Showing 51001 words to 54000 words out of 224014 words

Chapter 18 - Kanwar Maza 1&2 Hausa Novel Complete

12 Dec 2024

1075

wai babata tsohuwa, shi ne ni kuma na zana babarsu a allo, ta dakeni kuma aka bani rashin gaskiya, ni kuma washegari na rama, ina ga aljanuna ne suka tashi, na yi mata irin na 'yan wrestling, amma wallahi ban san za ta karye ba, raina ne ya ɓaci sosai"

Headmaster da tun da aka zo bai ce komai ba, sai girgiza kai kawai da yake yi, dan ya rasa me ma zai ce, bai taɓa zaton haka rumaisa take ba.

Headmaster ya numfasa ya ce "Yanzu dai tun da sabga ce ta yara, ayi ƙoƙari a sulhunta kowa ya yi haƙuri"

Babar Asiya kuwa kallon ruma kawai take, yadda take bayani da confidence, tana ciye-ciye kuma aka rasa mai tsawatar mata, sai ma nema ake a goyi bayan ruman.

DPO ya kuma kallon ruma ya ce "Matso nan kusa da ni 'ya ta, magana za mu yi"

"A'a, ba na zama a kusa da maza, Huzaifa ya ce idan ina zama a kusa da maza haihuwa zan yi, kuma korata za ayi daga gidanmu, idan aka koreni kuma ban san in da zani ba, rannan ma Allah ne ya taimakeni, da malam Habibu ya taɓa mini hannu ban haihu ba, mama ta ce lafiyata ƙalau ba ni da ciki".

ba ƙaramin dariya ruma ta basu ba, Aliyu ya dafe kai ya sunkuyar ƙasa, ita ruma ba ta san rufi ba, ko zaka kasheta za ta faɗi gaskiya ne".

Duk yadda aka so yin sulhu, babar Asiya taƙi yarda.

DPO ya ce "Yanzu Madam, so ki ke a kai ku kotu ke da wannan yarinyar jikarki ko kuwa?"

Aliyu ya ce"Yallaɓai, ta ƙirga abin data kashe, in sha Allah ba zai gagara ba sai a biyata"

Sai da ta ji haka hankalinta ya ɗan kwanta, ta lissafa kuɗi dubu talatin da biyar ta ce a biyata.

Aliyu ya ce"Yallaɓai a nema mana sassauci, wallahi yarinyar nan marainiya ce, kuma na gaya maka, tana da matsalar ƙwaƙwalwa, ana kai ta shan magani, ana ta abin da za a ci ga karatun ta, ga rashin lafiya abun da yawa"

"Wallahi lafiyata ƙalau, ni bana rashin lafiya sai zazzaɓi, ko gudawa, amma dai wataran idan raina ya ɓaci sai na ji aljanuna sun tashi, ƙarfina ya ƙaru, idan na kama mutum na dunƙule hannu na dinga dukansa ko hmmm ba a magana, da na ce na daina dambe saboda mama ta daina fushi, ita Asiyar ce ta janyo muka yi faɗa".

Aliyu ya ce "Dalla rufewa mutane baki, Yallaɓai ba ta da cikakkiyar lafiya"

Headmaster ya ce "Amma ai mu da ku ka kawota makarantar baku gaya mana ba"

Babar Asiya ta dage, ba zata rage ko sisi ba, DPO ya ce zai biya dubu ashirin a aljihunsa, su ruma su biya dubu goma ".

Aliyu 'yan kuɗin registration ɗin sa ne da yake tarawa, haka ya biya, suka din ga bada haƙuri shi da ruma.

Duk da wannan abu, babar Asiya ba ta huce ba, dan ta so a zane ruma, sai dai bisa ga mamakinta yarinyar sa'ace da ita, babu wanda ya daketa, sai ma nasiha da DPO ya yi mata, yana cewa Aliyu "Ka ga irin wannan yaran, idan aka yi haƙuri, suna da ɓoyayyiyar baiwa da Allah ya yi musu, da al'umma za iya amafana, ku yi haƙuri ku cigaba da kai ta Asibiti tana ganin likita, da sauƙi tun da har tana iya zuwa makaranta, sannan ku kiyaye abin da zata din ga kallo".

