Showing 204001 words to 207000 words out of 224014 words

Chapter 69 - Kanwar Maza 1&2 Hausa Novel Complete

12 Dec 2024

1122

yi cikin shege, ana yi mata kallon ƴar iska, saboda ta zo da sabir, idan ban saka takawa ya aureta ba, shikenan an yi mata mummunan tambari, mutane ɗa idan ba na su bane ba, sun din ga janyo masa jafa'i kenan"

Nusaiba ta ce "Haka ne, Allah ya shirya, ya tabbatar da alkhairi" suka amsa da amin.

Baba uwani da take laɓe ta ji hirar ta su sama-sama, sannan bakomai ta ji ba, amma a abun da ta jin, ta ƙudurce za ta je ta sanar da Mummy.


Rumaisa mita a cikinta, kamar an yi mata gori, yau wuni ta yi tana cigaba da mitar abubuwan da ake yi mata a unguwar nan, mama tun tana yi mata nasiha tana cewa ta bar wa Allah, har ta yi mata banza ta ƙyaleta, Abdallah ya sakata a gaba yana cigaba da kunnata, tana mita. Bayan fitar Abdallah rumaisa ta shiga ɗakinsu, ta duba wurin da yake ajiye fensiransa na zane kasancewar sa architect.

Ta zauna ta nutsu sosai, ta hau zane-zane.

Mama ta ce "Uban me ki ke yi musu a ɗaki, ki ka shiga ki ka yi shiru?"

Rumaisa ta ce "Bakomai"

"To fito musu daga ɗaki, tun basu dawo sun tarar da ke ba"

"Mama zan fito ina zuwa"

Sai da ta gama abun da Allah ya nufeta da yi, sannan ta fito ta fice ba tare da sanin mama ba.

Maƙwabciyarsu ta zana, kuma zanen ya fita sosai, ta yi headline da munafukar unguwa, a ƙasa ta rubuta by Rumaisa Mahmud ƙanwar maza. Ta je ta liƙe a ƙofar gidan matar, ta nausa ta tafi gidansu Habiba, ba tare da mama ta san ta fita ba ma.


Ayshercool.

paid book ne, ₦500 via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143


*KANWAR MAZA*

*39*



*PAID BOOK NE, ₦500 VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143*




Jin shirun yayi yawa ya kuma sanyawa mama ta ƙwalawa rumaisa kira, amma har ta kira kusan sau uku shiru, ba ta amsa ba, mama ta kaste abun da take yi, ta fita domin duba me rumaisa take aikatawa ta ji shiru. Sai dai da ta fito tsakar gida babu rumaisa ba alamarta.
Mama ta leƙa ɗakin ƴan maza, amma babu rumaisa ƙarshe ma sai shiga Maman ta yi ta kwaso kwanukan ta, da suka kai ɗakin suka bar su, ta fito ta duba banɗaki da kitchen duk babu rumaisa, tsayawa ta yi tana tunanin ina rumaisan ta tafi ba ta gaya mata ba?.

Tana cikin jimamin in da rumaisa ta tafi babu izininta, shamsiyya maƙwabciyarsu ta yi sallama, ita da wata mata.
Mama ta amsa musu cikin sakin fuska, ba tare da nuna mata ta san ta yi wa ƴarta ƙage ba.

"Maman rumaisa ni ba zama zan yi ba, ki shiga tsakanina da yarinyar nan, kalli abun da ta yi mini jiya a fuskata, da ɓarnar da ta yi mini a cikin gida, maigidana ya kawo ƙararta, ƙarshe ba wani mataki da kuka ɗauka, sai ma cin mutumci da ya biyo baya, yau kuma ta je ta yi zane ta liƙe mini a ƙofar gidana ya ƙi fita, wai munafukar unguwa, me na yi muku haka ne?"

Cikin dattaku mama ta ce "Dan Allah ki yi haƙuri, yaran zamani ne sai godiyar Allah, wallahi da kaina na yi niyyar shigowa na baki haƙuri, wallahi ban san ta yi ba, kin san dai ni ba zan goyi bayan ta yi wannan rashin kyautawar ba, ban san ta yi miki ba, dan Allah dan annabi ki yi haƙuri, bari ta shigo gidan, zan hukunta ta kuma zan sanya ta je ta cire, dan Allah ki yi haƙuri"

"Wallahi banda ina jin nauyinki, Allah da sai na kama rumaisa na yi mata shegen duka".

