Showing 189001 words to 192000 words out of 224014 words
razana iman ta yi da ya shigo ɗakin, wanda ita kanta ba ta san dalilin razanar ba.
Ya risuna ya gaida ammi, sannan ya tunkari rumaisa, ya durƙusa ya riƙe mata kunne ya ce "Abinci ba kifi ba nama ba zaki ci ba ko?" Ya ajiye mata leda a gabanta ya ce "Ki kai musu su dafa miki wani abun, dan yanzu ma sai ki ce yayi sanyi ba zaki ci ba, tuwo ma ki ce ba zaki ci ba, ki yi ta wahalar da mutane babu dalili". Ta sunkuyar da kai ta ƙi magana. Ya dungurar mata da ledar ya sanya hannu ya ɗau sabir a kan cinyarta ya yi waje.
Ammi ta din ga murmushi, gaba ɗaya rayuwar rumaisa burge ammi take yi.
Kifi ne manya ya kai na dubu, mai sunan baba ya kawo wa rumaisa, ta tashi cikin murna ta tafi kai wa su yasir su yi mata wani girkin bisa umarnin mai sunan baba.
Ammi ta dubi mama ta ce "Amma dai kamar akwai wani abu da yake damunki, bayan rashin lafiya ma"
Mama ta ce "A'a, jinina ne ya hau"
"A tunanina zuwa yanzu mun zama ɗaya, dukkanninmu iyayene, masu fuskantar matsalar iyali kala-kala, dan Allah idan wani abu ne ke faruwa kar ki ɓoye mini ko ba zan yi wani abu a kai na yi addu'a"
Mama ta nisa ta ce "Babar ƙawar rumaisa ce ta zo, take gaya mini maƙwabtana na ta yaɗa jita-jita, wai rumaisa ciki ta yi, na kaita garinmu ta haihu, muka ce wai saceta aka yi, wai Allah ne kaɗai ya san yadda muka yi da ɗan"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, maƙwabta kuma?"
"Wallahi kuwa shi ne abun ya dameni, wai abun ya cika unguwa, sun ɓata mini sunan ƴa, na san rumaisa ba ta ji, amma ko kusa komai zaki yi wa rumaisa ba ta san hanyar lalacewa ba, balle ta yi ciki".
Ammi ta ce "Wallahi ba sai kin faɗa ba, duk wanda ya ji maganar nan ya san son rai ce, ki yi haƙuri basu isa su ɓata mata suna ba, duk wanda yake son ta da gaske jita-jita ba zata hana shi aurenta ba, ki kwantar da hankalinki kuma kar ki bari ta sani, tun da da bakinta ta ce mini duk wanda yayi mata abu sai ta rama" shigowar rumaisa ɗakin ce ya sanya ammi sauya maganar.
Suka miƙe zasu tafi, rumaisa ta ce "Ammi, an ɗora mana abinci fa, ku tsaya a gama"
Ammi ta ce "Tuba muke, muna sauri ne, ayi haƙuri" rumaisa dai ba haka ta so ba.
Suka fito zasu tafi, mama ta ce ina ga mai sunan baba yana waje da sabir.
Suka fito aikuwa yana wajen, ammi ta ce "Iman karɓo sabir"
Jikinta har rawa yake yi, saboda gaba ɗaya mai sunan baba tsoro yake bata.
Kamar munafuka sai sunkuyar da kai take, ta miƙa hannu za ta karɓe shi, amma shiru bai bata shi ba.
Sai da ta ɗaga kai suka yi ido huɗu, gabanta ya sake faɗuwa, har numfashinta ya tsaya na wucin gadi.
Ganin yadda ta tsorata ta rikice, sai da ya bawa mai sunan baba haushi, shi ba dodo ba meye na wani tsorata.
Ammi ta saka sidi ya buɗe booth, ya ɗebo cartons na lemo da kayan marmari, na dubiyar mama.
Ammi ba ta tsaya ba, dan ta san mama cewa za ta yi yayi yawa, suka shiga mota suna ɗaga musu hannu.
Tun da suka tafi ammi take saƙawa da warwarewa a zuciyarta, dole mama ta shiga damuwa, babu uwar da za ta ji daɗin a ɓata sunan ƴa a cikin unguwa dan wannan kawai sai ya hanata auruwa.
Suna tafe Nusaiba da iman na ta yi wa rumaisa dariya, yadda take gudanar da al'amuranta da yadda yayyenta ke kula da ita.
