma ta maida kan qasa.
Daddy kau sai kallon diyar tashi yake yana karantarta
"Meyasa kika amince da cigaba da zama da Ashraf?" Ya jefa mata tambayar yana kallonta.
Shiru tadanyi na yan daqiqu sannan ahankali tafara cewa
"Saboda aganina dakuma tunanina wannan auren hadine na Allah, akwai manufofi da dama acikin wannan auren, ta dalilinshi abubuwa da dama sun warware, zumuncinda ya dade da watsewa yana neman cigaba ta dalilinshi, wannan ba komai bane face ikon allah" ta qarashe maganar asanyaye
"To amma Ashraf fa? Kina sonshi? Shifa aure ba'a zamanshi akan wani dalili kuma baya dorewa idan babu soyayya, wadanda akayi na soyyayama yaya aka cika bare wannan wanda dalilinshi bekai hujja ba, gashi shi da kanshi yafadi abubuwa dadama dayamiki marar dadi a dan zamanku, kina ganin baxaki dinga tunawa ba duk in kin ganshi?"
Hadiye yawun daya tararmata a maqoshi tayi sannan tabude baki dakyar, allah ma yasan dauriya kawai take amma ita kadai tasan me takeji acikin zuciyarta.
"Kawu kamar yadda nafada, qaddara dakuma ikon allah ne ya hadamu, Ashraf... ya bijiro da wannan abun ta dalilin fansar dayakeson daukane, da ba'ayi auren ba akazo har yanzu da haryanzu yana ciki da daddy, yakuma yimana abubuwane bisa rashin sani, da yasan gaskiya nasan baxaiyi hakaba, so kuma allah kesawa azuciyar mutum ya musanya qiyyaya da so alokaci daya kuma... hakan na iya faruwa" ta qarashe zancen taba lumshe idanu, maganarnan datake ita kadai tasan yadda takeji, sosai zuciyarta ke zafi yayinda ita kanta tasan qarya take shirgamasu don batajin akwai ranarda zata ta6a kallon ashraf da sunan so.
Tunda tafara magana dama ashraf ya dago yana kallonta, he can't believe she's saying all these. Atunaninshi yanzu zata qara tsanarshi ne dataji cewa yana amfani daita ne dan daukar fansa, atunaninshi tsanarshi zata qara hauhawa ne acikin zuciyarta, ashe zata fahimceshi? Ashe zata bashi second chance? She look soo real that yakasa gane she's just framing up ne. Kallonta kawai yake wani sabon kaunarta nasake huda zuciyarshi.
"To alhamdullilahi, yanzu dai kowa yaji amsarta data bada da bakinta da kuma dalilanta, me zakuce?" Inji kawu ibrahim yana kallonsu.
Ajiyar zuciya abba ya sauke yace
"Masha allah, haqiqa dalilanta abin dubawane kuma babu abinda ke ciki sai gaskiya, fatanmu anan shine allah yasa hakan shiyafi alhairi kamar yadda tafada da farko"
Daddy ma yace
"To alhamdullilah, gaskiya naji dadi sosai da faruwar hakan fatanmu allah yabada zaman lfy ya kauda fitina kuma yaqara danqon zumuncinmu"
Kawu zahradini shima yace
"Amin amin, nima nayi farinciki qwarai da hakan allah ya tabbatarda alhairi"
Umma da bata cika magana sosai tun sadda sukazo tace "masha allah allah yabada zaman lfy, ya tabbatar da alhairi"
Kallonsu suka maida gabadaya gun ummy datayi zugum cikin damuwa kawu ibrahim yace
"Kefa? Bakice komaiba"
Ajiyar zuciya ta sauke ahankali sannan ta kalli saudart da kanta ke qasa sai kokowa take da hawayen dake neman tonamata asiri sannan ta maida dubanta kan ashraf dashima kanshi ke qasa sannan tace
"To allah ya tabbatar da alhairi yakuma sanya albarka aciki"
Duk aka ansa da amin cikin farinciki.
"Kaifa oga gauro? Baxaka tofa naka albarkacin bakin ba?" Inji kawu zahradini yana kallon sadeeq.
Murmushi yayi a kunyace sannan yace
"Allah yabada zaman lafiya, ya kauda fitina"
Duk aka amsa da amin.
