Showing 99001 words to 102000 words out of 173829 words

Chapter 34 - Auren Kwangila Book 1 Hausa Novel Complete

11 Dec 2024

1144

ko?" Inji mamy tana kallonta sosai tana qoqarin gano inda ta ta6a sanin fuskar.

Murmushi mai sauti ummy tayi tana kada kai

"Sosaima, nasanki kema kin sanni wataqila dan an dade ba'a haduba shiyasa kika kasa ganeni, shekaru Ashirin ai ba wasaba"

Kallon juna Abba da Mamy sukayi sannan suka maida kallonsu kanta

"Fateema ce, matar aminin tsohon mijinki Shamsu... Matar Alhaji Auwal"

Tsit dakin ya dauka, kowa yazuba masu idanu yayinda ita mamyn tazuba ummy idanu babu ko kyaftawa tanason tuna inda ta ta6a jin wannan sunan.

"Auwal aminin mijinki dakika sameshi lokacin dakuka fara samun mtsl da tsohon mijinki" ummy taqara fada ganin mamy ta antaya kogin tunani.

Ahankali mamy tafara ware idanu tana kallon ummy daketa murmushi yayinda take nunata da yatsa bakinta na rawa

"Ummyn muhammad?!" Tafada tana ware manyan idanunta sosai

Murmushi kawai ummy tayi tana kada kai.

Dasauri mamy tanufi wajen ummy suka rungumi juna

"Ummyn muhammad? Kece or am dreaming? This is unbelievable" tafada cikin alhini.

Murmushi duk mutanen dakin sukayi suna kallonsu.

Nanfa akayita firar yaushe gamo, haryanzu mamy takasa yarda ummy ce surukarta, jinjinama ikon Allah takeyi, ko a mafarki bata ta6a tunanin zata sake ganinta ba sai gashi cikin ikon allah sun sake haduwa kuma wannan karon da strong bond atsakaninsu.


Sun dade suna fira suna dariya suka dan ta6a kayan motsa baki da aka kawomusu sannan suka nutsu suka dawo serious don tattauna abinda yakawosu, ummy sai kallon mamy take tana jin badadi don tasan dole hankalin mamy yatashi idan taji dalilin zuwan nasu.

Ciki hikima da iya tsara zance Kawu ibrahim ya gabatarmusu abinda yakawosu wanda saida yafara basu labarin abota da amintar dake tsakanin margayi Auwal da Shamsu sannan ya gangaro zuwa yadda suka samu matsala dajuna suka koma basa ga maciji da juna zuwa yadda aka kame mottocin margayin da yadda labari ya iskesu nacewa aikin tsohon amininshi ne sanadi harzuwa jinyar dayayi wanda sanaddiyar girgizar dayayine dajin cewa tsohon abokinshi ne sanadin karayarshi wanda wannan jinyarce sanadinshi.

Ya gangaro kan yadda rayuwa ta sauyamusu da yadda suka siyarda gidansu suka samu allah ta tallafamusu zuwa inda Ashraf yasamu scholarship yayi karatunshi a Uk xuwa inda yagama yabude company na A.A ENTERPRISES.


Tsit falon yayi, kowa shiru kamar ruwa ya cinyesu, mamy kau idanunta sun kada sosai mood dinta ya chanza

Abba kau he is expressionless, baxaka iya gane awane yanayi yake cikiba.

Ajiyar zuciya kawu ibrahim ya sauke sannan yacigaba daga inda yatsaya yafara magana akan abinda ya tarasu.

Tunda yafara magana mamy takafamashi idanu tana kallo babu ko kyaftawa harya kai aya.

Daga mamy har Abba rasa mai kwakwarran motsi akayi, they're all dumbfounded.

Kwakwalwarsu kasa daukar zancenshi sukayi.

"I don't understand, i don't really understand" inji mamy tana girgiza kai hawaye na taruwa idanunta, kallo daya zaka mata kasan hankalinta yayi matuqar tashi.

Kama hannunta ummy tayi kasancewar dama kusada ita take asanyaye tace
"Khadija, nima i was shocked danaji wannan zancen, it's unbelievable banta6a jin makamancin wannan yafaruba ko a tatsuniya amma it's real" tafaxa asanyaye.

