Showing 87001 words to 90000 words out of 173829 words

Chapter 30 - Auren Kwangila Book 1 Hausa Novel Complete

11 Dec 2024

1128

kuma qara budamashi har ya tara kudi shima yasiya mota daya dukda da second yafara don gangar jikin motar yafara siya sannan ahankali ahankali yacigaba da hadata harta zama cikkakiyar mota nan shima yabadata haya ga qanninshi Zaharadini yayinda shima yacigaba da nashi tuqin, saiya kasance ana bashi haya shima yana bayarwa kuma hakan ba qaramin budi ya qaramashi ba.



Ana cikin haka suka hadu da *SHAMSU ABUBAKAR* wanda akafi kira da *SHAMSU QOLO* d'an qauyen kankiya dake jahar katsina shima yashigo kano ne cirani.

Sun hadune wani zuwan da shamsu yayi zai sari jarkokin man olga sai aka hadoshi da motar Auwal suka taho alokacin shamsu na aiki ne awani qaton shagon kayan masarufi aqarqashin wani.


A wannan tafiyar suka qulla abota kasancewar shamsu mutum ne mai saurin shiga rai ga iya tsara kalamai ga raha.

Cikin dan qanqanin lokaci suka zama aminan juna don sosai suke qaunar juna har takaiga indai auwal nacikin gari to zakagansu jone koda wane lokaci, hakan yasa kowa yasan da abotarsu.



Shekara daya da aurensu Auwal Allah yayima Mallam mamman rasuwa, mutuwae data girgiza mutane dadama don bawani jinya yayiba, amai da zawo yayi na yini daya ya sheqa.

Babu shiri su Auwal suka tarkato sukayo wudil.

Suna wudil har akayi sadakar bakwai.
Cikin masu zuwa masu gaisuwa harda Shamsu qolo don shi tun ranar kwana biyu yazo saida akayi addu'ar uku yajuya washegari.

Bayan addu'an bakwai su Auwal na shirye shiryen komawa kano Raliya matar Ibrahim ta haihu kasancewar dama da tsohon cikinta akayi rasuwar.

Ta haifi danta namiji tubarkallah babu wata wata aka maida sunan margayi mallam mamman sai aka dinga kiranshi *Mallam*
Sai bayan suna sannan su Auwal suka koma kano.


Haka rayuwa tacigaba da tafiya, ahankali ahankali Allah yaita budama Auwal yaqara siyan mota yaqara badata haya itama wanda hakan besashi barin tuqinba.

Haka yacigaba tun yana sayan tsoffafi yana hadawa harya fara siyan sabbabi dall zuwa lokacin arziqi ya zaunamashi sosai don harya ginama kanshi gida mai kyan gaske.
Yakumu rushe ginin qasan gidansu ma wudil yayi na zamani ya zuba kayan more rayuwa a gidan musanmman dakin inna wanda babu yadda beyi ba daita kan yamaidota kano taqiya wai gwara ta mutu a mahaifarya.

Haka zalika bebar qannenshi ba, yana taimakamasu bakin yinshi donshi mutum ne mai yawan kyautaa dukda suma basu rasa komaiba sunada rufin asiri daidai gwargwado.



A 6angaren abotarsu da shamsu qolo kau sai abinda yaci gaba don izuwa lokacin shamsu shima ya bude nashi qaton supermarket wanda babu abinda mai siyar na kayan masarufi.

Tun yana order a garruruwa har aka fara kawomashi daga qasashe daban daban wanda harda cotonou inda ake kawomashi shinkafa mottoci mottoci wanda duk yawanci motoccin Auwal ne, hakan yaqara danqon zumuncinsu ya kasance kansu a hade yake.



Saidai matsalar Shamsu daya, had'ama da son kudi, dik inda ta qyallo zai samu saiya kutsa yabi yasamu, hakan yasa yake hadawa da ha'inci a al'amuranshi.

Auwal yasha yimashi fads akan wannan halin amma yakasa dainawa don tun farko betashi ta wata isashiyar tarbiya ba na iyaye saina malamin makarantar allonsu wanda sunmashi yawa baya iya controlling dinsu duka.

