Showing 105001 words to 108000 words out of 224014 words

Chapter 36 - Kanwar Maza 1&2 Hausa Novel Complete

12 Dec 2024

1117

kuka, Abubakar yana rarrashinsu, Abdallah ma ya haɗe kai da gwiwa usman kuwa ya zuba tagumi yana bin su da kallo, hannunsa riƙe da Alqur'ani, Aliyu ne kawai a kwance shima kuma ba bacci yake ba.

A hankali mai sunan Baba ya ja da baya, ya koma tsakar gida ya zauna, yama rasa ina zai saka kansa, shima da hali kukan zai yi, ya riga ya gama karaya.

Wayewar garin Allah, jikin ruma ya ƙara tsanani, sai rawar jiki take tana kwarara wani irin koren amai, ga kukan ciwon ciki da take yi duk ta fita hayyacinta.

Babu wanda ya damu da halin da take ciki, sai wannan matar, da a yanzu ba ta kanta take ba ta ruma take, saboda tausayin da take bata, sai sannu take yi mata, tun tana iya amsawa, har ta daina .

Cikin damuwa matar ta ce "Dan Allah bawan Allah ku taimaka ku kai yarinyar nan asibiti, kar ta mutu a haka, wallahi tana jin jiki sosai".

"Idan ta mutu meye naki? Ki ji da kanki mana uwar shishshigi" wani daga cikinsu ya bata amsa.

Cikin damuwa ta ce "Amma yarinya ce, dan Allah ku taimaka ko magani ku sai mata kar ta galabaita" banza suka yi mata suka cigaba da shaye-shayen su.

Kamar zata yi kuka, sai sannu take yi wa ruma tana dafa goshinta.

Ruma kuwa sai jujjuya kai take tana kiran sunan mama, duk ta fita kamar ta shekara tana ciwo.

Ko da rana ta ɗan ɗaga idon matar nan yayi ja, jikinta sai rawa yake saboda yunwa da take ji, ga ɗan cikinta sai motsi yake, ga mura da ta addaba mata, amma tafi tausayin halin da rumaisa take.


Mijin iya ne wato dagaci a tsaye a tare da wannan dogon mutumin da su ruma suka taɓa haɗuwa da shi.

"Dan Allah dogo ku taimaka dan zatin Allah ku sako yarinyar nan, ko ku faɗi abin da za a baku, ba 'yar garin nan bace ba, a mayar da ita hannun ahalinta wallahi marainiya ce".

Dogo ya ce "Ni ba 'yan ƙungiyar mu ne suka kawo farmaki ba, kuma dama yarinyar na ga kanta yana rawa, tun da aka kai wannan lokacin ba su ce muku komai ba, wataƙila sun kasheta".

Cikin kiɗima dattijon ya girgiza kai ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, dan girman Allah tun da baka tabattar ba ka duba mini, waɗanda suka sako suka dawo gida,  sun ce mana tana can a raye, dan girman Allah ka duba mini ka sanya baki a lamarin nan dan Allah"

"Ni ne zan saka bakin? Su sha tara ne fa suka yi aikin, ban maka wannan alƙawarin ba, zan dai je na duba maka ko tana nan"

Dagaci ya ce "To shikenan, hakan ma na gode sosai"

***

Mummy na barin gidan wambai ta tafi gidan aminiyarta Hajiya Lubabatu, domin fesa mata labarin da ta guntso a gidan wambai.
Sam labarin bai yi wa Hajiya Lubabatu daɗi ba.

Cikin hasala take cewa "Yanzu saboda tsabar wulaƙanci ace har yana shirin yin murabus amma ni ban sani ba".

"To da baki sani ba ni ba gashi na gaya miki ba, kuma shi yana can Germany ke kina nan ta ina zaki sani?"

"Amma shima wannan wamban ƙasurgumin munafuki ne"

Waro ido mummy tayi ta ce "Rufa mana asiri kar wani ya ji mana, ke ai ba a wannan yakamata ki mayar da hankali ba, wai yana tunanin idan yayi murabus Adam za'a dawo wa da sarauta, sai dai na gyara miki hanya, dan na kunno mus wuta daga shi har uwarsa, dan sai da na tabattar da na fusata shi sosai a kansu. Yanzu dai ki nemi Jabir ku tattauna a kai, ku yi duk iya ƙoƙari kar a rabaku da sarautar nan, Jabir ya gaji ubansa".

Hajiya Lubabatu ta ce "Ai faɗa ma ɓata baki ne, ai dan ubansa dole ya zo ya san abin yi, ya tare a gindin Adam sai ka ce ubansa".

