Showing 87001 words to 90000 words out of 224014 words

Chapter 30 - Kanwar Maza 1&2 Hausa Novel Complete

12 Dec 2024

1567

ce "Wallahi wasu fulani ne suka kafa sansani a wurin, cikin dare aka kawo hari, aka ƙona musu shanunsu, suka ce manoma ne suka yi musu ake ta rigima, da ƙyar abin ya lafa"

"Kaii aka ƙona musu shanunsu, kuma da gaske manoman ne suka yi musu?"

Lawisa ta kai bakinta kunnen Ruma ta ce "Ke 'yan ta'adda ne fa suka yi musu, amma aka ce faɗan fulani da manoma ne, amma kar ki ɗaga hankalinki fa, mu nan haka lafiya lau muke zaune, an fi tashin hankalin a wuraren su Baba habu".

Ruma ta yi ajiyar zuciya ta ce "To kuma ba a gayawa 'yan sanda ba?"

Lawisa ta ƙwalo ido ta ce "'yan sanda, a ina zamu ga 'yan sandan ko sun zo me zasu yi, wataran dai sojoji na zuwa ayi ta harbe-harbe abin tsoro"

"Zo mu je wurin, in ga wurin sosai da sosai "

"Ke, Aikuwa tsaf fulanin nan zasu illata mu, yadda suke a ƙule zo mu tafi gida, na cewa Gwaggo ba zamu daɗe ba"

"Ke ki tafi, ni ba yanzu zan taho ba".

"To ai baki san hanya ba"

Ruma ta ce "Idan na ɓata na tambayi hanyar, ni wurin can nake son zuwa " tsoro ne ya kuma kama Lawisa ta cewa ruma "Ki zo yanzu mu koma gida, akwai hanya mai sauƙi da zan bi da ke muje wurin ".

Ruma ta ɗan rausayar da kai ta ce "Ina fatan ba ƙarya ki ke yi mini ba, ina son in ɗauki hotunan wurin in ɗau komai, yadda zan ji daɗin bayar da labari, kuma idan na bayar a yadda tunda ina da hoto".

Lawisa ta yi murmushi ta ce"Haka ne, karki damu" ta lallaɓa ruma suka koma gida.

Sai dai a washegari ruma ta faki idon mutanen gidan ta fice, kai tsaye wurin da aka yi wa fulanin nan ƙone-ƙone ta je. Sai dai tafiyar da nisa sosai, wurin shiru ba kowa sai ragowar abubuwan da aka ƙona, da tsirarun bukkoki a can gaba kaɗan, wurin kamar an yi wata annoba.

"Ke wace wannan me ki ke yi a wurin nan?" A hankali ta waiwaya taga wani dattijo a tsaye s bayanta, hannunsa riƙe jallon ruwa.

"Sannu baba" ya amsa da yauwwa.

Yana cigaba da ƙarewa ruma kallo.

"Baba gidan 'yan uwanmu mu ka zo, na hau wani dutse na hango nan shine na ce bari na zo na gani, Allah ya mayar da alkhairi amma kun gayawa 'yan sanda abin da ya faru?"

Kallon ruma yake, yadda take magana fiye da shekarunta.

Yayi ajiyar zuciya ya ce "Gidan wa ki ka zo a garin nan?"

"Gidan dagaci ne, ɗan uwan babanmu ne" ya jinjina mata kai ya ce "To mun gode da jajen da ki ka yi mana, amma maza ki tafi kar sauran mutanen rigar nan su ganki".

"To in sun ganni mai zai faru me na yi musu?"

"Kasheki za su yi, dan haka muje na raka ki hanya" babu musu ya saka ruma a gaba har zuwa cikin gari, suna tafe suna hira ruma tana addaba masa da tambayoyinta da ba sa ƙarewa"

A hanya suka yi sallama, ya koma ita kuma ta ƙarasa gida.

Gwaggo duk ta tashi hankalinta rashin ganin ruma, ita kuwa ko a jikinta ta ce kallon gari ta fita yi.

Sai dai a tattaunawar ta da dattijon nan ya gaya mata wasu abubuwa da suka sake ɗaure tunaninta.