" *AUREN KWANGILA?* contract marriage? Dama akwai irin wannan auren? Am confused" tafada kaida gani kasan she's not herself.

"But how? Tayaya Saudart da hankalinta zata yarda da irin wannan shirmen? This is unbelievable" inji Abba shima cikin alhini

"He forced her, bada son ranta bane, shiya tilasta mata" inji ummy

"Shiya tilasta mata?! Ni meye amfanina? Why can't she come over to me and tell me! Daqiqancinta harya kai takasa confiding in me as her mother?.... dama nafada! Babu yadda banyiba akan kar amayar mashi daita tun farko akaqi saurarata, ga irinta nan, ya siyar daita akan kudi, ya musayata da kudi! Kagani ko Alhaji? Kaga abinda nake fada? Allah kadai yasan me da me yakoyamata, Allah kadai yasan tarbiyarda ya dorata akai, ya maidamani yarinya cash worm..." kuka ne ya kufce mata ta toshe bakinta tanayi sosai.

Rungumota ummy tayi asanyaye tana rarrashi.

"But how come tun farko baku ganeshi ba dakukazo?" Inji Abba da duk jikinshi yayi sanyi.

"Alokacin nida Nura mukazo tareda yan uwan ummy, lokaci yaja gashi dama ni sau daya nata6a ganinshi lokacin rasuwar mallam, shi zahradini daya sanshi sosai bayanan lokacin yayi tafiya, kuma munyi bincike mun samu gamssashiyar shaida gamedashi tun kafinma muzo din" inji kawu ibrahim.

"Innalillah waina ilaihi rajiun, wannan abu beyi dadiba samm" inji Abba yana girgiza kai.

Dagowa mamy dake kuka haryanzu tayi tareda cewa
"Dama nasani, that greedy man can do anything don yasamu kudi, gashi greediness dinshi yaja zai lallatama diyata future, koko ince yama lallata tunda gashi itama saboda kudin ta yarda tayi auren"

"No mamy, he forced her ne" inji umma da tundazu batace komaiba.

Kallon umman mamy tayi tace "bawani forcing, nasan saudart ciki da bai, idan batayi niyyar yin abuba babu wanda ya isa yasata, besides baganiba? Ni meye amfanina idan bazata iya gayamin damuwarta ba? Am her mother for goodness sake, dama i smell something fishy gameda auren nan don everything come all of a sudden ne, now yayi nasarar maida diyata kwadayyaya irinshi" tafada bitterly.

Rarrashinta akai tayi don kuka take sosai, banda zafi babu abinda zuciyarta keyi.

Ajiyar zuciya Abba ya sauke sannan ya kalli su kawu ibrahim dakyau ya bude baki calmly yace

"Now meye abin yi? Aikin gama dai yariga da yagama, sai samun solution yarage, yanxu ku me kuka yanke?"

Kawu zahradini da shima tundaxu beyi maganaba yadan muskuta sannan yafara cewa
"To yanxu dai two things are involved, na farko case din shamsu nabiyu kuma auren nan.

Mudai bamu riqe shamsu araiba akan abinda yaima margayi, wannan tsakaninsu ne da margayi da Mahallicinsu, Allah zaima kowa sakayya daidai dashi.


Batun aure kuma Ashraf yanuna yanason matarshi kuma ya janye contract din tsakaninsu, idan so samune sucigaba da zama a matsayin ma'aurata saidai wani hanzari ba gudu ba.. *saudart!*.... dole yadda tun farko auren yarjejeniya ne a tsakaninsu yanxuma yarjejeniya zamansu zai zama, ma'ana dole saida amincewar dukkansu, bazamuso mu cutar da daya ba don farantama dayan. Idan saudart ta amince zata cigaba da zama dashi to fallilahil-hamd don muma bazamu so yankewar wannan alaqar tamuba, munason saudart kamar yar cikinmu, abinda mahaifinta yayi can baya bazai ta6a shafanta ba don kwata kwata babu kamanceceniyar hallaya tsakaninsu, saudart yarinyace mai nutsuwa da tarbiya wanda samun irinta ayanzu yayi wuya, ladabi da biyyayarta yasa tunfarko ta yarda da qudurin babanta wanda ita tausayamashi tayi ganin halin dazai fada idan bata aminceba, saudart macece mai amana da zuciya mai kyau don ba don itaba da yanzu company don A.A ya fuskanci mummunar asara da karaya, muna sonta amma hakan baxaisa idan taqi yarda da cigaba da zama dashi mu tilastata tayi zaman cutuwa ba"