Itadai saudart kanta na qasa amma zuciyarta inbanda suya babu abinda take, tasan tayi wauta sosai, wautar da har ta mutu bazata bar ganin sakamakonta ba, ta ida wargaje rayuwarta da hannunta, ta ida tabbatar wa kanta bazata ta6a yin rayuwar auren da ta dade tana tsarawa kanta ba. Shikenan bakin alqalami ya bushe, there is no going back.
"To alhamdullilah yanzu sai ayi maganar tarewa ko? Koko sai munsake shagalin biki tunda wancan na contract ne wannan kuma na gaskiya?" Inji kawu ibrahim cikin sigar tsokana.
Duk dariya sukayi inka cire saudart da ashraf sai ummy data murmusa, shikau sadeeq duka 36 dinshi suna waje don dariya.
"Duk yadda kukayi ai daidai ne" inji daddy cikin fara'a
"A'a badai yanzu ba, abari amarya tagama shirye shiryenta sannan, su da kansu zasu bamu lokaci" inji umman sadeeq tana murmushi.
Haka dai suka gama tattaunawarsu wanda saudart kawai jinsu take, aqagare take awatse ko tasamu ta ke6e taci kukan dake cinta yadda ya kamata, lumshe idanu tayi jin kanta na dan sara don hayaniyartmsu ma kanta bataso.
Sadeeq kau a 6angarenshi sai mintsinin ashraf dako kwakwarar motsi beyiba tundaxu yana mashi rada saidai ko kadan be nuna yasan yana yiba, farincikin dake ranshi kawai ya isheshi.
Yanajin yadda mutanen falon suke tashi suna barin falon har yarage saura sadeeq kadai sai shi da saudart, wani mintsini mai uban zafi yaqara mashi sannan shima ya tashi yafita.
Murmushi yadan saki wanda saika lura zakasan yayishi sannan ya daga kai yabishi da kallo harya fice yaja musu kofa.
Ajiyar zuciya yasaki marar sauti sannan ahankali ya maido dubanshi kanta.
Tana dai yadda take, zaune lullu6e cikin makekiyar hijabinta kanta a qasa.
Kallonta yake babu ko kyaftawa yanajin wani shauqi acikin zuciyarshi, be ta6a tunanin abubuwan zasu zo da sauki ba haka, a tunaninshi idan tasan gaskiya komai dagulewa zaiyi ashe ba haka bane, ashe zata yafemashi, ashe zata fahimceshi, ashe zata bashi dama.
Motsi yake da baki amma yakasa fadin komai, yarasa ta ina zai fara, yarasa da wacce kalma zaiyi amfani, kallo daya zaka mashi kasan a diririce yake.
Soyake tadago ya kalleta, ya kalli fuskar dake sashi cikin shauqi, fuskarda be gajiya da kallonta, fuskar da ke sashi cikin nishadi.
Ahankali yayi parting din pink lips dinshi cikin muryar rada yace
" *SAUDARH*"...✍
Ngd qwarai da addu'o'inku gareni, allah yasaka ma kowa da mafificin alhairi (amin)
Ummin fasihu🧚🏻♀️
👰🏻🤵🏻AUREN KWANGILA🤵🏻👰🏻
(Contract marriage)
Story written by Ashaanty love💖
(Ummin fasihu)
080
Bata ko motsaba bare asaka ran xata dago daga sunkuyar da kan datayi.
Shiru yayi yana kallonta, he can't believe yanzu tashi ce har abada, atunaninshi izuwa yanzu alaqar dake tsakaninsu tagama yankewa, yariga yacire rai da samunta don atunaninshi abune marar yiwuwa amma dayake allah me yin yadda yaso ne, gashi ya maida impossible zuwa possible.
Kallonta yake wata iriyar soyayyarta na fizgar zuciyarshi, jiyake kamar ya rungumeta a qirjinshi yaita fallasa mata sirrin zuciyarshi gameda ita.
"Thank you" yafada ahankali idanunshi akanta
"Words... can't express how am feeling right now, i feel i am the luckiest person in this world... thanks for choosing to stay with me...forever, thanks for forgiving me, thanks for.... everything" yafada cikin romantic tone.
"I promise...