"To wallahi ku san abun yi"

"Kar ki damu zaki ji ni" daga haka suka cigaba da hirarrakin su.

****
Kamar a bayi haka aka fara rabawa su ruma abinci, gurasa ɗaya da ruwa ɗaya, haka ake basu kullum, sai ranar da Allah ya kawo wannan mutumin, ya kan kawo mata abinci.
Wannan matar kuwa ko magana ta kasa saboda a wahale take, ji take kamar yunwa za ta kasheta.
Ko da aka bata gurasar nan ba ta tsaya komai ba, ta yi loma uku da ita, saboda azabar yunwar da take ji.

Ruma ta miƙa mata tata ta ce "Gashi ki ƙara da tawa ni na ƙoshi".

Matar ta girgiza kai ta ce "A'a, ke ce baki da lafiya, ki daure ki ci, sai ki ji ƙwarin jikinki" ruma ta girgiza mata kai alamar a'a.

Matar ta saka gefen zaninta, ta sharewa ruma gumin da ta fara yi, saboda zazzaɓin jikinta ya sauka.

Mutumin da ya tinkaro su, ruma ta tsaya ta zubawa ido, sarai ta gane shi, mutumin da ya tare su yana tambayar wacece ita?
Kenan duk rabin mutanen garin abu ɗaya suke yi kenan, satar mutane? Ta tanbayi kanta.

Suka gaisa da 'yan bindigar da suke wurin, ya yi musu magana da yaren da ruma ba ta iya ji.

Suka amsa masa, sannan ya shiga duba mutanen wurin, can ya nuno ruma, ya ce "Waccan ce".

Ƙaton da ya taɓa dukan ruma da bakin bindiga ya tashi ya je ya danƙo ruma, kamar an yi cinikin kaza za a sayar haka ya fizgota, cikin dakiya ta fizge hannunta tana haki.

"Bata da lafiya ka yi mata a hankali" cewar matar da haryanzu ruma ba ta san sunanta ba.

"Ke idan baki kiyayeni ba, da shiga abin da ba a saka ki ba, wannan cikin naki ba zai hana na keta miki haddi ba a gaban jama'a ba, ki shiga hankalinki" daga haka ya mayar da idonsa kan ruma ya ce "Wannan ka ce ko?"

Dogo ya ce "Eh ita, ya ce ku taimaka ku faɗi abin da za'a bayar ku bayar da ita"

Ya ƙyaƙyace da dariya ya ce "Ai wannan ta zama tamu, ba zamu bayar da ita ba, ta ce sai da a kashe ta a wurin nan, dan haka muma muna so,  su yi haƙuri su mance da ita, ko su fansheta da 'yan mata biyar, dan ni ba dan barde ya saka mini ido a kanta ba, da tuni ta zama yarinyata, kawai su je idan ubanta da sauransa yayi wani ƙoƙarin su haifi wata, wannan kuwa ba zamu bayar ba" yayi maganar yana ƙoƙarin rungumo ruma jikinsa.

Duk da yadda take a galaibaice, amma haka ta dunƙule hannu, ta ɗirka masa duka a ciki.
Sak suka yi gaba ɗaya suna kallonta, kamar wata zakanya, ta ja da baya ta dunƙule hannu "Wallahi idan ka kuma taɓani sai na yi maka duka, ni ba 'yar iska bace ba, wane irin azzalumai ne ku? Ba kwa tausayinmu? Muma fa mutane ne kamar ku, kar Allah ya sa ku sake ni, ku kasheni ka kasheni idan kai ɗan halak ne, ni a duniyar nan bana tsoron kowa sai Allah La'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimin" cikin tsananin ƙwarin gwiwa take maganar ga jikinta yana tsuma.

Ƙare mata kallo ya yi, dudu tsayinta bai fi cikinsa ba, ko a shekaru baya tunanin tayi sha huɗu, ko maza surrender suke idan suka shigo hannu amma yarinya ƙarama ta tsaya a gabansa tana wannan maganar.

"Dan Allah ka kashe yarinyar nan mu huta, sun hana a taɓata sun ƙi bari a saketa duk ta gallabi mutane, barde yana da matsala, kalli yadda take rashin mutunci fa" ɗaya daga cikin mutanen yayi maganar yana gyara bindigarsa tare da saita ta a kan ruma.

"Kai kuma ban saka da kai ba, idan kuma na kasa da kai to ka kwashe, kuma in sha Allah ba zaku gama da duniya lafiya ba, sai kun ga abun da Allah zai yi muku".