Ana haka wata shekara Auwal ya tilastama Shamsu dole suka tafi aikin hajji tare wanda da ason ran shamsu ne bazaijeba don shi be qaunar abinda zai zazzagarmashi da account dinshi.


Bayan dawowarsu Alhaji Auwal da Alhaji shamsu, Alhaji Auwal ya tadda labarin farincikina na samuwar juna biyun Fatima wanda shekararsu ta uku kenan da aure.

Farincikin da Alhaji Auwal dama makusantanshi sukayi baya misaltuwa don sadaka yaitayi yana godewa allah da kyautar dayabasu.

Nanfa suka dauki son duniya da kulawa suka dorawa cikin, ba Alhajin ba ba zaharadini qannanshi ba ba fatima ba.

Haka fatima taita samun kylawa ta musanmman suka raini cikin cikin tsantsan kulawa har allah ya sauketa lfy ta sum6ulo qaton d'anta mai kama daita sak masha allah.


Farincikin da Alhaji Auwal yashiga alokacin 6ata bakine.

Kan kace me? Mutanen wudil harsun iso lokacin har ansakama Nura mai bima Ibrahim biki.

Suma yan adamawa yan ywan fatima ba'a barsu abaya ba da jamila yar kakumu haka suka garzayo kano don taya wannan ahali murnar samun qaruwa.


Ranar suna d'a yaci sunan kakanshi wato Muhammad ana masa laqani da *ASHRAF*...✍️



Ummin fasihu ce🧚🏻‍♀️

👰🏻🤵🏻AUREN KWANGILA🤵🏻👰🏻
(Contract marriage)


Allah ka yayemana wannan annobar (covid19)🤲

Allah ka ji6anci lamuranmu, karka barmu da kanmu🤲



Story written by Ashaanty love
(Ummin fasihu)








066




Ranar suna Fatima tasamu kyauttutuka dayawa wanda duk yawanci abokan huldar Auwal ne sukafi badawa, sosai suka nuna bajintarsu wajen kawo kyaututtuka na Alfarma.

A 6angaren Alhaji shamsu kau abin ba'a cewa komai don shima ba qaramin kudi yakashe ba don har ragunan da aka yanka shiya siya bayan kayan jarirai da lasa lasai dayaba mai jego.

Haka dai akayi sunan aka watse, kowa yakoma inda yafito.

Anan Fatima tacigaba da wankanta Auwal yasamomata wata dattijuwa dake qasan unguwarsu tana zuwa kullum tana wanke jariri.

Haka suka cigaba da kula da dansu cikin so da qauna, kan kace me yaron ya girma yayi bul bul kamar irin 'ya'yan turawan nan ga wayau kamar me?

Yanada wata biyar suka tattara sai wudil bikin Nura.

Shima babu laifi ansha shagalluluka kala kala, Ashraf kau saboda farinjini fatima har rasa hannun wa yake don beda qiwuya ko kadan da yaga saiya 6angale mashi baki yana miqo hannu alamun yanason adaukeshi, hakan yasa Fatima bata ganinshi sai ya buqaci abinci sannan za'a kawoshi ta shayar dashi akoma dashi.

Saida sukayi sati sannan suka juyo kano wanda tun washegarin biki Alhaji Auwal dama yayi gaba sukuma saida suka zagaye dangi sannan suka taho.

Haka rayuwa tacigaba da kasancewa.
Ashraf ya taso cikin gata da soyyaya tako wane 6angare saidai duk gatan dayake samun hakan be hanashi samun inganttaciyar tarbiya ba don duk yadda suke dashi idan yayi ba daidai ba suna tsawatar mashi kuma suyimashi nasiha.

A 6angaren arziqin Alhaji Auwal kuwa sai abinda yayi gaba don yanzu yabar tuqi yakoma harkar shinkafa kawai, mottocinshi basu qilguwa kullum cikin busy yake yazama babban dan kasuwa.