Ummy itama ta dora da "tun farkon haduwarmu da saudart tashiga raina, nasan she's the best wife for my son, she's a girl with a pure heart, ina jinta araina fiyeda yadda nakejin baby araina, bazamu ta6a mata dole zama da Ashraf ba, haqurin datayi dashi da farko ma ya isa, i know yamata abubuwa don ni nasan waye dana idan yanaqin abu, wataqila cin zalinta dayaitayi batareda haqqintaba yasa allah ya jarabceshi da sonta lokaci guda don dama ance idan qiyyaya tayi yawa takan zama soyyaya daga baya, yana sonta fiyeda tunaninku yanzu amma hakan bazai sa a tauyema saudart haqqinta ba, cigaba da zamansu da rabuwarsu will depend on amsarta ne"

Shiru dakin yasake dauka sai can Abba ya sauke ajiyar zuciya yace

"To yanzu abinda za'ayi shine zamu zauna dukkanmu harda Alhaji shamsu da saudart dashi kanshi mijin natan a yanke koma menene, aganina hakan zaifi? Koko?" Yaqarashe zancen yana kallonsu kawu ibrahim

"Masha allah, hakanma yayi"

"Yanzu zanma shi Alhaji shamsun magana inyaso duk yadda muka yanke zanyi informing dinku insha allah"

"To allah ya yarda yakuma mana jagora" inji kawu ibrahim

Duk amsawa da amin sukayi har lokacin mamy batabar hawaye ba.

Haka dai suka tafi kowa zuciyarshi babu dadi.

Mamy tayi kuka kamar me? Sai blaming din alhaji shamsu take da lallatamata rayuwar diyarta.

Shidai abba inbanda rarrashi babu abinda yake don shima har zuciyarshi beji dadin abinda yafaruba don shima yanason saudart harcikin zuciyarshi kamar kingin yayan cikinshi.


Aranar dai haka suka wuni cikin damuwa da bacin rai.



A 6angaren Ashraf kau tunda suka dawo yakasa xaune yakasa tsaye don fargaba, jiyake zuciyarshi zata iya tarwatsewa idan yaji mummunan sakamako, dama tunda suka tafi yaketa addu'ar allah ya dorashi akansu allah yabashi nasara don rashin saudart daidai yake da rasa farincikinshi a rayuwa.

Duk up and down din dayakeyi ummy na hankalce dashi tayi banza dashi kamar batasan me yakeba.

Sai kai komo yake a falon yaji ko zata kirashi amma tayi banza dashi daga baya ma zama yayi a falon yana kallo yayinda dukkan hankalinshi ke kan duk wani motsi da ummy zatayi.

Haka yasha zamanshi daga qarshe ummy ta tashi ta hayewarta sama tabarshi nan zaune.

Babu yadda ya iya haka ya tashi shima jiki a sanyaye yakoma part dinshi zuciyarshi namashi saqe saqe.




Zaune take a garden bisa wata plastic chair ta rungume hannayenta tana kallon waje guda babu ko kyaftawa wanda hakan ke nuna cewa tayi nisa cikin tunani ne


Tun ranar dasuka rabu da ashraf bakery dinta wurin yazama wajen zamanta, bata qara marmarin fitaba tun ranar, kullum anan take zuwa ta zauna ba uhm bare uhm uhm sai tunani wanda yazame mata jiki.

Kallo daya zaka mata ka hango fadawar datayi sosai, duk takoma shiru daita kamar ba active saudart ba.


Ringing din wayarta ya maidota daga duniyar tunanin data lula.

Ahankali ta kalli wayar sannan cikin rashin kuzari ta jawo wayar ta duba.

Maryam ce hakan yasata yatsuna fuska sannan ta daga.