Mama ta ce "Ashsha, ba za ayi haka ba, ai ke ma ƴarki ce, yanzu kina taɓata komai zai ɓaci, yayyenta ba sa ganin laifinta, amma dai ina baki haƙuri, da kaina zan hukunta ta, kuma zan aikota ta baki haƙuri".

Haka Jamila ta yi ta farfaɗar maganganu, mama tana bata haƙuri, da alwashin hukunta rumaisa, bayan tafiyarta mama ta dafe kai, haryanzu rumaisa babu alamar hankali a tare da ita, tuno damben da suka sha da ƴar ajinsu ta yi, abu har wurin ƴan sanda saboda wannan shegen zane-zanen da take yi, shi kansa Abdallah dan ba yadda za ta yi da shi ne, abun da yake karanta kenan, ga rumaisa na neman gadarsa, in dai zane-zanen banza da na wofi ne, a litattafan makarantar ta ma yi take.

Mama ta rasa mai ma yakamata ta yi, ba ta san ta ina zata fara neman rumaisa ba.

Rumaisa kuwa gidansu habiba ta tafi, suka shantake suna ta hira, ta bawa habiba labarin abun da ta yi wa maƙwabciyarsu.
Habiba ta ce "Kin mini daidai, da nice ba zan iya ba, tsoro nake ji, kin ji yadda matar nan ta din ga yayata maganar nan a cikin unguwar nan, ummanmu ce ta fara taka mata burki ta ce ƙarya take yi, daga nan ta je ta gayawa mamanku"

Rumaisa ta ce "Hmm, ai sai ta gane ba ta da wayo kan ma bar unguwar nan, da ina mutunta ita da mijinta, amma tun da ta taɓo ni, za ta gane bata da wayo"

Cikin rashin fahimta habiba ta ce "Ki bar unguwar nan ki koma ina?"

Rumaisa ta ɗan yi jimm, sannan ta ce "Ke share kawai, na san zuwa yanzu wataƙila ta je ta kai ƙarata gidanmu"

"Me ki ka yi mata?"

Cikin ƙwarin gwiwa rumaisa ta ce "Zanata na yi, na rubuta munafukar unguwa, na liƙe mata a ƙofar gida, na san yau za a azabtar da ni a gida, amma ba zan koma yanzu ba"

Habiba ta ce "Wai ruma ba kya jin tsoro ke? Mama ba ta san kin zo nan ba?"

"Ba ta sani ba, idan aka kai ƙarata ina gidan, a gabanta mama zata bani rashin gaskiya, duk da abun da ta yi mini, zuwa yanzu kuwa na san ta tafi, in koma gida a haɗani da mai sunan baba, ya bani gwale-gwale"

Dariya habiba ta yi ta ce "Wato ke har ma kin san me za ayi miki, ina yaya Aliyu?"

Rumaisa ta yi mata kallon ƙasan ido ta ce "Yana makaranta, in ce kina nemansa ne?"

Habiba ta waro ido ta ce "Ke a'a, kawai dai tambayarsa na yi"

"Meyasa duk cikin yayyena shi ki ka sani?"

Habiba ta ce "Bakomai, ya na da kirki ne"

Rumaisa kawai ta yi dariya, tana lissafa yadda zata wanye da mama idan ta je gida.

Mama kuwa sai kallon agogo take yi, tana lissafa, ina rumaisa ta tafi haka? Ta ƙi dawowa, zuciyarta ta bata saboda abun da ta aikata ne ya sanya ta fece.

Kasancewar azahar ta yi, kuma juma'a ce ya sanya ƴan samarin mama dawowa gida, domin shirin masallaci, kuma aka yi sa'a ana public holiday, rumaisa ba makaranta ta je ba.

Faɗan Abdallah mama ta jiyo, yana faɗin "Uban waye ya taɓa mini kayan zanena, bana son rashin mutunci, Huzaifa ban hanaku taɓa mini kaya ba?"
Huzaifa ya ce "Ni na iya amfani da wannan abubuwan naka ne? Sai dai ko Yasir"

Yasir ya tari numfashin Huzaifa ta hanyar cewa "Saboda ni ka raina ba, yaushe na zauna a gidan balle na taɓa masa kaya".

Mama ta fita tsakar gida ta ce "Ba aikin kowa bane, rumaisa ce ta taɓa maka, ita ta shiga ɗakin ta yi shiru, ita ce ba wani ba".