Tun bayan haihuwar Ashraf *Ummy* kamar yadda Ashraf ke kiranta bata qara haihuwa ba sai 6arin datakeyi akai akai wanda sunyi maganin amma a banza.

Da farko Alhaji Auwal (Abbu) yaso ajuya mahaifarta saboda wahalar dayaga tanasha amma saita qiya acewarta abarta ahaka haka allah ta tsara mata.

Ashraf nada shekara biyar Abbu tabiyama inna, inna Raliya, ummy, inna jamila da zainab matar Nura hajji suka dunguma sukaje suka sauke faralli.


Bayan dawowarsu da yan wattanni akasama Alhaji shamsu biki dawata shuwa Arab ta garin borno.

Acikin wannan lokacin ciwon zuciyar Inna yatashi sosai babu wata wata Auwal ya daukota takawota asibitin kano aka cigaba da bata kulawa saidai dayake lokacinta na kusa kwana biyar tayi tana jinya ta rasu.

Sosai mutuwar ta girgizasu don sunyi kuka marar iyaka.

Haka suka dauki gawar suka juya wudil don Inna tabar wassiya idan tamutu koma inane a maidota wudil arufe don tafison arufeta a mahaifarta.

Bayan sati biyu suka dawo kano rayuwa tacigaba da tafiya.

Izuwa yanzu ansaka Ashraf makarantar primary ta private kuma allah yayimashi qwalwa da basirar daukar abu don shike ciwo nadaya a ajin duk qarshen term

Ba'a dadeba bikin Alhaji shamsu ya matso nanfa sukaita shirye shirye babu kama hannun yaro.

Duk tare suke komai da Alhaji Auwal don bawani dangi ke gareshiba sosai sai tarin abokan arziqi da abokan kasuwanci.

Gaggarumin biki akayi nagani na fada inda babu laifi ansha shagulgula sosai sannan aka kawo amarya khadija dakin mijinta.


Haka rayuwa tacigaba da tafiya Ashraf sai qara girma yake da wayau, arziqin Abbu sai qara hauhawa yake allah nasa mashi albarka hakan yasa yakeda maqiya da mahassada masu hassada dashi a6oye batareda yasaniba.

Bayan shekara daya da aurensu Alhaji Shamsu sai Allah ya azurtasu da samun diya mace kyakyawa sak uwarta.

Alhaji shamsu baki yaqi rufuwa don murna, ranar suna na zagayowa aka radamata sunan *SAUDATU*


bayan haihuwar da 'yan wattani su Alhaji shamsu da matarshi khadija suka fara samun matsala atsakaninsu sanaddiyar sata dayayi acire mata mahaifarta wai diya daya ta ishesu acewarshi 'ya'ya talauci suke jawowa.

Firr khadija taqi yarda acewarta bazai sata ta kashe kanta da rai ba, tun suna abin a tsakaninsu har yakai kunnen Abbu kasancewar Khadija tagayamashi ko zata samu yanunama Alhaji shamsu daidai.

Abin yaba Abbu haushi sosai saiyaje yasamu Alhaji shamsu har company dinshi yayimashi magana shikuma sai abin ta hassalashi sosai ganin wai khadija takai qararshi wajenshi kamar wani ubanshi.

Nanfa Alhaji shamsu yafara zazzaga bala'i ta inda yake shiga batanan yake fitaba, aranar dakyar Abbu yafito company din rai 6ace abinda beta6a faruwaba a tsakaninsu.


Shikuma Alhaji shamsu yana komawa gida yarufe khadija da fada ta inda yake shiga batanan yake fitaba yace kuma cire mahaifa dole ayi muddin tanason cigaba da zama dashi.

In taqaice muku dai saidai auren yamutu da abu yaqi dadi wanda hakan ba qaramin 6ata ran Abbu ba yayi.

Wannan karon har gida Alhaji Auwal ya tadda Alhaji shamsu sukayi tatass inda daganan abotarsu ta shekara da shekaru ta watse.

Ummy sam bataji dadin hakanba amma ya suka iya?

Kan kace me? Har labarin 6atawarsu ya zagaye koina da aka sansu, mutane sai jimamin abun suke yayinda wasu suke farinciki akan haka.

