Showing 213001 words to 216000 words out of 224014 words

Chapter 72 - Kanwar Maza 1&2 Hausa Novel Complete

12 Dec 2024

1110

sosai, abun yayi masa ciwo, sai dai ya bar abun a ransa, wani irin takaici ya cigaba da ci masa zuciya, a rayuwarsa ya tsani raini da wulaƙanci, amma Mahmud ya ci masa mutunci haka.

Aliyu ne ya faɗo masa, dan haka ya kira shi, domin jin idan babu wata matsala.

Aliyu sai da ya ɗan ji kunya, ya ce "Tuba nake babban yaya, ni yakamata na kiraka, ya ka je gida?"

Adam ya ce "Lafiya ƙalau, ya mama?"

"Tana lafiya, ta ce za ta yi maka godiya, amma muka tarar ka tafi"

"Ahh haba, ba wannan tsakaninmu, ina fatan babu wata matsala, dan irin yaran nan, ka san suna da nasu yaran, duk da an kama su, kar su cutar da ku, ko kai ko ita da yayi iƙirarin zai kashe".

"Aliyu ya ce babu wani abu, duk muna Lafiya, mutuniyar ce dai ta tatara kayanta wai barin gidan za ta yi, ba a ƙaunarta".

Adam ya ce "What? Ku saka ido a kan ta sosai fa, na fuskanci za ta iya aikata duk abun da ta ce, kar ku je ta yi wani wurin"

Aliyu ya yi murmushi ya ce "Babu in da zata je, mai sunan baba ya tsawatar mata".

Adam ya ce "To Allah ya tsare, ka gaida mutanen gidan"

"Za su ji in sha Allah, a gaishe mana da mai sunan babanmu"

"Zai ji in sha Allah".

Ganin yadda rumaisa ta addabi kanta, ya sanya mama sakkowa daga fushin da take yi da ita, ta yi ta mata nasiha, duk da ta san nasihar tata ba ratsa rumaisa take yi ba, dan za ta iya gama nasihar tana fita tsakar gida, ta ɗora daga in da ta tsaya.
Bayan ta gama yi mata nasihar, ta dubeta ta ce "Ni kuwa rumaisa, ya batun al'ada ne? Tun da ki ka dawo baki yi ba fa, ko kin yi a can hannun ƴan bindigar?"

Rumaisa ta ce "Wace al'adar?"

"Jinin haila mana"

Rumaisa ta ce "Taɓ, ni fa tun da na yi sau ɗaya, na fitsarin jinin nan, ban kuma yi ba, Allah ya yaye mini, shi ma dan wannan mugun mutumin ya watsa mini ruwan kwata ne na yi" mama ta ɗan yi jimm tana kallonta, dama hakan ta kan faru ga macen da ba ta saba yin al'ada ba, amma ta ƙudirce a ranta za ta kai rumaisa asibiti.

Adam yana office ɗin sa, yana tsaye a jikin window yana kallon titi, hannunsa riƙe da kofin shayi, yana ta tunani daban-daban, ƙarar buɗe ƙofar office ɗin ce ta dawo da shi hayyacinsa, ya waiwaya.

Jamil ya gani kamar an koro shi, Adam ya ce "Ya dai? Ya na ganka a haka kamar ba lafiya?"

"Adam da gaske aure zaka yi?"

Adam ya ajiye kofin hannunsa ya ce "In ji wa?"

"Mai girma turaki ne ya sanar da ni"

"Ba yana umara ba?"

"Magana mu ka yi da shi ta video call"

Ya juyo ya fuskanci jamil sosai ya ce "Haka ne, Turaki ba zai yi maka ƙarya ba"

"Amma Adam idan ka yi wa Samha haka ka yi mata adalci kuwa? Meyasa zaka auri wata ba samha ba, ko dan ba ƙanwarka ba ce ba ka san zafin so ba?"

Adam ya shafi sumar kansa ya ce "Ba soyayya nake dubawa ba, makomar ɗana nake dubawa, samar masa da jajirtacciyar uwar da za ta kula mini da shi"

"Kana tunanin akwai wanda zai so ɗanka, ya nuna masa kulawa sama da ita da suke uba ɗaya da Aisha"

"Ba za a rasa ba" ya bashi amsa cikin ko in kula.