"Kaii wallahi ni babu wani likita da nake gani, nifa lafiyata ƙalau, wato Yaya Aliyu kana nufin ni mahaukaciya ce?" Harar ya watsa mata yana yi mata daƙuwa suka cigaba da magana da DPO.

bayan sun fita daga ofishin, Headmaster ya ce ruma ta zauna a gida, sai wani satin sa duba su gani idan zasu iya bari ta cigaba da zuwa makarantar.
Tsalle ta yi tana faɗin Alhamdilillah.

Aliyu ya girgiza kai ya ce "Mara hankali kawai"

******
"Takawarka lafiya magajin galadima, Allah ya baka yawan rai, ya ja kwanan hajiya" ɗaya daga cikin hadiman Mummy kenan, da ta ware maƙogwaro, take ta zabga wa Adam kirari kamar za ta dungura, maƙogwaronta ko zafi ba ya yi mata.
Hannu ya ɗaga mata, ya cigaba da tafiya zuwa cikin falon.

Sanyi A.C ya cika ɗakin, ga ƙamshin turare da ya haɗu ya gauraye falon.

Risunawa ma'aikatan da ke cikin falon suke yi a gareshi, tamkar sun ga sarki.

Jinjina musu kai ya yi, ya nemi wuri ya zauna a ɗaya daga cikin kujerun falon. Ya shafe a ƙalla mintuna takwas, sannan ta fito cikin wata haɗaɗiyar shadda sai ɗaukar ido take yi.

Ta na ganin Adam, ta yalwata murmushin fuskarta ta ce "Hutawarka lafiya takawa, fatan ana lafiya? Kuma ina fatan ba a gaji da jirana ba, ina shiryawa ne"

Girgiza mata kai yayi ya ce "Barka da wannan lokacin"

"Yauwwa barka dai, an dawo lafiya ya ibada?"

"Alhamdilillah"

Ta sake yin murmushi sannan ta ce 'Ai har na fara shirin zuwa da kaina na kwashi gaisuwa, na ji labarin ka dawo, amma ba ka zo mun gaisa ba, kuma har aka yi bikin gidan Turaki aka gama ban ganka ba, ko jikin ne?"

Ya ɗaga idanuwansa ya kalleta, amma bai bata amsa ba.

"Well, kun haɗu da Mahmud kuwa?, yazo gari shima ya kusa komawa ma, ya dawo lokacin kana saudiyya"

"Dama zuwa na yi na gaishe ki, and a gayawa su Fauziyya ba na son yawan fitar nan" yana kaiwa nan a maganarsa ya miƙe, ya fara takawa sannu a hankali.

Murmushi ta yi ta bi bayansa da kallo. "A zahiri mutum har mutum, amma baɗini ba wanda ya san cikakken waye, kamar bil adama kamar kuma wani abu daban, da ni ki ke zancen Binta, sai na rabaki da komai sai na tabattar da na huce a kam abin da kk ka yi mini" ta yi maganar a hankali tana bin bayan takawa da kallo.

Ya kai tsakiyar falon, Mahmud ya buɗe ƙofar ya shigo, ganin junansu ya sanya suka yi turus, suna musayar kallo, kamar abokan gaban da suka yi shekara da shekaru ba su haɗu ba sai yau.


LITATTAFAN DA NA RUBUTA SUN HAƊA DA.

ABDULJALAL (FREE BOOK)
AƘIDATA (BOOK1 FREE 2 PAID)
WATA KISSAR SAI MATA (FREE)
WUTA A MASAƘA (FREE)
RUƊIN ƘURUCIYA (BOOK1 FREE 2 PAID)
GABA DA GABANTA (1FREE 2 PAID)
ƘANWAR MAZA (1FREE 2 PAID)

Mai buƙata ni zai tuntuɓa ta lambata Please, a din ga biya kan a karanta, in kin sai littafi baki faɗi ba, atleast kin taimaki marubuciyar da bata ƙwarin gwiwa 😒


https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
*Wai ina da ku fans, ace haryanzu ban haɗa 1k subscribers a channel ɗi na ba, anya akwai amana kuwa😒*


Taku har kullum
Ayshercool
08081012143
[24/07, 7:43 pm] JAKADIYAR AREWA:                     *ƘANWAR MAZA*




Na Aisha Adam (Ayshercool)

MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES

*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHI YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR  DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA? TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN FATA NE? KO KUWA SO KI KE FATARKI TA DIN GA SHEƘI TA NA HASKAWA? MAZA KI GARZAYO WURIN MEENA DOMIN SAMUN MAFITA*