Sudan jima suna magana akan abinda yashafi business dinta wanda yanzu rabonta da leqasu tun ranar nan, akasalance taita amsamata suka dan tattauna sannan sukayi sallama.

Tana niyyar ajiye wayar wani kiran yashigo wayarta.

Tsayawa tayi tana kallon sunan dake yawo a screen din wayar batareda ta iya dagawa ba yayinda takejin qaruwar bugun zuciyarta.

Kasa dagawa tayi har kiran ya tsinke, babu 6ata lokaci wani kiran yasake shigowa again.

Limshe idanu tayi ahankali tayi ta bude tana kiran sunan allah.

Cikin rawar hannu tayi picking din call din ganin zai qara tsinkwa ta kara a kunne atsorace....✍


Ummin fasihu ceπŸ§šπŸ»β€β™€οΈ

πŸ€΅πŸ»πŸ‘°πŸ»AUREN KWANGILAπŸ‘°πŸ»πŸ€΅πŸ»
(Contract marriage)



Story written by Ashaanty loveπŸ’–
(Ummin fasihu)






074


"Aslm alaiki" tafada ahankali zuciyarta fall fargaba

"Wslm Amaryar contract, ya kike?" Taji anfada daga dayan 6angaren

Dumm! Gabanta ya yanke ya fadi, ahankali ta sauke wayar daga kunnenta taqara kallon screen din don qara tabbatar da mai kira din.

Maidawa tayi a kunne tafara magana ad'an daburce

"M...mamy? Mamy ina wuni?" Tafada bugun zuciyarta na qaruwa

"Save your greetings don bana buqata, banida wannan matsayin awajenki so hang it" inji mamy

Hankalinta ne yatashi wanda har saida tamiqe tsaye bakinta nadan 6ari tace
"M...mamy... mmm..meya faru please" tafada yayinda wasu hawaye suka fara kawo mata.

"Mefa? Just call to hear from you dukda bawani matsayi nakedashi awajenki ba"

"Mamy..." saikuma tayi shiru tana toshe bakinta don kuka ne ke neman kufcemata.


"Bye" mamy tafada a dayan bangaren zata tsinke kiran

"No mamy please don't hang u..."

Ding... taji an katse kiran.

Sakin wayar tayi takoma kan kujerar tana dafe kanta da hannaye bibbiyu tafashe da wani irin kuka.

"No..no" tafada tana kuka sosai.

Saurin duqawa tayi tasake daukar wayar data yar qasa tana kuka tashiga re-dialling din number mamy, hannunta sai rawa suke.

Takira yafi so biyar amma ba wanda aka daga.

Wani kukan tasake fashewa dashi tana cillar da wayar.

Dama tsoronta kenan, kullum fargabar datake kenan, shikenan tafaru taqare.

"Am doomed!" Tafada tana daura hannu aka kamar wanda aka kawoma saqon rasuwar uwarta.


Wayar tasake dauka tanufi cikin gida tana kuka sosai tashiga dialing din number Daddy.

Kallo daya zaka mata kasan bata cikin hayyacinta.

Ringing biyu daddy ya daga.

Kukanta dayaji ya katsemashi sallamarshi wanda hakan yasashi zabura amiqe.

"Shalele?"

Zubewa tayi qasan falo don harta shigo falon tana kuka sosai wayar kare a kunnenta.

"Shalele menene? Talk to me" inji daddy cikin rawar baki.

"Nashiga uku daddy, daddy am doomed!" Shine abinda kawai ta iya fadamashi cikin kuka.

"Subhanallilah! Shalele what happened? Meya sameki?" Yafada yana laluban car key dinshi kan table

"Daddy kazo... zan mutu" tafada cikin kuka sosai

Kafin yasamu damar yin wata maganar harta katse wayar.

Bashiri yayo waje hankalinshi a matuqar tashe.







Zaune yake jigum, yarasa meke mashi dadi.

Tagumi yabuga da hannu bibbiyu yana bin screen din laptop dinshi da kallo wanda ke dauke da hotonta daya fito tarr wanda duk ya turasu akan laptop dinshi daga cikin wayar databar mashi


Ahankali aka bude kofar dakinshi baby ta leqo.