Cikin fushi Jamil ya ce "Anya kuwa kana da imani Adam, duk wahala da son da yarinyar nan take yi maka, ba zaka duba ba".

"Jamil, maganar ammi zan ajiye na bi son zuciyata ne?"

"Kana nufin ammi ce ta zaɓi wadda za ka aura?" Abun da Jamil ya faɗa, ya sanya Adam sanin cewa turaki bakomai ya gaya masa ba dan haka ya ce "Ina nufin ammi ma ta yi amanna da Yarinyar"

"Kenan menene makomar Samha?"

Adam ya numfasa ya ce "Da zan iya, da na haɗa su su biyu, sai dai ba zan so gidana ya zama irin gidanmu ba, bana son damuwa, kuma na san dole zan cutar da ɗaya a cikinsu, Samha ƙanwata ce, muna da alaƙa ta jini da ita, zan iya karkata gareta, saboda kusancin alaƙarmu, ita kuma waccan ta yi mini abun da ko duniya zan ba ta ba zan biyata ba, zan iya karkata gareta dan girman halaccin abun da ta yi mini. Sai dai a duk su biyun babu wadda zan gazgata cewar ita zuciya ta ke so, abu ɗaya na sani" ya taka gaban Jamil yayi ƙasa da muryarsa ya ce "Bana son ɗana ya yi rayuwa irin wadda mahaifiyarsa ta yi, so nake ya rayu a matsayin sa na cikakken ɗa a gidan mahaifinsa, ka san abun da nake nufi".

Ayshercool.
08081012143


PAID BOOK NE, ₦500 VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143.



Cikin tsananin mamaki, Jamil ya kalli Adam ya ce "Me ka ke nufi?"

Adam ya dafa kafaɗar Jamil ya ce "Ba sai mun zurfafa ba, ka san abun da nake nufi, kai ɗan uwana ne Jamil, Samha ma ƙanwata ce, ba na son zumuncin mu ya samu matsala saboda wani dalili, a madadina dan Allah ka bawa Samha haƙuri, ina fatan Allah ya zaɓa mana abun da ya fi alkhairi daga ni har ita"

Daga haka Adam ya fice ya bar Jamil a tsaye da buɗaɗɗen baki.

Ammi kuwa waya suke yi da rumaisa, rumaisa tana ba ta labarin yadda takawa ya fito da Aliyu bayan rigimar da suka yi aka rufe shi, wanda shi Adam ɗin sam bai gaya mata ba.
Ammi ta jinjina al'amarin, tare da yi mata Allah ya kyauta.
Gaba ɗaya rumaisa ba ta san wani abu wai kunyar suruka ba, mama na ta ƙifta mata ido, amma sosai take ta yi wa ammi surutu.

Ammi ta numfasa ta ce "Rumaisa na bayar da saƙo a kawo miki ki ka ƙi karɓa ko?"

Rumaisa ta ce "Laa ashe da gaske yake, na zata shi ya bani, na ce ba zan karɓa ba, bana son wataran yayi mini gori"

"Ahh haba dai, ba zai taɓa yi miki gori ba, duk abun da ya baki ki karɓa ba zai cutar da ke ba, sannan ki din ga yi muku Addu'a a kan lamarin auren nan na ku, turaki na daf da dawowa".

Ita gaba ɗaya ma ta manta da maganar auren, sai yanzu da ammin ta tuna mata.

"To, ammi kin san wani abu?"

Ammi ta ce "Sai kin faɗa"

"Kewar sabir nake yi sosai, daurewa nake yi dan kar na din ga takura muku"

Ammi ta ce "Subhanallah, rumaisa zan ci gidanku fa, ni akwai wani abu mai kama da takura tsakanina da ke, ba ni na ce duk lokacin da ki ke so ki gaya mini a kawo shi ba? Za'a kawo miki shi ranar da babu makaranta, na san shi ma yana kewarki".

Rumaisa ta yi murmushi ta ce "To ammi, na gode sosai ki gaida kowa da kowa"

"Yauwwa ko ke fa, za su ji in sha Allah" Ammi ta katse wayar tana murmushi.

A can falo kuwa, Iman ce take bawa sabir abinci, an fara gwada masa abu mai ruwa-ruwa.