****
Hajiya Lubabatu ce ta tsaya a tsakiyar ɗakinta, tana kallon hoton Galadima mai ci a yanzu, wands ya kasance mijinta da yake can ƙasar Germany yana jinya, ta ɗan lanƙwasa yatsan hannunta ɗaya sannan ta furta "Ka yi haƙuri ranka ya daɗe, bani da isasshen lokacin da zan cigaba da ɓatawa a kan ka, goben ɗana ita ce a gabana yanzu " ta yi maganar tamkar na cikin hoton yana jinta.


Khalifa ne zaune a kan kujerar da take kallon wadda mahaifinsa yake, mahaifinsa sai murmushi yake sannan ya nisa ya ce "Ina jinka Khalifa".

"Yauwwa daddy, kamar yadda nayi maka bayani, na tsara komai kuma ina da yaƙinin komai zai tafi dai-dai da yardar Allah".

"Haka ne, banƙi ta taka ba, na kuma yabawa ƙoƙarin da kake yi, amma gani nake komai zamu yi wa yaron nan ba zamu huce ba, yanzu haka bayanai sun zo mini yana garin Abuja, sai dai ban san wurin wa yaje ba, idan har ya cigaba da abin nan EFCC zata bincike ni, kuma daga haka ya ɓata siyasata, ya ci mutuncina kuma ya ɓata gobenka".

Khalifa ya gyara zama ya ce "Daddy, ai shiyasa nake ta ƙoƙarin aikin nan ya tabatta, ta yadda zan kau da hankalinsa a kan komai, ya tattarashi a wuri ɗaya, ka harda dani, abin nan zai yiwu daddy, kuma akwai nasara a ciki".

Senator wakili ya yi murmushi ya ce "To shikenan, ina saurarenka, sannan duk abin da kake buƙata, i will make sure that I provide it".

"To Shikenan Daddy, godiya nake "

Yayi murmushi tare da jinjina masa.

***
Kwanakin su ruma uku, ta saki jikinta, duk da kullum sai sun yi waya da mama, yawo kuwa kamar ta ci ƙafar kare, har gona suke zuwa ita da Lawisa, har ta saba da sirikan gwaggo da yaran maƙwabta.
Sai dai gona ɗaya aka samu aka sayar, a gonakin baban nasu, kuma shima dubu ɗari bakwai kawai aka samu, saboda yanayin in da gonar take babu tsaro sosai.
Ana i gobe zasu dawo kano, Gwaggo ta shirya ruma, ta haɗata da lawisa lawalli ya kai su can wani ƙauye, gidan wani ƙanin mahaifinsu, wai su gaishe su.
Aliyu sai mita yake yana tambarat gwaggo yaushe su ruma za su dawo, saboda da sassafe yake son su kama hanya, gwaggo ta ce kar ya damu, gobe da safe zasu dawo.

Har washegari da safe su ruma ba su dawo ba, Aliyu ya ce "Gwaggo, wai haryanzu su ruma ba zasu dawo ba, tafiya fa zamu yi, bana son rana tayi mana".

Gwaggo ta ce "Gadanga, sai dai kayi tafiyarka kai kaɗai, ina sane na tura ruma can, sai za a koma makaranta zan dawo da ita da kaina, yanayi ya nuna mini babu isasshen tsari a jikinta, kuma akwai buƙatar ta zaga ta san dangin mahaifinta suma su santa"

Aliyu ya ce "Amma gwaggo ba mu yi haka da mama ba, dan Allah kar ki yi mini haka".

Gwaggo ta ce "Mhmm, sai kuma ka yi, na gama magana"

Saroro Aliyu ya yi ya ma rasa mai zaice, ya ciro wayarsa ya kira mama a waya.

Yana kira mama ta ɗaga ta yi sallama.

"Mama, gwaggo fa ta tura ruma wani ƙauye, wai ba zamu taho tare ba sai an koma makaranta zata da wo da ita".

Gwaggo ta ɗan ɗaga murya ta ce"Eh, ni na ce ba zata dawo yanzu ba, sai na gama nema mata tsarin jiki, sannan kuma ta san dangin mahaifinta, tunda ba zuwa take ba"

Mama tayi ajiyar zuciya ta ce "Aliyu ka taho kawai, idan ka tsaya zai zama abin magana, ƙyaleta taho"

"Amma mama...

"Kar ka ce komai, in dai ruma ce, da kansu za su tattaro su dawo da ita, ka taho ka barsu".



Ayshercool.