Ko dagowa beyiba don bemaji budewar kofarba

Qarasa shigowa tayi da sallama wanda hakan ya fargar dashi yayi saurin dagowa.

"Yaya?... yaya wai ka sauko muyi dinner" inji baby ahankali


Komawa yayi ya jingina da kujerar dayake akai yana sauke ajiyar zuciya

"Go... banajin yunwa" yafada ahankali.

Jimm tadanyi kamar bazata wuceba saikuma tajuya tafita.


Can saigashi tasake dawowa.

Dagowa yayi yakalleta kawai batareda yace komaiba

"Yaya wai kawu yace kazo"

Lumshe idanunshi yayi ya bude
"Ok" yafada ataqaice


Saida tadan jima da tafiya sannan shima ya tashi ya dora shirt saman singlet dinshi yafito.


A dining ya taddasu duka, a ladabce ya gaidasu kai a qasa.

Kawu ibrahim kawai ya amsa ummy ko ko kallo be ishetaba.

"Zoka zauna babana" inji kawu ibrahim yana nunamashi kujerar gefenshi

A natse ya qaraso ya zauna baby tayi serving dinshi

"Now eat" inji kawu ibrahim

Ba musu yadauki spoon din yafara cakula abincin don bawani cin kirki yayimashi ba sai jujjuya spoon din dayake aciki.

Haka suka gama in silent sannan suka fara tashi daya bayan daya yarage saura kawu ibrahim da Ashraf.


Goge bakinshi kawu ibrahim yayi shima yatashi

"Kasameni a garden" yafada tareda ficewa.

Haka kawai yaji gabanshi yafadi ya kasa kai kofin ruwan a baki.

Ajiyewa yayi yana sauke ajiyar zuciya.

Tunda suka dawo yake kasa kunne yaji ki zasuyimashi magana amma shiru gashi yanzu ammashi din amma jiyake beda courage din jin sakammakon daza'a gayamashi.

Ya dade zaune awajen yana saqa da warwara kafin daga baya ya miqe dakyar ya fita zuwa garden din kamar kazar da kwai yafashe mawa aciki.




"Shalele kiyi hqr please, kibar kukan hakanan" inji daddy daya gaji da rarrashi

Zaune take jan gadonta cure wuri guda ta hade kanta da gwiwa tana kuka cikin muryarta dabaya fita tsabar kukan datasha.

"Shalele, am sorry, duk nine silar komai, ki gafarceni 'yata" yafada shima kamar zaiyi kukan

Ko dagowa batayiba haka zalika batabar kukanba hakan yasashi jawota ajikinshi cikin sigar rarrashi.


"Shalele kiyi hqr, nasan yadda kikeji, please kibar kukan haka, ni da kaina zanmasu bayyani kinji? Nina jawo komai kuma ni yakamata inga consequence dinshi, please kibar kuka please"

Itadai batace komaiba sai kukan datakeyi qasa qasa, sosai zuciyarta kemata zafi gawani sara da kanta keyi agefe daya jitake dama tamutu ta huta.


Dakyar daddy yasamu ya lalla6ata tasha tea tasha magani ta kwanta.

Ya dade sosai dakin har saida yaga tayi barci sannan ya lalla6a yafita don karya tadata.


Saida taji alamun yafita sannan ta bude kumburarrun idanunta ta miqe zaune ahankali, hade kai da gwiwa tayi tacigaba da hawaye tana kukan zuci.


Daddy a 6angarenshi shima kasa rintsawa yayi, sosai yake danasani marar amfani.

Danasani yake sosai na halinshi, yasan yanzu tuni dan kingin mutuncinshi yarigada yazibe a idanunsu mamy

Sosai yakejin kunya, sai yanzu yake mammakin yadda acan baya idanunshi suka rufe yakasa hango abubuwan dazasu biyo baya.

Alokacin shidai kawai abinda zai qaru dashi yake hange, be ta6a hangen abinda zai ragu dashiba.

Gashi yanzu ya tsunduma 'yarshi kwaya daya, mai son farincikinshi cikin qunci da bakinciki.




**********************************

Fada sosai kawu ibrahim yayimashi kan abinda ya aikata, ta inda yake shiga batanan yake fitaba.