Shekara daya da faruwar wannan al'amari Ummy tasake samun juna biyu lokacin shekarar Ashraf takwas kenan.

Sosai cikin yabata wahala sannan tasamu ta haifeshi bayan tasha baqar wahala tasamu diya mace sak Ashraf saidai bata ida kamoshi a haskeba.

Zokaga murna wajen Ashraf don sosai yake sha'awar qane ko qanwa dama.

Ranar suna na zagayowa akasamata sunan margayiya Inna wato AMINATU amma ana kiranta da *Baby*


Ana haka bikin zaharadini yataso inda ya auri yar kano suka tare a gidanshi da shima yagina a unguwar.

Kwanci tashi ba wuya, baby anfara girma don harta shekara biyu wanda yayi daidai da shekarun ashraf goma da wattanni.

Har a lokacin Abbu basa ga maciji da Daddy, sun watsar da zumuncinsu don ko labarin juna basaji.

Ana haka watarana Abbu na zaune cikin iyalanshi zaharadini ya bugo mashi waya kome yacemishi oho? Saiga Abbu ya zabura zaune har yana qwarewa da abinci

Cikin sauri ummy ta bashi ruwa suna jeramashi sannu ita da yaran.
Saida tarin ta lafa sannan ta tambayeshi lafiya? Yace ba lafiya bari yaje yadawo.

Haka ya fice be ida qarasa abincinba wanda itama ummy kasa ci tayi sai barosu ashraf datayi a dining tadawo falo tazauna tana addu'ar allah ya jiyardasu alhairi.


Acan kau Abbu yashiga tashin hankali marar misaltuwa don duka mottocinshi jami'an custom suka kame da abinda suka dauko.

Babu yadda beyiba wajen ganin an sakarmashi su amma abu yaci tura kai daga baya ma har gidanshi jami'an sukazo suka watsamashi komai suka 6alle store dinshi suka kwashe shinkafa ko taci basu bariba.

Wannan cin zarrafin baqaramin qonama Abbu rai yayiba don gani yake wannan cin fuskane babba.

Be ida shiga tashin hankaliba saida yaji cewa tsohon abokinshi kuma amininshine ummul aba'isan faruwan wannan lamarin.

Sosai abun ya dakeshi wanda har saida yakwanta ciwo.

Alokacin zaharadini ne yake taimakonsu dana magani don yadda kasan daukewar ruwa hakan komai na arziqin Abbu ya qare.

Magani akema Abbu amma kamar qaramashi ciwon ake.

Kullum cikin ambaton sunan Shamsu qolo yake yana hawaye.

Sosai su ummy dama kingin danginshi suka shiga tashin hankali akoda yaushe ummy da ashraf dashima yafara sanin komai cikin kuka suke saiya kasance Ashraf yakasa mance sunan da abbu ke yawan maimaitawa yana hawaye. Abinka da yaro saiya riqe sunan gamm a kwakwalwarshi yayinda yakema mammalakin sunan tsana wacce bata misaltuwa.


Saida Abbu yayi sati biyu sannan Allah ya dauki ranshi, mutuwar da ta girgiza jama'a da dama kar ummy ma taji labari.

Haka dole akamashi sutura jama'a takoina ancika unguwar danqam suka rakashi aka kaishi gidanshi na gaskiya.


Su ummy basu tashi gane kurensu ba saida duk aka watse nan fa talauci ya kunnomasu kai.

Gashi dama zaharadini yake dan taimakawa to shima yanzu babu mota hannunshi kuma kamar hadin baki kowa yaqi bashi dukda kau mutuncin da mutanen keyi da margayi Auwal dayake raye.

Hakan yasa yakoma kasuwa yana tsaron shago wanda abinda yake samu bewani taka kara ya karya ba.

Ganin haka yasa ummy ta tuntu6i zaharadini akan asiyarda gidan dasuke ciki su siya qarami kingin kudin saisu jujjuya.

Saida zaharadini ya tuntu6i yayyanshi na wudil saboda hadin kai irin tasu suka kauyi maraba da hakan don suma basujin dadin halin da iyalan dan uwan nasu yake ciki kawai don basuda halin taimakawa ne.