Tun a hanya ammi ta kira adam a waya, ta ce idan an yi sallar magariba tana son ganinsa.
Kamar yadda ta buƙata ya je ya sameta, ta idar da salla tana lazumi, bayan ta kammala ta dube shi ta ce "Mai ka yi wa rumaisa ne? Take cewa da tana da zuciya ba zata sake ɗaukar sabir ba?"
Ya kalli ammi ya ce "Wani abun ta ce na yi mata ne?"
"Ba ta ce ba, amma abun da ta faɗa ya tabattar mini da wani abun ka yi mata"
"Ba wani abu bane ammi, na mata gargaɗi a kan zuwa gidan nan ne? Idan aka fuskanci wacece, za'a iya ƙoƙarin citar da ita ko cutar da sabir ta hanyar ta".
"Na ji, yanzu ba wannan ba ma, wata shawara na yanke a matsayina na uwa na kira ka na sanar da kai, ba dan kana da hakki a kan abun ba ma sai dai ka ji na zartar".
"Wane hukunci kenan?"
"Ina son ka auri rumaisa!!!"
*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*
*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*
*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*
👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*
*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*
*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*
*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*
*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*
*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*
*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*
*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*
*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*
*9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*
*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*
*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*
*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*
*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*
*15. Supplement for Acne, dark spots remover*
*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*
*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*
*Littafin kuɗi ne, ₦500 ne via 0009450228 sai shaidar biya ta 08081012143, aisha adam jaiz bank, masu buƙatar vip kuma, zasu iya zuwa arewabooks su yi searching sunan littafin*
Waro ido adam yayi yana kallon ammi, yana tunanin ko haluccinations ɗin da ya saba ne ba gaskiya bane, ya tsatstsare ammi da ido.
"Ba ka ji me nace bane kake kallona?"
"Amm..mmm wai wace rumaisa?"
"Rumaisa dai ta zo da sabir, ita nake nufi"
"Amma ammi nan da shekara nawa?"
Ammi ta ce "Nan da abun da bai fi watanni uku ba in Allah ya kaimu"
Adam ya ma rasa me zai ce, "Amma ammi yarinya ce ƙarama, me ta sani a kan rayuwar aure? Ta yaya zan yi rayuwar aure da ita"
"Saboda kai abu ɗaya ka saka a gaba a zamantakewar aure ko?"
Da sauri cike da jin kunya ya ce "No, ammi ba abun da nake nufi ba kenan, amma meye manufar yin hakan?"
Ammi ta numfasa ta ce "Ɗazu muka je gidan su, mahaifiyarta babu lafiya a dalilin jita-jitar da ake yaɗawa, wai ciki ta yi aka kaita ta haihu, ni uwa ce na san raɗaɗin irin wannan abun. Abu na biyu kuma a duniya na san babu wata mace da zaka aura ta riƙe sabir da imani da amana kamar rumaisa, ba zan so sabir ya yi rayuwa irin wadda mahaifiyarsa ta yi"
"Amma, Ammi yarinyar nan ta daɗe a hannun ƴan bindiga, Allah ne kaɗai ya san abun da suka yi mata tsawon wannan lokaci"
"Ko sun yi mata wani abu, kai yakamata ka yi shahadar aurenta, ko dan albarkacin abun da ta yi maka. Sannan ka san dole za a saka mana ido, a fara zancen ka yi aure, ko ma ace gashi an baka mata, wanda idan aka baka bamu isa mu ce a'a ba. Dan haka kafin su motsa mu zamu motsa, idan ya so ko wani auren ne ka yi daga baya, amma ina son ka auri rumaisa ka inganta rayuwarta, ta yi karatu mai kyau mai zurfi, ka ciyar da ita abinci mai kyau, ta kwana a muhalli mai kyau, ba zamu biyata abun da ta yi mana ba, amma zamu iya kyautata mata".
Adam ya ja wani irin gwauron numfashi, dan ya san akwai ƙura, ita kanta rumaisan ba lallai ta amince dan ta ce a duniya ba wanda ta tsana kamarsa.
"Ka yi shiru ba ka ce komai ba"
"Shikenan, Allah ya tabbatar mana da alkhairi".
"Amin ya Allah, Ubangiji Allah ya yi maka albarka, Allah ya sanya ta zame maka alkhairi a cikin rayuwarku" jinjina kai kawai ya yi, bai iya amsawa ba ya tashi tafi.