Sosai jikin ashraf yayi sanyi don tunda yake beta6a ganin kawunshi cikin irin wannam 6acin ran ba.

Sai daga baya yafarayi mashi nasiha mai ratsa zuciya wanda ya ida kashe jikin ashraf.

Saida yaimashi nasiha sosai sannan ya gayamashi yadda sukayi dasu Abba, ya dora dacewa

"Yanzu dai dorewar aurenku ya danganta ne da amsar da yarinyarnan tabada, bazamu so kanmu dayawa ba, bazamu bari ayi zaman cutuwa ba, idan ta amince zata cigaba da zama dakai to fallilahil hamd, amma idan ta nuna akasin haka bazamu tilasta mataba, saidai muyima dukkanku fatan allah ya hada kowa da mafi alhairi"

Bayan haka ya sallameshi.

Tashi yayi jiki amace, yabi ta hanyar baya yashiga cikin gidan ya haye sama kamar marar lakka.

Ahankali ya zauna gefen gadonshi ya jingina kanshi da jikin gadon ya lumshe idanunshi da suke a rine.

Yasan shikenan, shikenan sun rabu da saudart sun gama.

Tun yanzu yasan matsayar aurannan, dama mai neman kuka ne aka jefa da kashi.

She hate him so much, ta tsaneshi ta tsani ganinshi burinta su rabu, meye to amsarta bayan anbata za6i yanzu na cigaba da xama dashi ko rabuwa dashi?

Ofcourse rabuwa ce, yasan bazata tsaya dogon tunaniba zata za6i rabuwa dashi.


Ahankali hawaye suka gangaro daga ruffafun idanunshi yanajin tausayin kanshi.

Yasan rabuwarshi daita daidai yake da rabuwarshi da farincikinshi.

Yasan rabuwarshi daita kamar bude sabon shafin kunci ne arayuwarshi.

His last hope was gone, yanzu baida sauran wani hope, kawai yariga yarasata yagama ne.


Adaren babu wanda ya rintsa acikinsu daga Ashraf da saudart har Alhaji Shamsu daya tsangwami kanshi yake ganin shine umul abaisan faruwar komai.



πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–



Washegari da zazzafan zazza6i saudart ta tashi.

Sosai Alhaji shamsu ya rude don jin jiki take sosai kuma taqi yarda akaita hospital saidai aka kira family doctor dinsu yazo hargidan.


Ranar wuni yayi tareda ita bekosan motsawa daga gefenta, duk motsin dazatayi saiyayi mata sannu, he's feeling guilty, yanajin duk shine silar komai, hqr kau har saudart tagaji dajinshi abakinshi. Haka ranar tazo tawuce masu dukkansu cikin qunci.


A 6angaren ashraf kau sai abinda yayi gaba.

Haka shima yawuni sukuku, saidai kaganshi zaune ya kafe waje daya da idanu yana tunani.

Baya fita gidan sai yaga lokacin sallah yayi sannan yafita masjid, daga nan kuma sai dakinshi.

Idan kuma ya sauko qasa to ankirashi ne ya sauko yaci abinci wanda ko kwata beci zai tashi wai ya qoshi daganan kuma yakoma daki ya dasa daga inda ya tsaya.


Ganin tunane tunanen bazasu amfaneshi dakomai ba yasashi tashi ya daura alwala misalin shabiyu na dare yahaye sallaya yaita nafilfili yana addu'ar allah yabashi haquri da juriyar rabuwa daita yakuma yayemashi sonta kamar yadda ya doramashi don shi yarigada ya fidda rai da kasancewa tareda ita.





Saida tayi kwana biyu kwance sannan tadanji sauqi.

Damun daddy tayi da kuka akan ita gidan mamy zata don tasan tana fushi daita.

Ganin bata ida warwarewaba yaso hanata dafarko amma ganin ta burkucemashi yasashi yarda akan tayi hqr zaikaita dakanshi washegari.

Haka ta haqura badon yasoba.


Washegari sukuku ta tashi, fargabar haduwarsu kawai take da mamy don tasan haduwarsu won't be funny at all.

Haka ta shirya jiki amace kallo daya zaka mata kasan atsorace take.

Daddy ne yaita kwantarmata da hankali ganin yadda duk ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login