Baba uwani na ta tsokanar iman "Ohh tsakanin uwa da ɗa sai Allah, tsakanin Sabir da iman sai Allah"

Iman ta yi murmushi ta ce "Tsakanin kaka da jikarta ma sai Allah ba"

Baba uwani ta ce "Uhumm kakar da yake yi wa ƙyuya, daga ke sai ammi sai babansa, sai kuma Nusaiba idan ya ga dama, yaro ba ya yadda da kowa"

"Kar ki damu baba uwani, zai yadda da ke ne"

"Mhmm, ni kuwa Iman, ina yarinyar da aka ce ta tsinci yaron nan, Haryanzu tana nan kuwa?"

"Laa tana nan baba uwani, baki taɓa ganinta ba?"

"Oho, yo ni a ina zan ganta ma"

Iman ta ce "Kai haba, ta zazzo gidan nan fa sosai da sosai, ai duk ƙyuyar nan da yake yi, ba ya yi mata, dariya sosai ke ba kya ce shine ba".

Baba uwani cikin son bugun ciki da gulma, ta sake ƙasa da murya ta ce "Ni kuwa wai babba ce ko yarinya?"

"Gaskiya Yarinya ce sosai, dan duk mun girmeta"

"Ikon Allah, ƴar nan unguwar ce kuma? Na ji kin ce tana zuwa gidan nan, ai ni fa ban zaci ma ƴar nan garin ce ba".

"A'a ba unguwar nan take ba, zuwa take yi, amma kwana biyu ma ba ta zo ba".

"Ikon Allah, ni kuwa dan Allah duk ranar da Allah ya kawota ki nuna mini ita"

Iman ta yi murmushi ta ce "Maman sabir, to shikenan in sha Allah" Baba uwani ta yi gaba tana jin alamun nasara.

Tafiyar baba uwani babu jimawa, sai ga Jabir yayi sallama, cikin sauri Iman ta rufe kanta da hula, ta gyara zamanta, tare da mayar da hankalinta sosai a kan Sabir.

Murmushi Jabir yayi, ya ƙarasa kusa da ita ya zauna ya ce "Gashin ake yi mini rowar gani kuma?" Ta yi masa shiru ba ta ce komai ba.

"Talk mana iman, ko miskilanci ne?"

Ta yi masa shiru, ta cigaba da bawa Sabir abinci, Jabir ya miƙe hannu ya ɗauki Sabir, yana ƙure Iman da wani irin kallo, wani irin abu yana fuzgar zuciyarsa game da ita.
Wuyanta yake bi da kallo, ya haɗiye wani irin yawu, ya zaunar da sabir a jikinsa, amma Sabir ya ce bai san zance ba ya sanya kuka.

"Ka bani shi abinci nake ba shi".

"Ba zan baki ba, sai kin kalleni kin amsa mini"

Ammi ce ta fito falon, cikin fara'a ta ce "Jabir, kwana biyu ina ka ɓuya ne?"

Yayi murmushi ya ce "Tuba nake ammi, ayyuka ne suka yi mini yawa sosai"

Ammi ta kalli Sabir ta ce "Rigimamme, kai ba ka gane iyayenka ne, kowa ma ba zai ɗauke ka ba?"

Iman ta tashi daga kan kujerar, ta karɓi Sabir ta bar falon, yadda ya ɗan shagala yana kallon iman ne ya sanya ammi jinjina kai a ranta ta ce "Yaushe wannan lamarin kuma ya kunno kai? Akwai ƙura idan Hajiya Lubabatu ta sani, amma da zan so faruwar hakan jabir ba shi da matsala'

"To ya gidan ya hajiyar taka?"

"Tana nan ƙalau Ammi, na je na duba Mahmud ne, na ji abun da ya faru sam bai yi mini daɗi ba ammi"

Ammi ta nemi wuri ta zauna ta ce "Kai dai bari jabir, lamarin ɗan uwan nan na ku sai addu'a kawai, dan ku din ga yi masa faɗa, yanzu a garin wannan zafin zuciyar ta sa da ya yi masa illla ko ha salwantar masa da rayuwa fa?"

"Kai, ai takawa sai haƙuri, iya masa sai Allan da ya yi shi, amma iya ƙoƙari muna gaya masa gaskiya, sai dai ayi ta yi masa addu'a, Allah ya yaye masa wannan azababbiyar zuciyar"

"To Amin, Allah ya iya mana"

Nan suka cigaba da hira da shi da ammi, sai dai hankalinsa ya fi karkata ga yadda yake jin iman a ransa.