*Paid book ne, 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143, wanda suke ba a Nigeria ba kuma, za su iya saya a arewabooks*






Abin da gwaggo ta yi ba ƙaramin ɓatawa Aliyu rai yayi ba, da ya san haka ne da ba zai taɓa bari ta saka a kai ruma ko ina ba, daga zuwa ziyara kawai ta riƙe 'ya wai sai wani lokaci.

Ya sake duban gwaggo ya ce "Gwaggo, ruma fa ba zata yarda ta zauna a garin nan ba, rigima za ta yi miki idan ta dawo ta tarar na tafi na barta".

Gwaggo ta ce "Babu komai, na san yadda zan shawo kan kayata, amma a yanzu dai ba in da zata".

Takaici ya ishi Aliyu, ya bi gwaggo da kallo.

"Gadanga ko dukana zaka yi ne? Na gama yanke hukunci, idan kuma kaima zaka zauna ne ni haka nake so, sai mu zauna idan lokacin yayi sai ku tafi duka".

Tabbas ba dan gobe yana da test mai muhimmanci a makaranta ba zama zai yi, ya saka lawalli a gaba sai ya kai shi ya ɗauko ruma, amma ba yadda iya ya ɗauki jakarsa ya fice.

****
Har Adam yayi kwanakinsa uku a birnin tarayya, bai iya aikata komai ba, saboda da ya fita da niyyar zuwa wani wuri, sai jiki ya hau rawa kai ya hau ciwo, ga ruma da ta addabawa rayuwarsa ya kasa mantawa da ita, komai yake yi sai ya din ga ganinta.
Bayan ya cika kwanaki huɗu, ya kira Ammi yayi mata ƙaryar bai gama abin da yake yi bane, sai dai tattaunawar haka aka yi ta babu shi, duk da halartarsa tattaunawar na da matuƙar muhimmanci.
A kwana na biyar ya kira direbansa a waya, ya ce ya zo da mota ya same shi a hotel ɗin da yake.
Ƙarfe biyu direban ya sameshi, sai dai a wannan karon cikin ikon Allah tun da ya fito sau ɗaya kan ya sara, jiri ya ɗan ɗebe shi, amma  ya tattara nutsuwartsa, yana addu'a, ya nufi motar.
Suka gaisa da direban nasa, yayi masa ya hanya, daga nan ya ce ya gaya masa in da zai kai shi.
Mintuna ashirin ce ta kaisu, a harabar wata plaza suka yi parking, Adam ya buɗe motar ya fita.

Wani matashi ne zaune wanda zai yi sa'an Adam, yana danna computer, yana ganin Adam ya miƙe cikin girmamawa yana murmushi ya ce "Barka da zuwa"

Adam ya ƙarasa yana murmushi, ya miƙa masa hannu suka gaisa, sannan ya zauna.

Matashin ya kalli Adam ya ce "Adam, ya aka yi an shirya zama da kai, amma ba ka yi attending ba?, na din ga kiran wayarka ba ka ɗagawa, har wayar ma ta daina shiga gaba ɗaya?"

Adam ya ɗan taune lips ɗinsa na ƙasa ya ce "Am sorry Habib, wata matsala aka samu, amma komai normal yanzu in sha Allah".

Cikin kulawa Habib ya ce "Are you safe?"

Adam ya jinjina kai sannan ya ce "Me aka tattauna, wace matsaya aka cimma?"

Habib ya ɗan rausayar da kai ya ce "To, mun tattauna yadda yakamata, amma dai kamar yadda na yi maka bayani da farko, ko da ka fito ƙarara ka bayyana lamarin nan, ko an je kotu za a sake su, saboda haryanzu baka da wata cikakkiyar hujja ta zahiri da zaka kafa, yanzu ko kun yi wani abu a kai, ya riga ya gama shiri, da tattaunawa da lawyoyinsa, ya shirya tsaf da ka yi attacking zai yi depending, yanzu abin da yafi shine ka sake mayar da hankali sosai da kai da abokan aikinka, ku samo hujja ta gaske, ta zahiri da za ayi amfani da ita, nima zan shirya tsaf domin cimma nasara ni da tawagarmu"

Adam yayi ajiyar zuciya tare da dafe goshinsa, ya sake ɗagowa ya kalli Habib ya ce "Duk wata hanya da zan bi domin neman hujjar kama mutumin nan an tosheta, kuma kullum kallon mutunci ake masa, ana sake bashi girma tare da shigar da shi cikin al'amuran ƙasar nan, bayan su ne babbar matsalar mu"

"Adam, tun da ka ga haka, ba shi kaɗai bane, ko dai an san me yake yi ake rufa masa asiri, ko kuma akwai wasu manyan da suke aikin tare "

"Haka ne, abin da nake tunani kenan nima, amma babu komai in sha Allah zamu yi nasara, zan cigaba da ƙoƙari, ina son magana da saifu ma, zan zauna a garin nan sai Allah ya kaimu monday zan koma kano".