Murmushi ƙaton nan yayi cikin ƙarfin hali, da jin kunyar dizgin da ruma ta masa ya ce "Idan ka kasheta a yanzu ai ta ci bulus, bari in gwada mata tabon da zata tafi lahira da shi, yau ko ni ko barde amma sai na nunawa yarinyar nan iyakarta, ni ki ka ce zaki daka ko?"

Ruma ta sake gyara tsayuwa ta ce "Wallahi kana taɓani sai na ware ƙwanjina, na rama kai ka san wace ruma kuwa?"

Dogo kuwa kamar soko haka ya riƙe hannu yana kallon ikon Allah.

Cikin magiya da kuka matar nan ta fara "Dan girman Allah kayi haƙuri, kar ka yi mata wani abun zafin ciwo ne"

Ruma ta ce "Ba wani zafin ciwo, a hankalina nake, wallahi ya taɓani sai na rama, bana tsoron kowa a wurin nan"

Ya shammaci ruma ya danƙonta, zai fizge hijjabinta da yayi daƙal-daƙal saboda dauɗa, ta riƙe hijjabin ta shiga kai masa duka da hannu ɗaya tana wani gurnani da ihu kamar zakanya.

Ya saka kan bindiga ya ƙwala mata a ka, ihu ta yi ta durƙushe a wurin, sai ga jini ta hancinta.

Tasowa matar nan ta yi da ƙyar ta nufo su, sai dai kan ta ƙarasa ruma ta miƙe cikin tangaɗi ta saka hannu ta dintsi ƙasa da ciyayi, ta watsa masa a jikinsa, gaba ɗaya suka taso suka yo kan su.
Riƙe ruma matar ta yi ta shiga tsakiya, ta haɗa hannayenta biyu cikin magiya 🙏
Ba ta yi maganar ba ya hankaɗeta ƙasa, ta fasa ihu jin kamar a take ɗan cikinta zai faɗo, wani irin gigitaccen ciwo ya ɗaure mararta zuwa ƙafafuwanta.
Hankalin ruma ya koma kan matar, ta nufeta da sauri, amma mutumin nan ya kwarfeta, ya sanya bindiga ya dinga kwaɗa mata, yana takata da ƙafarsa, ihu take amma bakinta yaƙi mutuwa "Idan ka isa azzalumi ka kasheni, kuma in sha Allah yadda Allah ya kuɓutar da Annabi yunus a cikin kifi, ya kuɓutar da Annabi Ibrahim daga cikin wuta, sai Allah ya kuɓutar da mu, haka malamin mu ya ce mana mu yarda da Allah, in sha Allah zai saka mana" ya daka ya daka ya takata, ya sanya wani itace ya maka mata a baya. Wani irin ihu ta kuma yi, bakinta da hancinta na ta zubar da jini.
Tuni ta fara gani dishi-dishi, gadan gadan ya nufi ruma, ya durƙusa a kanta ya kama skirt ɗin jikinta ya fara ja.

Ayshercool


*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR  DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*

*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*

👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*

*1.  Supplements na gyaran jiki ciki da waje*

*2.   Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*

*3.  Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*

*4.  Supplements na karawa fata kyau da sheki  glowing skin*

*5.   Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6.   Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*

*7.   Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*

*8.  Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*

*9.  Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*

*10.  Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*

*11.  Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*

*12.  Supplements na gyaran HQ ciki da waje*

*13.  Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14.  Supplement na whitening/glowing skin*

*15.  Supplement for Acne, dark spots remover*

*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*

*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*


Paid book ne, 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143, wanda suke ba a Nigeria ba kuma, za su iya saya a arewabooks*





Salati da salallami mutanen wurin suka fara yi, duk rashin imanin mutanen, idan suka so keta wa haddi, suna barin idon mutanen da su, amma yana nema ya keta ruma a gaban su.

Wasu kuwa gani suke ruma ita ta janyo wa kanta, tsananin ciwon da matar nan ke ji bai hanata jan jikinta zuwa in da suke ba, ta riƙe rigarsa tana kuka tana girgiza masa kai. Wani irin mari ya kwaɗa mata, da a take shatin yatsun sa suka bayyana a kan kuncinta.
Ɗaya daga cikinsu ya zo ya saka hannu ya dinga jan matar a ƙasa, ya wancakalar da ita a gefe.

Ya kuma danƙar skirt ɗin ruma, amma cikin ƙarfin hali ta riƙe.

Ji yayi an fincikoshi ta baya, an kwaɗa masa mari.
A gigice ya kalli wanda ya mare shi, barde ne wanda ruma ta bawa gyaɗa kuma yake kawo mata abinci wasu lokutan.