Kan kace me? Har an saka gidan kasuwa aka kau siyeshi da daraja, zaharadini ya samarmasu dan qaramin gida a unguwarsu suka zauna ya miqamata kingin kudin inda taqi amsa tace yaje yaita jujjuyawa kawai.

Shima qin yarda yayi har saida magana taje gasu Kawu ibrahim nan shima kawu ibrahim yayi na'am da shawarar Ummy kan zaharadini ya juyasu tunda shima kusan beda sana'a yanzu tsayyaya albashi sai aba ummy wani kaso acikin kudin itama tafara business.


Hakan kau akayi, zaharadini yaje ya sari kayan kitchen da kudaden yayi hayar shago acikin kasuwa itakuma ummy tafara sana'ar saida kayan humra da turrarukan wuta wanda Allah ya dubi maraicinsu yasamasu albarka aciki.

Ashraf da tuni ancireshi daga makarantar kudi don yanzu tafi qarfinsu aka maidashi ta gomnati yazana common entrance dinshi yakau fito da result mai kyau yasamu admission awata makarantar gomnati ta secondary.

Ashraf yanada hazaqa sosai kasancewar yasamu good background a makarantar primary dinsu kasancewar private ce.

Ahankali yafara suna don ashraf akwai qoqari da saurin fahimta don shike topping din class dinsu duk term.

Bayan haka ga baiwar kyau da Allah yabashi don kallo daya zakamashi kasan ya hada jini da fulani.

Ganin yadda ake sonshi ake kuma lilliqemashi yaja ashraf tsirowa da halin jinkai da miskillanci.

Yaga daman kana mashi magana saiya mula yasha iska sannan ya amsa a dage.

Haka yan aji ke fama dashi musanmman masu liqemashi ya koyamasu karatu, bazaiqi koyamusu ba amma saiya wanasu son rai ya shamusu qamshi sannan ya koyamasu hakan kuma be 6atamasu rai don su shan qamshinshi ma burgesu yake don komai yake kyau yake musu.


A ss1 suka hadu da *SADEEQ UMAR* the mathematician kamar yadda aka samashi suna a school din.

Duk aji daya aka sasu kuma ga lokacin basusan junaba don sadeeq transfer akayi mashi yayi junior waec a school din, sai ya kasance dukkansu sun hadu a commercial class.


Da farko gaba da kishi suka farayi dajuna kasancewar kowa na taqama shi genius ne.

Ashraf yafishi qoqari a sauran subjects din irinsu biology, english, business studies da dai sauran subjects din da babu calculation saidai sadeeq ya dokeshi a calculation don yadda kasan aljani haka ya iya lissafi hakan baqaramin 6ata ran ashraf yakeba don yasaba shine agaba a komai.

Hakan yasashi yin kishi da sadeeq musanmman idan yaga students naxuwa wajenshi solving din lissafi.

Shima sadeeq lura dayayi da yadda ashraf kemashi wani gani gani yasashi kama kanshi yanuna besan da wanzuwarshi ba.

Haka fa akacigaba da competition tsakaninsu kowa nason gwadawa dan uwanshi iyakarshi.

Saida suka shiga ss2 suka shirya shima sadeeq ne yanemi suyi abota don harga allah ashraf na burgeshi.

Kamar yadda yasaba saida yasha qamshi yana hura hanci sannan ya amince dukda can qasan ranshi murna yake don shima sadeeq na burgeshi don sadeeq badai raha da barkwanci ba, kwata kwata beda saurin fushi saidai idan aka quleshi beda kyau sa6anin ashraf da kamar akan wuya yake abu kadan ke hasalashi.

Ahaka suka qulla abota mai qarfi duk inda kaga daya sai kaga dayan har takai babu wanda besan da abotarsuba a fadin makarantar.

Alokacin allah yasama sana'ar kawu zaharadini albarka sosai don harya canza shago ya kama babba yana cigaba da sana'arshi ta kayan kitchen ashraf na dan kama mashi da tsaron shago duk sadda beda wani aikin yi.