Habib ya ce "To shikenan, Allah ya yi jagora, gashi ko shayi ban baka ba"

Adam ya girgiza kai ya ce "Kar ka damu"

Daga haka Adam ya tashi ya fita, ya saka direbansa ya mayar da shi masauki. Sam ya ƙi yadda yaje gidan sa, saboda wani Dalili nasa.

***

Ƙauye ne sosai in da aka kai ruma, sai dai mutane masu matuƙar karamci da girmama ɗan Adam, tamkar za su goya ruma, dan wasunsu duk basu santa ba, sai dai sun san mahaifinta sosai tunda ɗa ne a wurinsu.
Garin sun yi noma sosai, sai dai an girbe an tare shi a cikin gonaki, ba a kwashe an kai gida ba, ga yanayin garin kamar yanayin garin da aka yi wata annoba.
Wani wurin a ƙone, wani wurin dai gashi nan.
Tun da safe ruma ta fara cewa ita azo a mayar da ita gidan gwaggo, yau zasu koma gida ita da yaya Aliyu, amma dattijon da ya kasance ƙanin kakanta ne ya ce "Ai jikata ba ke ba tafiya, sai hutun makarantar bokonku ya ƙare, kina nan tare da mu"

A ɗan razane ruma ta ce "Saboda me?"

"Haka gwaggonki ta ce"

"Ni gaskiya ba zan iya zama a garin nan ba, gida nake so na koma na ga mama, na gaji, ni ku mayar da ni gida" ta yi maganar tana kuka.

Matarsa da ake kira da iya ta ce "Haba rumaisa, muma fa duk iyayenki ne, muna ƙaunarki sosai, ki kwantar da hankalinki kin ji, za a mayar da ke, idan ki ka matsa zasu iya ƙwaceki gaba ɗaya, 'yan kwanaki zaki yi a mayar da ke"

"Ni mama nake son na gani".

"Ki yi haƙuri, za a mayar da ke in dai wurin mama ne" An kai ruwa rana sosai da ruma, kan ta daina koke-koke, sai dai ita ma ta haɗa musu aiki, ba komai take ci ba, tsirfar yau daban ta gobe daban.

In da ta ɗan ƙara samun sassauci, shine tana tare da lawisa, kuma a gidan akwai wata sa'ar tata zaliha, dan haka sukan ɗebe mata kewa.

***
Ba ƙaramin ɓacin rai 'yan mazan mama suka shiga ba, tun bayan da Aliyu ya dawo musu babu ruma, tare da sanar da su hukuncin da gwaggo ta yanke ba.
Abdallah ya ce "Wallahi gwaggon nan tana da matsala, tsabar mugunta ta yi garkuwa da yarinya dan son zuciya daga kai mata ita a sada zumunci".

Sai da suka yi dariya jin abin da ya ce, wai tayi garkuwa da ita.

Usman ya ce "Wane irin garkuwa kuma?".

"To idan ba garkuwa ba, ta yaya zata saka a kai yarinya wani ƙauye a ɓoyeta, wai ba zata dawo yanzu ba, amma idan ta cika musu ciki da rashin ji, ai sa dawo da ita da kansu"

Suna cikin tattaunawar mai sunan Baba ya dawo, suka gaisa da Aliyu, ya tambaye shi ina ruma? Ya sanar masa da yadda suka yi da gwaggo.

Tsuke fuska yayi ya ce "Wane irin abu ne haka? Idan na gama exams ranar lahadi zan je na taho da ita, akan me zasu riƙe ta?"

Mama ta ce "A'a babana, tun da na haƙura dan Allah kuma ku yi haƙuri ku ƙyalesu, yanzu sai ace zigaku nake yi, su je su ƙarata, sati biyu ai kamar yau ne"

"Duk da haka, bai kamata ruma ta zauna a wurin nan ba, babu tsaro gaba ɗaya dole zan je na taho da ita, dan ba ta zuwa makarantar boko yanzu, islamiyya fa?" Sosai ya ɗau zafi, mama dai ta ce ba ta yadda wani yaje ya ce zai taho da ruma ba.