Tun da ya fita kansa har wani zafi yake yi masa, saboda tsabar caji da zafi, kamar shi ya auri wannan fitsararriyar yarinyar da take iƙirarin ta tsane shi. Lokaci ɗaya ya tuna yadda ƴan bindiga ke cin zarafin mata a hannunsu, Allah ne kaɗai ya san meyafaru da ita, duk da likita bai faɗi wani abu da ya shafi hakan a kanta ba lokacin tana asibiti, amma duk da haka ba shi da tabbas.
Har lokacin kwanciya baccinsa yayi, ya nemi wuri ya kwanta, bacci ya gagare shi, tunani kawai yake yi, tayaya zai zauna zaman aure da wannan fitsararriyar yarinyar mara kunya, wadda ko magana ba ta iya ba, shi ga saurin fushi da zuciya tsaf zai ɓallata wataran. Baya son bijirewa ammi, sai dai har ga Allah amsa matan da ya yi ba har zuciyarsa bane ba, dan shi auren rumaisa a wurinsa zai ƙwaru da yawa.
Shi a rayuwarsa ba shi da sha'awar zama da mace sama da ɗaya, sakamakon irin zaman da ya tashi ya ga yana yi a gidansu, ba ya son ɗan sa ɗaya ya tashi a irin yanayin da suka tashi na makircin matar uba. Hakazalika ba zai so ya zauna da mata biyu ya ƙwari ɗaya ba, ga uwa uba kishi da tashin hankalin mata shi ba zai iya ba, abubuwan kansa sun isheshi.
Auren rumaisa kuma a yanzu gara zamansa a haka ba mace, ina amfanin yayi aure da matar da babu duk ɗaya, sai ma da yayi raino, dan wannan raino ammi za ta ɗauko masa, tun da ta ce ya kula da cin ta shan ta da makarantar ta, ban da haka shi bai ga mai rumaisa za ta tsinana a gidan aure ba.
A hankali ya lumshe idanunsa ya na son bacci ya ɗauke shi, saboda tarin matsalolin da suke kansa, sun sanya har wani zafi cikin kansa yake yi masa.
Yayi ta karanto adduoi, a hankali bacci ya fara ƙoƙarin ɗaukarsa, cikin barcin ya ji muryar rumaisa da kan yi masa gizo tana faɗin "Sarki mai koriyar alkyabba ka ɗanani a kan doki" da ire-iren maganganun ta, suka dinga kai komo a kunnensa.
A hankali ya buɗe ido, haryanzu ya kasa daina mamakin yadda rumaisa take yawan yi masa gizo. Ya canza bugiren da yake kwance yana karanto adduoi, a take wani baccin yayi awon gaba da shi, sai dai a wannan karon aisha ya din ga mafarki, mafarkin ƙarshe da yayi da ita ya ɗan razana shi, aisha ya gani tana ce masa.
"Takawa, dan Allah ka bawa rumaisa ɗan ta, kar ka ɗau hakkinta, bana son wata damuwa ta sameta, ita ce maganin damuwowinka, ko ba ka aureta ba kar ka rabata da ɗanta" a razane ya sake farkawa yana wani irin gumi, ƙirjinsa na bugawa da sauri.
Da sauri ya saukko daga kan gadon, ya buɗe tagar ɗakinsa, ya zubawa harabar gidan ido, ya tuna abubuwa da dama da suka wakana, shekarun da suka gabata.
Ganin bashi da wata mafita, ya sanya ya shiga banɗaki yayi alwala ya fito ya ɗau alƙur'ani.
Ɓangaren ammi ma tsayuwar dare take yi, tana kaiwa Allah kukanta a kan iyalanta, dan addu'arta bayan nemawa kanta gafarar ubangiji, ƴaƴanta kawai take yi addu'a.
Ta haɗa da roƙon Allah ya ɗorata a kan iyayen rumaisa su yarda da auren nan da take son haɗawa, dan a jikinta take jin rumaisa alkairi ce ga ɗan ta.
Yau jikin mama da ɗan sauƙi, ruma sai shirin tafiya tahfiz take yi, su Huzaifa sun goge mata uniform ɗin, ta cika tsakar gida da waƙe-waƙe kamar an yi mata bushara da wani abu mai muhimmanci.
"Ruma ki rufe mini baki da waƙe-waƙen nan, ki yawaita tasbihi, wannan surutan da waƙe-waƙen ba in da za su kai ki"
"Mama ina tasbihin nan fa".