Wata irin ashar yayi masa, cikin ƙaraji ya ce "Me ka yi mata? Me na ce maka da aka kawo ta? Au har ka manta zaka karya yarjejeniyar?"

"Amma ai ka tsaya ka ji meyafaru kan kayi mini haka"

Cikin hasala barde ya ce "An maka ɗin, wallahi da ka aikata abin da ka yi niyya, da sai na yi gunduwa-gunduwa da namanka a wurin nan" cikin huci ya nufi kan ruma, jikinta duk shaidar duka.

Ya ɗagota ya girgiza ta, ta buɗe ido ta kalleshi, a hankali ta fizge hannunta daga nasa ta mirgina ta kwanta a gefe, tana kallon matar nan, da take ta sauke numfashi da ƙyar, kamar sumammiya.

Bai sake ƙoƙarin taɓa ruma ba, ya ja ƙaton nan yayi gefe da shi yana yi masa magana.

Ruma ba ta sake bi ta kansu ba, a hankali ta mirgina, ta ƙarasa in da matar nan take kwance, tana numfarfashi, ruma ta ɗora hannunta a kan na matar, a hankali ta ji matar ta riƙe hannunta, ta sake matsawa jikin matar ita ma tana mayar da numfashi ba tare da wani ya tankawa wani a tsakanin ita da ita ba.

Dagaci kuwa tun da suka yi magana da dogo, a kan zai je ya bincika masa ruma, ya kira Aliyu ya sanar masa domin hankalinsu ya ɗan kwanta, dan haka suka cigaba da dakon abin da dagacin zai ce masu, gashi Aliyu ya riga ya gaya musu yadda suka yi dagaci, dan haka mama kullum sai ta tambayi Aliyu, haryanzu dagaci bai yi magana ba?.

***
Kasancewa Adam ba a family house ya kwana ba, Kamar kullum bisa ga al'ada yana biyawa ya gaida Ammi, dan haka yau ma a cikin hanzari ya yake tafiya, ya ƙarasa sashinta.
A bedroom ya tarar da ita, sai dai saɓanin kodayaushe, ya tarar da fuskarta a haɗe, hakan ya tabattar masa da akwai damuwa.

Sai dai ya bari sun gama gaisawa, sannan ya ce "Allah ya baki yawan rai, lafiya na ga fuskar ki babu walwala?"

Ammi ta ce "A'a lafiya ƙalau, wambai ne ya bani saƙon cewa idan ka tashi daga aiki, yana nemanka" sak takawa yayi, ya dubi Ammi ya ce "Wani abu ne ya faru?"

"Ni ma ban sani ba, kawai dai ya ce yana nemanka?"

"Ko laifi na yi mass?" Adam ya sake tambaya.

"Ban sani ba takawa, ka je dai ka ji ko menene"

"Shikenan" ya faɗa a taƙaice, ya tashi ya ce "Na tafi".

"Allah ya tsare" Ammi ta faɗa ba tare da ta kalleshi ba.

Har ya kai bakin ƙofa Ammi ta ce "Adam!" Sai da tsigar jikinsa ta tashi, dan abu ne mai wahalar gaske ta kira sunansa haka kai tsaye.

Ya tsaya ya waiwayo ya kalli Ammi.

"Idan ka je wurinsa, ko me zai ce maka ban yadda ka tofa ko ka yi ƙoƙarin kare kanka ba, ka bishi da to kawai"
Ɗan shiru yayi yana nazari, akwai wata a ƙasa kenan, a zahiri kuma ya ce "To, in sha Allah".

A falo ya haɗu da Nusaiba, ta gaishe shi, bai iya amsawa ba sai jinjina mata kai kawai ya fice.

Yana tafe yana auna kashedin ammi da kiran da wambai yayi masa, saboda shi a yanzu tension ɗin da yake ciki ya ishe shi, ba sai an ƙara masa da wani ba.

Nusaiba ta shiga ɗakin Ammi, ta tarar da ita zsune a gefen gado, ta yi shiru.

"Ammi" Nusai ta yi maganar kamar tana tsoron wani abu.

Ammi ta kalleta ta ce "Na'am ya aka yi?"

"Amma dai baki gaya wa takawa yadda kuka yi da wambai ba ko, kar ya hasala?"

Ammi ta girgiza kai ta ce "Ta yaya zan gaya masa, ni babban fatana idan ya je kiran da yake masa, Allah ya sa kar yayi masa irin cin mutuncin da yayi mini,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login