***
Gaba daya ta tattara hankalinta da nutsuwarta a kan litattafanta, gefe kuma ga calculator tana dannawa, tayi ɗai ɗai a ƙasan carfet, ta saki dogwayen kalbar da aka yi mata, ta zubo har kafaɗarta, duk da kalbar ta tsufa amma ta yi kyau sosai.
Nusaiba ta turo ƙofar ɗakin ta shigo da sallama.
Iman ta amsa mata, ta zuba mata ido tana kallonta.

"Sarkin littafi, me kuma ake yi?" Iman ta kalli litattafan ta yi murmushi ta ce "Boko nake ci masoyiyya, ta samu ne?"

Nusaiba ta zaune ta ce "Eh to, ba nace ba, uncle J ne ya zo, kuma da alama ke yake son gani, sai tmbayata yake kina ina?"
Tsaki iman tayi, ta gyara zamanta tana ƙoƙarin mayar da kanta kan litattafanta.

"Kai, uncle J ɗin ki ke yi wa tsaki, ya zo ya sakani a gaba sai tambayata yake kina ina?"

"Anty Nusaiba dan Allah ki ƙyaleni da sabgar mutumin nan, wai me zan yi masa ne dan Allah?"

"Nifa na kasa gane abin da kuke ɓoyewa, anya ba sonki yake yi ba?"

Da sauri iman ta girgiza kai ta ce "Dan Allah Anty Nusaiba kar ki ɗaga maganar nan, idan har Ammi ta ji za ta bayar goyon bayan hakan, ni kuma ba zan watsa mata ƙasa a ido ba, amma ni bana sha'awar duk wani wanda ya fito daga masarautar na, ke kin san me nake nufi".

Nusaiba ta yi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan, na daina cigaba da aikin ki, zan je na ce masa bacci ki ke kawai"

Iman ta jinjina kai alamar to.

****
Tafe suke su uku, ruma na ta shan tsamiyar biri tana zubarwa a hanya, mayafinta a kafaɗa. Su fuskarsu duk da hoda da kwalli, ruma kuwa tata yadda take haka take kamar namiji, kunneta babu ko ɗan kunne.

"Kai ku tsaya" ruma tayi maganar tana kallon wata bishiyar mangwaro, 'yar gajeriya amma tayi 'ya'ya fal.

Suka kalli ruma suna son jin dalilin tsayar da su ɗin.

"Mangwaro zan tsinka".

A ɗan razane Zaliha ta ce "A'a ruma, a garin nan fa bakomai ake taɓawa ba, baki ga gonaki duk an yi girbi ba, amma ba a ɗauka ba,masu garin ake jira su zo su yanke harajin da za a biya sannan a ɗebi amfanin gona, yanzu idan suka zo wucewa suka ganki, zaki saka mu a matsala.

"Suwaye masu garin?" Ta yi maganar cikin ko in kula.

Lawisa ta ce "Ke dai ki bari kawai ruma, ki bari idan muka je gida sai a saka a samo miki"

Ruma ta cire mayafinta, ta ɗorawa lawisa a kafaɗarta, ta nufi bishiyar nan, suna ƙwala mata kira, amma ba ta tsaya ba, ta kama bishiya ta haye kamar buranya, hawan katanga da bishiya ba abu ne mai wahala a wurin ruma ba.

Ta naɗe doguwar rigarta, ta tara mangwaron sannan ta saukko, su kuma suna ƙasa suna jiranta cikin tsoro suna cewa ta sauko.

Bayan ta sauko ta karɓi mayafinta ta zuba a ciki, ta saɓo abunta tayi gaba ta ƙyalesu.
Bin ruma suka yi da kallo, ta ci uwar ubansu a rashin ji, haka suka rufa mata baya suna kallonta.

Suna cikin tafiya suka ga ta saki hanya ta shiga wata gona, tarin masarar da aka jingine ta je ta fara ɗauka.

"Innalillahi, dan Allah ruma kar ki janyo mana masifa, dan Allah ki fito mu tafi, duk wanda aka gani a gona bayan girbi ba a biya haraji ba kashe shi za ayi".

"Kisa kuma sai ka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login