"Tana ina, sai ta ci ubanta yau sai na zaneta, har da gum ɗina ta buɗe ta bar mini a buɗe"

"Hmm, wannan yarinyar ai sai fatan shiriya, ina fatan Allah ya sanya auren nan ne mafi alkhairi, ko yau aka ce za ayi zance a ɗaura su tafi da ita"

Abdallah ya ce "Tana ina?"

Mama ta ce "Ina na sani, ta yi wata aika-aikar ta gudu, ban ma san ta fita ba".

Yasir ya ce "Kai wannan yarinya, Allah ya yi mata maganin abun da yake damunta yake sanyata rashin ji".

Rumaisa ba ta tashi tafiya gida ba, sai da unguwa ta yi tsit, duk an tafi masallaci, sannan ta nufo gida, cikin shirin karɓar kowane irin hukunci za a yanke mata.

Da sallama ta shiga gidan, ta yi sa'a mama tana salla, ta lallaɓa ta shiga ɗakin ta zauna, tana jiran mama ta idar, ta shirga mata ƙaryar da zata kare kanta.

Mama tana jin motsin rumaisa, amma ta shareta, ko da ta idar da sallar ma ta yi lazumi, ba ta tankawa rumaisa ba.

Cikin tsoro rumaisa ta ce "Mama" banza tayi da ita ta shige uwar ɗaki ta bar rumaisa.

Tun rumaisa tana ɗar-ɗar har ta ɗan saki jikinta, da ta ga mama ba ta da niyyar kulata.
Sai dai ba ta ankara ba, mama ta shammaceta, ta janyota ta din ga ɗirka mata dundu.

Ihu rumaisa take yi, tana neman agaji rabon da mama ta daketa har ta manta.

Tun daga waje Yaya Abubakar ya jiyo ihun rumaisa, a soro ya yasar da sallaya, ya shiga da gudu, ya tarar da mama ta samu mafici, tana jibgar rumaisa tana yi tana haɗawa da hannunta.

Ai da hanzari ya ƙwaci rumaisa yana faɗin mama lafiya.

"Rabu da ni, yau yarinyar nan ta kaini bango, rumaisa a rayuwarta ba zata bari na huta ba, daga wannan sai wancan, gidan ubanwa ki ka tafi?"

Cikin kuka rumaisa ta ce "Gidansu habiba"

"Gidansu habiba gidan ubanki ne? Wato kin san abun da ki ka aikata ko?, To fita ki je ki bata haƙuri, ki cire takardar da ki ka liƙe mata a ƙofar gida, tun kan na murɗe miki wuya ki mutu in huta, da ɗaukar maganar da ki ke yi, kullum nike nan cikin bayar da haƙuri da faɗa da mutane saboda ke?
Bari na kira babar adam ɗin a waya, idan sun shirya ko jibi su zo a ɗaura auren nan na huta na gaji" Rumaisa ta yi fici-fici da ido tana kuka.

"Ba zaki fice ki je ki bata haƙuri, ki cire abun da ki ka liƙa mata ba?" Ruma ta fita da sauri, tana jin haushin sake kai ƙararta da matar ta yi.

Ta je ta yi iya ƙoƙarin ta, wurin cire cardboard paper da ta yi zanen a jiki, amma gum ɗin da ta yi amfani da shi ya kama sosai, dan haka ta samo wata ƙusa, ta dinga durzawa takardar, ta haɗa da sabon fentin da aka yi wa ƙofar duk ta kankare abun ta, sannan ta shiga cikin gidan matar.

Ta tsaya daga soro ta yi sallama, matar ta amsa sannan ta fito, ta sakawa bakinta da goshinta shanshanbale, in da rumaisa ta fasa mata da dutse.

"Kin kai ƙarata, mama ta ce sai na zo na baki haƙuri, na cire takardar da na saka miki, na cire takarda, idan ki ka kuma kai ƙarata zan yi miki abun da baki zata ba, kuma wallahi ban yafe miki ba sharrin da ki ka yi mini, wuta balbalin bala'i, idan baki nemi yafiyata ba, sai kin ga abun da Allah zai yi miki, kayan da ki ke sayarwa ma sai an daina siya" tana gama maganar ta juya ta tafi.

Da sauri ta biyo bayan rumaisa, sai dai tana zuwa ta tarar da sabuwar ta'asar da rumaisa ta ƙyanƙyasa mata a ƙofar gida, ta kankare tsakiyar ƙofar da ƙusa, duk fentin ya fita ga sauran takardar ba ta gama fita ba, gaba ɗaya ta sauya fasalin ƙofar.