*Royal jelly big 22000*
*Royal jelly 30 pieces 2200*
*Royal jelly small one 60 pieces inside the pack 3000*
*Vitamin C-100, 2700*
*Vitamin E big 3000*
*Pesona 2300*
*Dara 2300*
*Cantik ayu 2300*
*GLUTA white 2700*
*Khusus ibu 3800*
*Sugar wanita 3500*
*Majakani 3 in 1 3200*
*Eve Care 3700*
*Juliet eve 11,500*
*Phyton buster 18,000*
*Phyton collegen 18,000*
*Glute sparkling 18,000*
*7 days ginger oil for hair 1,200*
*Papaya oil for breast 1,200*
*Garlic oil for hips 1200*
*Vitamin C serum 1,500*
*Vitamin E serum 1,500*
*Busty blend 2800*
*Gluta prime 2800*
*Collegen+C 3800*
*Yan uwa abun fa da yawa bazan iya kawosu gaba daya ba amma muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
*Wai ina da ku fans, ace haryanzu ban haɗa 1k subscribers a channel ɗina ba, anya akwai amana kuwa😒*

Ku yi subscribing  YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro



Page 16

Kallon-kallo suka shiga yi wa juna, aka rasa wanda zai bawa wani hanya, Mahmud ne ya fara janye nasa idon ya wuce yana wani irin taku cike da rainin hankali, ya bawa Adam hanya.
Cikin hanzari Adam ya bar falon, yana jin wani abu yana tsikarar zuciyarsa.

Adam na fita, Mummy ta taso ta na faɗin "Mahmud ya haka, meyasa ba zaka tsaya ku gaisa ba, kamar ba ɗan uwanka ba?"

Mahmud ya ce "Mummy, ni baki ga abin da ya yi mini ba? Lokacin da ya sauke girman kai ya duƙa mini, wataƙila na fara saurarasa"

"Haba Mahmud, shi ne fa gaba da kai, ya zaka ce haka? ni fa bana son ace ina ziga ka, kuma ko ba komai ya ci sunan mai martaba, ya cancanci ka girmama shi, kuma idan Allah ya sanya sarautarmu ta dawo gidan nan, ka san shi ne magajin babanku, shi zai zama galadima tun da shi ne babba"

Ya dubi Mummy ya ce "Ni wata sarauta ko wani abu makamancin haka bai dameni ba, a naɗashi sarki ma gaba ɗaya, wannan shi ta shafa, look Mummy, a bar wannan zancen ni bani da lokacinsa, bari na je na karya"  yana gama maganar ya wuceta, ya na bada baya, Mummy ta yi murmushi ta ce "Haryanzu ina wasana yadda nake so, Mahmud dole na ɗarsa maka zaƙin mulki da ƙaunar sarauta, sannan kuma azo a rasa sarautar gaba ɗaya mu je zuwa".

****
Aliyu suna tafe a hanya, yana ta yiwa ruma faɗa.

"Dan ubanki kuɗin makaranta na, na registration na fara tarawa, yanzu kin saka na kwashe na bayar a banza, ban ci ba ban sha ba, dan ma Allah ya sanya DPO ya biya mafi yawa daga kuɗin. Saboda ba ki da mutunci ina kareki ki na ƙaryata ni, ni dama na ƙyaleta ta yi miki shegen duka".

Ta waro ido ta ce "Kaii, idan ta sumar da ni fa?"

"Ai gara ta sumar da ke ɗin, tun da ke dai har abada ba kya hankali, wai ki ka karya 'yar mutane saboda tsabar kanki ba daɗi"

"To ba kai ne ka ce mini mahaukaciya ba, wai ana kai ni asibiti"

"To meye marabarki da mara hankalin? Zaki gane kurenki ne, bari mu je gidan sai na daki kuɗina" har suka isa gida, ruma ba ta sake cewa komai ba.

Mama na ganin Aliyu tare da ruma sun dawo, ta fito daga ɗaki ta na tambayar ko lafiya?

Ruma ta ɗan sosa kai tana kallon Aliyu.
"Zaki dai na kallona ko sai na tsokane idon? Sai ki yi mata bayanin abin da ki ka yi ai".

Ruma ta kalli mama, kamar zata yi kuka ta ce "Wallahi mama tsautsayi ne"

"Tsautsayin me? Me ki ka aikata kuma?" Ruma ta yi tsilla-tsilla da ido.