"A'a, ni wasu lokutan ina raina ibadar da ki ke yi, ki na da ƙarancin ibada rumaisa, idan kina cikin farinciki ki yawaita ambaton Allah, dan wasu lokutan idan kana cikin matsala ko damuwa sai addu'a ma ta gagareka, ki din ga yawaita ambaton Allah ba waƙa ba"
Cikin mamaki rumaisa ta ce "Mama yanzu sai damuwa ta yi wa mutum yawa ya kasa ambaton Allah, to ko a hannun 'yan bindiga, addu'a na yi ta yi musu, Allah ya ƙwatoni, amma ni mai zai dami mutum ya kasa addu'a "
Mama ta yi murmushi ta ce "Rumaisa kenan, lokaci yana nan zaki gane abun da nake nufi".
"Au fata ki ke yi mini" tayi maganar cikin tura baki.
"Ya za ayi in yi miki fata, faɗa nake yi miki, ki ƙara nutsuwa".
"To hajiya mama, yanzu dai ki bani kuɗin makaranta zan tafi"
"Ke idan babu kuɗin makarantar ba zaki ba kenan?" Huzaifa ya tambayeta yana ƙoƙarin ɗaukar agogonsa.
"Ni fa ba na son katsalandan ina ruwanka"
"Ni kar ku yi mini faɗa, ki ɗauka ki tafi".
Rumaisa ta ɗau kuɗin, ta fice tana hararar Huzaifa.
Ammi ta din ga lissafin ta ina za ta ɓullowa wannan al'amari, turaki zata fara gayawa, ko kuwa ta fara nemo iznin majaifiyar rumaisa tukuna?
Daga bisani ta yanke za ta fara tuntubar ɓangaren rumaisa, idan sun amince shikenan, sai dai tana fatan su amince ɗin ma.
Takawa har garin Allah ya waye bai samu ya rintsa ba, abubuwa da yawa sun dame shi, kasancewar yau weekends ne, ya sanya karyawa ma a ɗakinsa yayi bai fita ko ina ba. Dama shi ba wasu abokai ne da shi ba, daga abokan aikinsa sai su jabir.
Wayarsa ta cika masa kunne, duk da gandar da yake ji, da ya gaji da jin rurin wayar, sai da ya tashi ya ɗauko wayar ya duba.
Kakin rundur ƴan sanda ne cp baba habu yake kiransa, adam ya ɗaga wayar tare da yin sallama.
Cp ya amsa masa suka gaisa sannan ya ɗora da cewa "Adam kana garin nan kuwa? Wai ba zaka fito ka yi magana a kan abun da yake faruwa ba, sai sharri ake yi maka kala-kala kai kuma ka ƙi magana"
Adam ya yi ajiyar zuciya ya ce "Me zan ce? Ko na faɗa ba za a yarda da ni ba, ƙanin mahaifina ya fito ya wanke ni, amma ba a fasa surutu ba, me zan ce? Su yi ta yi idan sun gaji za su daina ne"
"Kana nufin ba zaka ce komai ba?"
"Ko na ce ba za a daina ba, ka ga maganar ba ta da amfani"
Cp ya ce "Ai shikenan, ɗazu mun yi magana da commissioner, saboda sabon posting ɗin da gidan jaridar nan ke cigaba da fitarwa, na yi magana da manema labarai, na sanar musu hukumar ƴan sanda mun san da case ɗin, sai dai abu ne na sirri da ba ya buƙatar a fito ayi ta yayatawa, shi ya sanya muka yi shiru muka yi ta bincike, kuma haryanzu muna kan yi ma."
Adam ya nemi wuri ya zauna a gefen gadonsa ya ce "To shikenan yallaɓai, na gode sosai da sosai"
"Kar ka damu, ai hakkinmu ne baka kariya, kuma abun da muka faɗa hakan yake ai, Allah ya tsare, wannan ba wani abu bane ba duk aikin maƙiya ne, kuma ba za su yi nasara ba"
Adam ya ce "Haka ne, na gode sosai"
"Masha Allah, Allah Ya ƙara tsarewa"
"Amin ya rabb sir, na gode" daga haka ya kashe wayar. Yana gama wayar ya ji zaman ɗakin ya ishe shi, dan haka ya fita domin ya gaida ammi ya ɗan fita.
Duk a falon sashen ammi ya tarar da su, har ammin, ana koyawa Sabir zama an shiryashi cikin wasu kaya masu kyau, an zaunar da shi a gefen kujera, cikin dabara iman tana taje masa sumar kansa, sai kai hannu yake yana turewa alamar ba ya so.
Adam ya fara gaida ammi, sannan ya ɗau sabir ya zauna da shi