Ahakan suka qarashe secondary school din lokacin baby ana primary.

Baby ta taso yarinya mai rigima da iyayi ga baki zai kamar parrot, rawar kanta yasa basa shiri kwata kwata da ashraf don kwa6darta yake idan tayimashi ba daidaiba babu abinda ya dameshi saidai yana sonta sosai.

Bayan result dinsu yafito ne suka samu daddadan albishir na scholarship da aka bada a school dinsu na mutane biyar qasar waje wanda ciki harda ashraf da sadeeq.

Farincikin ranar har rawa saida suka taka.

Cikin dan qanqanin lokaci aka gama shirin komai suka lula UK karatu.

Acanma bata sauya zaneba suna zuwa ba'a wani jimaba sukayi fice a school din saboda qoqarinsu ga hadin kai don kodayaushe tare suke dukda kamar kaji suke kodayaushe cikin fada suke donma sadeeq nada haquri.

Nanfa akaimasu caa don lokacin sun zama samari masu jida kyau da gayu dukda sadeeq ba fari bane amma baqinshi mai kyau ne ga uwa uba fara'a dake qarawa mutum kyau dayakeda ita.

Kan kace me yanmatan school din sukai musu caa dukda vasu cika tunkarar Ashraf ba don ba qaramin kwarjini yake musuba gashi fuskarshi ba wasa kullim a dinke take.

Sa6anin sadeeq da ba ruwanshi idan mace ta tinqareshi saiyace yanada aure harda 'ya'ya biyu qauye idan kuma tanason yayi nabiyu daita ya kaita qauye to.

Haka yake samu su rabu lfy dasu batareda ran kowa ta 6aci ba.

Ana haka kwatsam yaga ashraf na soyayya da suzy wata yar nigeria wanda itama karatu yakawota qasar saidai batada kamun kai ko kadan ga shiga ta fidda tsiraici.

Da farko yaso nisarda ashraf aibunta anma saiyaga kamar yana sonta sosai saiya qyaleshi saigashi basu wani yi nisaba suka rabu inda sukayi wani gaggarumin fada a filin makaranta sadda yaganta suna kissing da wani bayahude mai suna chris james

Daya nuna 6acin ransa akan haka saita fara bala'i wai bawani matsiyacin da zai hanata sakewa a school donma sun samu an biyamusu scholarship da a ina zasu ganta bare har raini yashiga tsakani?

Sosai abun ya6atawa ashraf rai don dakyar sadeeq ta janyeshi daga filin wanda yacika danqam da yan ganin qwam.

Tun daga lokacin kowa yakama gabanshi babu mai kula dan uwanshi har suka kammala abinda yakaisu suka dawo nigeria.

To anan ne zaharadini ya maidomasu dukiyarsu duka ganin ashraf ya mallaki hankalin kanshi.

Nan ummy taqi yarda suka amshi kudin kawai suka barmashi ribar dayaita juyawa hakan kuma ba qaramin dadi yayimasuba kuma hakan yaqaramata qima a idanun dangin mijinta.

Ahankali ahankali shima ashraf ya shiga harkar kasuwanci kasancewar shi dama ya karanta.

Nan sukayi hadin gwiwa da abokinshi kuma dan uwanshi sadeeq suka fara da kadan kadan har allah yasaka masu albarka suka bude tanqamemen company dinsu wanda suka samashi suna A.A ENTERPRISES LTD
wanda ahankali ahankali sukayi rassa a qasashe daban daban, talauci ya qaura a wannan ahalin suka koma kamar koma ince fiyeda yadda suke da.

Ashraf shima babanshi yabiyo a kyauta shiyasa kaf family dinshi babu mai kukan babu don babu babu din.


*CIGABAN LABARI*


sainaga ruwan comments tukun, naga alamun kwana biyu kun danyi sanyi🙁


Ummin fasihu ce🧚🏻‍♀️

👰🏻🤵🏻AUREN KWANGILA🤵🏻👰🏻
(Contract marriage)




Allah ka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login