"Ba zaki gaya mata ba"

"Mama, da wasa fa na gwada irin na wrestling ɗin nan, shi ne wata ta karye"

A ɗan hasale mama ta ce "Kai ka gaya mini abin da ta yi mana, ka tsaya ka na mini wasa da hankali".

Aliyu ya yiwa mama bayanin abin da ruma ta aikata, da yadda suka yi, zuwansu police station yanzu.

"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Allah ka shiga lamarina, Allah ka dubeni a kan halin wannan yarinyar".

"Mama dan Allah ki yi haƙuri ba zan sake ba, ita ta fara tsokanata na rama, ban san zata karye ba wallahi"

Mama ta dube ta ta ce "In dai kece, ba zaki canza hali ba, yanzu ruma har ta kai ki ga zuwa police station ruma, kaf yaran nan yayyenki babu wanda ya taɓa zuwa wurin 'yan sanda, sai ke ruma ko? Allah ya yi miki magani, ki je ki yi ta yi kar ki fasa" mama na gama maganar ta shige ɗaki ta bar ruma a wurin.

Ruma ta kalli Aliyu ta ce "Kai baka da rufin asiri, wallahi da yaya usy ne zai rufa mini asiri, amma na fuskanci da kai da Yasir, da Huzaifa baku taɓa rufa mini asiri ba, ƙiris ku ke jira .....

"Dalla rufe mini baki, tun ban daki kuɗina a jikinki ba, dubu gomar nan ta tsaye mini, ni Wallahi da ma ƙyaleki na yi su yi miki duk abin da suka ga dama" ɓata fuska ta yi, ta bi bayan mama, sai dai mama sam taƙi kulata, wanda hakan ba ƙaramin tayar wa ruma hankali yake ba.

Wunin yau gaba ɗaya aka rasa mai saurara ruma, duk wanda ta yiwa magana sai ya hantareta gaba ɗaya haushin abin da ta yi suke ji.

"Hmm huzaifa ni fa Allah ne ya taimake ni, da matar cewa ta yi sai ta dakeni, ka ganta kuwa, ƙatuwace sosai da sosai fa, a kan benci ta zauna, kaga hannun ta a cure da nama, idan ta dakeni ai ji zan kamar an buga mini guduma"

Usman ya ce "Sai na zubar da haƙoranki, ba zaki nutsu ba ko?, ki ke cigaba sa kwatanta yadda take, ina ma Alin ya bar ta ci ubanki, ke ban da rashin kan gado, kawai ki je ki karya 'yar mutane saboda tsabar wauta ta yi miki yawa, sai ka ce wata rainon gaɓa-gaɓa?"

Aliyu ya ce "Kai ba ka san abin takaicin ba ma, har da wani cewa ai aljanunta ne suka tashi, ba a hayyacinta ta daki yarinyar ba, tsabar cin kai"

Mama ta ce "Ba ku ne ku ke zigata ta ɗauko magana, ku ka ce kun tsaya mata, dole ta yi abin da ta ga dama ai, kuma daga yau duk wasu tashoshi na wrestling a gidan nan sai an sauke mini su, an daina kallon sa a gidan nan, kai kallon ma sai an daina"

Ruma ta waro ido ta ce "Mama, shikenan sai na daina ganin saurayina na wrestling"

Usman ya ce "Au ke har wani saurayi ne da ke a wrestling ɗin?"

"Eh mana, ba ka san shi bane, Huzaifa ya ma sunan sa, ɗan tuna mini, idan na ganshi har wani daɗi nake ji".

Huzaifa ya ce "Ke ki ka san shi ni ban san shi ba"

Yasir yayi tsaki ya ce "Wallahi Mama mi bamu go ahead, mu yi wa yarinyar nan ruƙiyya ni da Huzaifa, mu samo tsumangiya in cuɗa mata jikinta in haɗa da ayar Allah wallahi dolen aljanun na ta su magantu"

"Wallahi ni ba ni da aljanu sai raina ya ɓaci, kuma na sha tabara da ayatul kursiyyu, na fi ƙarfin aljani da makiri ko tsunburbura na fi ƙarfinta"

"Ke dalla ware, ai ke kin fi tsunburburar ma rashin ji" suka din ga caccakar ruka kamar zasu daketa.
Ita damuwarta a kan mai sunana Baba ne, hukuncin da zai ɗauka a kan ta, na abin da ta aikata, sai ta ji bai ce komai ba ma, yayi shiru kamar bai san me aka yi ba.