"Na shiga uku ni Jamila, wace irin masifa ce wannan, fentin ƙofar da bai fi sati da yi ba ki ka dirje?".

Rumaisa ta waiwayo ta kalleta ta ce "Idan baki gaji ba, yanzu ma ki je ki kai ƙarata, zaki sha mamakin abun da zan yi miki next"

Ta shige gida tana sunkuyar da kai, mama ta kalleta a fusace ta ce "Kin bata haƙurin ko kuwa?"

"Na bata" ta amsa tana sunkuyar da kai.

Aliyu ya kalli rumaisa ya ce "Allah ya shiryeki ruma, ke ko gajiya da ɗaukar magana ba kya yi, kullum ayi ta yi miki faɗa, daɗi yake yi miki ko?" Ta girgiza kai alamar a'a.

"Zo ki karɓi kuɗin nan ki sayo mini milo a kantin malam lawan, zan sha shayi bana son cin abinci" kallon yaya Aliyu ta yi, kamar tana hararsa ya ce "Ni ki ke yi wa wannan kallon, ko ba zaki ba?" Ta durƙusa ta ɗauki kuɗin, ya ce "Ki taho da manja kwalba ɗaya, na ga wanda muke da shi ya kusa ƙarewa".

Ita dai ba ta amsa masa ba, ta fice ko da ta fita a ƙofar gida ta hangi shamsiyya da mijinta, suna duba ƙofarsu da ta dirje, ba ta kula su ba ta tafi shagon.

Malam lawan mai kanti, yana ta yi mata wasa yana tsokanarta, amma ta share shi, ya auna mata manjanta, ta fito. Sai dai tana fitowa ta yi karo da wani tantirin ɗan daba da ya addabi unguwarsu, wanda har kisan kai yayi, amma aka sake shi.

Ya kalli rumaisa ya ce "Ke, karɓo mini sigari a cikin shagon nan"

Tsaki ta yi, zata wuce, ya sake daka mata tsawa ya ce "Ke, na ce ki karɓo mini sigari a cikin shagon nan"

"Na yi maka kama da ƴar iska, ni ce ma zan taɓa sigari saboda wulaƙanci, to ba zan karɓo ba" ware jajayen idanunsa ya yi a kan rumaisa, a hargitse malam lawan ya ce "Yi haƙuri bari na miƙo maka".

Cikin muryar mashaya, ɗan daban da ake cewa ɗan kada ya ce "Ni ki ke gayawa haka?".

Fitowa ta yi zata wuce shi, ta tafi, amma ya sanya ƙafarsa ya kwashe na rumaisa, a take kuwa ta faɗi ƙasa, manjan hannunta ya fashe, ta datse goshi.

Idan da abun da rumaisa ta tsana, bai wuce ganin jini a jikinta ba, jiki na rawa ta tashi ta kalleshi, ya kalleta ya ce "Sai na tsarge hanjinki da wuƙa, na kashe banza ni zaki nemi ki zaga wata jagwal da ke"

Cikin hanzari malam lawan da sauran mutane suka fara lallaɓa ɗan kada suna bashi haƙuri, rumaisa ta shiga cikin shagon, ta dumbuzo ƙwan da ke kan teburi, ta fito ta shiga jifan ɗan kada da shi.

Rikicewa malam lawan yayi, dan yanzu aka sauke ƙwan ko lissafawa ba ayi ba, ji ta yi zuciyarta na tafasa, ta juya da gudu ta tafi gida.

Aliyu na ganinta ya ƙare mata kallo ya ce "Meye haka?" Cikin kuka ta kwashe komai ta gaya masa, nan da nan ransa ya ɓaci ya ce "Mu je" mama na banɗaki tana gyaran murya, amma Aliyu ya ja rumaisa suka yi waje.

A ƙofar shagon suka tarar da ɗan kada, har ya karɓi sigarinsa ya fara sha, malam lawan kuma yana ta masifa, yana sai ya je gidansu rumaisa an biya shi, shi kansa ɗan kada yayi alwashin sai ya kashe rumaisa, saboda wulaƙancin da ta yi masa,ta din ga jifansa da ƙwai.