***
Cike da zullumi Samha ke cin abincin da yake gabanta, ba dan yana yi mata daɗi ba, sai domin zullumin abun da Jamil zai zo ya gaya mata, tun da ya gaya mata sun yi magana da turaki adam zai yi aure ta rasa nutsuwarta, so take ya zo ya gaya mata idan har hakan da gaske ne.

"Wai Samha ba zaki kwantar da hankalinki, ki nutsu ki ci abincin nan ba, sai jagwalgwala shi ki ke yi?"

Samha ta ce "Mama yaya jamil nake jira, hankalina ba zai kwanta ba sai na ji abun da nake son ji".

Ƙanwar Samha, wadda daga ita sai ita mai suna Zainab ta ce "Ni wallahi Samha mamaki ki ke bani, wallahi babu yadda za a yi namiji yayi mini abun da Adam yayi mini na sake kallonsa, ke kam kamar mara zuciya, shiyasa na koma zaman hostel ma na bar miki gidan, yadda ki ke zubar da classic ɗin ki a kan gayen nan yana bani haushi, kamar wani ɗan gold"

"Enough zainab, kar ki sake saka mini baki a maganata, idan ba so ki ke na yi miki rashin mutunci ba".

Mama ta ce "Ya isa haka, ni bana son faɗa, daga dawowarki".

"Mama kin san dai babu yadda za a yi ina ganin gaskiya in ƙi faɗa, Allah ya taimaki soyayyar wahala" ta ƙarasa maganar tana tashi ta bar dining ɗin.

Samha gaba ɗaya ba ta yanayi na yin faɗa, dan haka ba ta tankawa zainba ba ta shareta.

Jamil ne yayi sallama, mama ta amsa masa, Samha kuwa kasa amsa masan ta yi sai bin sa da ido da ta yi.

Ya nemi wuri ya zauna a ɗaya daga cikin jerin kujerun falon.

Samha ta taso cikin sauri, ta ce "Yaya Jamil ya ake ciki ne? Tun ɗazu nake jiranka"

Yayi shiru bai ce mata komai ba, "Yaya magana nake fa"

Ba tare da ya kalleta ba, ya ce "Samha ki na ji na?"

"Eh ina jin ka"

Ya taso ya zauna sosai ya ce "Samha, ina son ki saurareni da kyau, ki yi haƙuri ki cire Adam a ranki, a wannan karon ma ba zai aureki ba, domin kuwa ya tabattar mini da cewa mahaifiyarsa ta zaɓa masa wata matar, kuma turaki na dawowa za a kai masa kuɗin aure"

Ras! Gaban Samha ya faɗi, ta dafe ƙirjinta ta ce "What, again ta sama mata? Iman ko? Iman ce na sani, wai dan Allah me na yi wa matar nan ta tsaneni haka? A wancan karon ma ita ta yi uwa da makarɓiya ban auri Adam ba, a wannan karon ma ta kuma yi mini, na san ba wadda za ta zaɓa masa sai Iman"

Mama ta ce "To, ai a wannan karon sai ki kwantar da hankalinki, tun da an kuma kwatawa, sun nuna muraran ba sa ƙaunarki, sai ki ƙyale mata ɗanta ko?"

Samha ba ta iya cewa komai ba kawai ta tafi ɗakint, tamkar wadda take shirin zarewa, kaiwa ta din ga yi tana komowa a ɗakin, cikin zafin rai ta furta "Giwa me na yi miki, ki ke ƙyamar haɗa zuriya da ni ne? To wallahi a wannan karon ba zan yadda ba, ko ni ko ke ko mu rasa Adam daga ni har ke, har wadda zaki aura masan" ta yi maganar tana zubewa a kan gadonta cikin ƙunar rai.

***
Dukan teburin gabansa yayi, tare da tura kujerar da yake kai baya, ya ce "Aikin banza kawai, wai shi adam ɗin wanene da ganin ƙarshensa ya gagara, duk wannan abubuwan da aka yi a kansa, na gidajen jaridu da social media, yayi burus ya ƙi cewa uffan, sai ma wasu da yake turowa suna kare shi, wannan wane irin abu ne haka, ta ina kuma ya rage a ɓullo masa?"