***
Tsaye yake a bakin wardrobe ɗin, yana ƙarewa kayan ciki kallo kamar ba nasa ba, ya saka hannu da nufin ya ɗauko kaya, hannunsa a sauka a kan koriyar alkyabbarsa.
Kamar ya na jin tsoron Alkyabbar, ya zarota ya na kallonta.
*Sarki mai koriyar alkyabba a dawo lafiya, ka ɗanani a kan dokinka ko ka bani kyautar doki*
Shiru ya ɗan yi ya na tunani, ta yaya zai ji murya ɗaya a mabanbantan wurare, kuma haryanzu bai kai ga ganin fuskar wacece ba, gashi a duk lokacin da zai ji muryar, sai ta kira shi da sarki!.
Ajiye Alkyabbar ya yi, ya ɗauko wata dark blue ɗin suit, ya shirya a cikinsu ya ɗauki jakarsa ya fita.
A ɗaki ya tarar da Ammi tana sallar walaha, ya zauna ya jira ta idar.
Ta idar ta kammala Adduointa, sannan ta kalli Adam ta ce "Barka da wannan lokaci takawa".

Yayi murmushi ya ce "Barkanki Ammi, zan wuce ne"

Cikin tausayawa ta kalleshi ta ce "Ka na ganin babu matsala, zaka iya zuwa aikin?"

"Babu wata matsala in sha Allah"

"To matso na yi maka addu'a" ba musu ya matsa kusa sa Ammi, ya durƙuso mata da kansa, ta ɗora hannunta na dama a kan nasa, ta dinga kwararo masa Adduoi.
Wata irin nutsuwa ya din ga ji ta na ratsa shi, ya lumshe idonsa, sai da ta idar, sannan ya riƙe hannun ya sumbaci hannun ya ce "Allah ya ja zamanin giwar Galadima, ya baki yawan rai, Allah ya jiƙan Galadima"

Murmushi ta yi, tare da jin maganar har cikin ran ta ta ce "Amin takawa, Ubangiji Allah ya tsare" ya miƙe yana faɗin Amin, ya bar ɗakin.

***
Tun da abin nan ya faru, an kai ruwa rana sosai, kan malaman su ruma su yarda ta cigaba da zuwa makarantar, bisa sharuɗai sannan ruma ta cigaba da zuwa makarantar.
Tun baya da aka yi sulhu a police station, duk ranar juma'a sai mama ta aika wani ya tasa ruma a gaba sun je duba Asiya, sun kai wani abu, amma kullum babar Asiya babu godiyar Allah, kullum suka je sai ta yi complain, ita kuma ruma kan su taho, sai ta aikata wani abun da za ta sake tunzarata tayi ta masifa.
A haka duk suka ce sun daina zuwa, yau mama ta ce dan Allah mai sunan Baba ya saka ruma a gaba su je.
Tun da Allah ya sa babar Asiya ta yi arba da fuskar mai sunan baba, ta shiga hankalinta, ko maganar kirki ta kasa sai kame-kame.
Tun da suka gaisa, ya bata abin da zai bata, ya ce ruma ta tashi su tafi, ko yaya mai jiki bai ce ba balle ya ce Allah ya kyauta.

suka taho hanya, ruma a nutse take babu tsokana da hauma-hauma, saboda kura ta san gidan mai babban sanda.
da suka zo bakin layin su, cikin girmamawa ruma ta kalli mai sunan Baba ta ce "Mai sunan Baba, mama ta ce na taho mata da kayan miya a wurin Hudu"

Ya kalleta ya ce "Idan kin ga dama, ki tsaya hauma-hauma da neman magana a hanya, zaki zo ki sameni".

"In sha Allah ba zan yi ba"

Ganin da mutane a wurin Hudu, ya sanya ruma ta tsaya ta na jira, sai dai kan ya kawo kanta, ta ɗau wuƙa ta din ga daddatsa masa kabewa bai sani ba.

Da ta gaji ta ce "Malam hudu ka sallameni mana"

Ya ce "Yi haƙuri na fara sallamar matan aure, su da zasu ɗora girki"

Ruma ta yamutsa fuska ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login