Idan da abun da samarin gidan maman suka tsana, bai wuce taɓa Wannan tilon yarinyar ba, dan haka a zafafe Aliyu ya ƙarasa, yana zuwa ba tambayar ba'asi ya ci kwalar ɗan kada, ya shiga kifa masa mari.

Kokawa ta kacame, ga ɗan kada a buge, dan haka ya kasa wani abun arziki, Aliyu ya din ga haɗa masa naushi.

Da ƙyar mutane suka shiga tsakani, ana rirriƙe ɗan kada yana rantsuwa sai ya kashe Aliyu.

Mama kuwa a gigice ta fito daga banɗaki, jin wanda rumaisa ta tsokano, dan babu wanda bai san yadda ya addabi unguwarsu ba.
Mama ta kira mai sunan baba a waya, ta ce masa duk abun da yake ya bari ya tafi shagon malam lawan, Aliyu ya fita ba ta san mai zai aikata ba.

Aliyu kuwa ya kalli ɗan kada ya ce "Jinina da na zuriyar gidanmu ya fi ƙarfin mutum irinka,  duk wani hauka da iskanci da kake ji da shi a unguwar nan ƙyaleka aka yi, ƙanwata ta fi ƙarfin wawan mutum irinka su cutar da ita"

Malam lawan ya ce "Wai Meye haka ne Aliyu, ina nan aka sace ƙanwar ta ku me ku ka yi, sai yanzu zaku haddasa mana masifa a cikin unguwa"

"Wallahi malam lawan, duk shekarun da muka yi tare a unguwar nan, idan ka taɓa rumaisa sai na tuɓe na yi maka bugun sakwara, saceta kuma da aka yi wannan ƙaddararta ce, ba yadda muka iya"

Rumaisa ta riƙe hannun Aliyu ta ce "Yaya mu tafi gida"

Da ƙyar rumaisa ta riƙe hannunsa, suka juya suka fara tafiya, sai dai ana sakin mai kada, ya zare wuƙa ya nufi Aliyu da ita gadan-gadan yana ihu.

Ihu rumaisa ta saka ganin wuƙa tsirarata, wuƙa ba ta wasa ba an nufo yaya Aliyunta da ita, wanda ba da tabbacin ita aka nufo ko shi. Aliyu ya hankaɗeta, ya kuma riƙe mai kada suka hau kokawa ga wuƙa tsirarta.

Aliyu ya danne mai kada a ƙasa, ya ɗau wuƙar ya ce sai ya yankashi da ita a wurin.

Nan aka din ga kokowa da Aliyu, aka kasa ƙwace wuƙa.

Rumaisa ta ce "Yaya Aliyu kar ka yi kisan kai, amma dai ka yi masa dukan tsiya".

Cikin takunsa na isa da taƙama, ya din ga ture dandazon mutane, ya ƙarasa in da Aliyu yake kan mai kada ana fama da shi, ya riƙe hannun Aliyu mai wuƙar ya murɗa, ya jefar da wuƙar, sannan ya ɗago shi daga kan mai kada ya tsayar da shi a kan ƙafafuwan sa ya Kalleshi ya ce "Meya haka? Shaye-shayen kai ma ka fara ne?" Ya kalli rumaisa ya ce "Duk saboda ke ko? Sai ku wuce mu tafi ai".

Daga kwance mai kada ya ce "Na rantse da girman Allah, idan har ina yawo kana yawo a unguwar nan, sai na kasheka na kashe matsiyaciyar yarinyar nan, na ga uban waye gatanku"

Aliyu ya sake tunzura, jijiyoyin kansa suka kumbura, mai sunan baba ya kalli mai kada ya ce "Idan kana zubar da jini a unguwar nan kai da yaranka, ana tsoronku, kar ka ratso ta gidanmu, wallahi duk wanda ka zubarwa da jini in dai ɗan gidanmu ne, kaima sai na zubar da naka, ka kiyaye"
Ya riƙe rigar Aliyu, hannu ɗaya ya tankaɗa ƙeyar rumaisa zuwa gida.

Mutane wasu har da shewa, abun ya burgesu, kaf unguwar nan babu gidan da suke da haɗin kai da nunawa juna soyayya kamar gidansu rumaisa.

A gigice mama ta tashi da suka shigo, ta ga jikin Aliyu duk ƙasa, rumaisa kuma da fasashshen goshi, duk da ba ta zubar da jini da yawa ba.

"Mai sunan baba, maiyafaru?"

"Kar ki damu, ba abun da ya faru"

Mama ta riƙe Aliyu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login