Usman wakili yayi murmushi ya ce "Yaro man kaza, kai fa ka ce da na sakar maka ragamar komai, zaka iya komai ka san ta yadda zaka ɓullowa lamarin"

Khalifa ya ce "Haka ne Daddy, na yi duk iya yi na, ka sani na zaci yadda maganganun nan suka yamutsa hazo za su gigita shi, amma ya mayar da mutane mahaukata wato mu je ma mu yi ta yi kenan"

Senator ya yi murmushi ya ce "Na jinjinawa ƙoƙarin ka Khalifa, ban taɓa zaton zaka iya wannan ƙoƙarin ba ma, ka bani mamaki sosai kuma na yabawa ƙoƙarin ka, labarin da yake zuwar mini, hankalin yaron nan ba ya kanmu yanzu, kuma waɗanda suke jagorantar aikin tare da su, na saye wasu daga cikinsu, sannan kuma dama shi yake jagorantar aikin, kuma hamkalinsa ba ya kan aikin yanzu, na yi magana da shugaban kwamitin da shugaban ƙasa ya kafa, mun gama magana ba wani abu zasu wanke ni"

"Amma daddy kana ganin hakan ya wadatar, kar fa ya kuma ɓallo mana ruwa".

"Ai ba haka zan bar shi ba, ba ka da wata damuwa, na san abun da nake yi"

Khalifa yayi murmushi ya ce "To shikenan daddy"

***
Adam yana zaune yana aikinsa a office ɗin sa, ya ɗau wayarsa ya kira Bashir.
Suka gaisa Adam ya ce "Ka je ka maƙale ka ƙi dawowa, akwai update ne?"

Bashir ya ce "Babu wani update, sai dai na haɗu da barrister Sa'ad, ya ce akwai yiwuwar kwamitin da shugaban ƙasa ya kafa a kan senator Usman wakili ba zai yi wani tasiri ba"

Adam ya yi ajiyar zuciya ya ce "Na sani, dama ban ji a raina za su yi wani abun kirki ba, amma babu damuwa, zuwa next week ko upper in sha Allah zan shiga Abuja, ina son zuwa EFCC".

Bashir ya ce "Meyasa ba zaka shigo next week ba?"

"Wallahi ammi ce ta sakoni a gaba da wani batu, yanzu da na ce zan yi tafiyar nan, za ta ce ban ɗau abun da muhimmanci ba"

"Eh kuma haka ne, to shikenan Allah ya kaimu upper week ɗin, ni ranar sunda in sha Allah zan shigo kano, dama da zaka zo next week ɗin ne sai na jiraka, duk yadda ake ciki dai za mu yi waya"

"To shikenan Bashir, Allah ya yi mana jagora "

"Amin ya rabb, a tashi lafiya".

Ya ajiye wayar kenan, Jabir yayi sallama a office ɗin Adam, Adam ya kalleshi ya ce "Me ka ke yi a nan lokacin aiki?"

Jabir ya harare shi ya ce "Ban sani ba, sai avoiding ɗina kake, ba na samunka a gida, gidanka ma baka nan, na ce bari na zo na ritsaka a nan"

"Amma dai ka san lokacin aiki ne yanzu ko?"

Jabir ya ce "Ai lokacin salla ne kawai ba zan datseka ba, kuma sai ka saurareni, ai ka san abun da ka yi ba ka kyauta ba, dole ka yi ta gudun haɗuwarmu"

Adam yayi masa shiru, ya cigaba da aikinsa.

"Adam, ka san yanzu kaf idon duniya a kan kan ka yake, amma na lura kai ba ka damuwa da hakan, baka gudun janyo wa kan ka magana, yanzu dan Allah da wani mummunan abu ya faru da Mahmud saboda zuciyarka me zaka ce? Yakamata ka sassauta wa zuciyarka wannan ƙiyayyar da ka ke yi masa, ko kana so ko ba ka so ɗan uwanka ne shi"

Adam ya yi masa shiru, wanda wannan shirun shine halayarsa da ta fi ɓatawa makusantansa rai.

"Ko ka kulani, ko kar ka kulani, na san dai kai ba kurma bane ba, kuma ka na jina, jibi in Allah ya kaimu zan je duba galadima" sai a yanzu Adam ya ɗago ya kalli Jabir ya ce "Ubangiji Allah ya tsare hanya, ka ce ina gaishe shi" Jabir ya girgiza kai ya tashi ya fice, dan halin Adam sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login