Showing 102001 words to 105000 words out of 163036 words
FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣7️⃣
........Wajen ƙarfe tara ALLAH ya kawo aunty Bilkisu ɗakin zata ɗauki kayan biki data ɓoye dan bama facalolinta da zasu wuce. Da sauri ta ƙarasa gaban gadon tana ambaton sunan ALLAH. Ta kai hannunta a goshin Lulu dake barci. Zafi zau har tana jin harbawar jijiyoyin kan nata. Bargo taja ta lulluɓa mata, sannan ta kwashi abinda tazo ɗaukar ta fice. Bata san yin kwakwazo hankalin mutane ya dawo nan, dan haka ta sallami facalolin nata sannan ta koma cikin raɗa ta sanarma Ammah da ke a cikin danginta da zasu kwana. Hankalin Ammah ma ya tashi, ta miƙe cikin hikima ta shiga bedroom ɗin, itama dai tattaɓa goshin nata tai, sai kuma ta juyo tana kallon Aunty Bilkisu.
“Yanzu ya za'ayi kenan? Dan nima bana son kowa ya fahimta baki baka san yanda na wani yake ba”.
“Hakane Ammah, to kodai a kira Hydar, sai ya samo mata magani”.
Ɗan jimm Ammah tai na tunani, sai kuma ta ɗan sauke ajiyar zuciya da faɗin, “Kirashi ɗin to. Ki kuma turomin Auntynku”.
Da to Aunty Bilkisu ta Amsa tana fita, sai da ta fara zuwa tai kiran aunty Amarya da Ammah tace kafin ta wuce sashen samarin gidan. Duk suna waje wajen dj balle ga ƴammata dama cike da gida, dan kusan duk ɗakunan ma a kulle suke, sai ɗakin Smart ne da ya nuna haske ke tabbatar da mutum a ciki. Sallama tayi aka amsa mata sannan ta shiga. Shi da Ahmad ne kawai a ɗakin, dan abokansu su kam yau duk kowa ya kama gabansa tunma da safe kasancewar gobe idan ALLAH ya kaimu Monday kowa zai koma kan aikinsa. Ahmad da ke zaune yana shan fura ya dubi aunty Bilkisu da murmushi yana faɗin, “Aunty Babba ke da kanki”. Murmushin ta mayar masa da faɗin, “To ya na iya Ahmad, amaryarku ce babu lafiya”.
“Ya Salam! Miya faru?”.
Ya faɗa da sauri. Dai-dai nan Smart ya fito da ga toilet da alama wanka yayi, sai dai sanye yake da jallabiya sai ƙaramin towel yana goge sumar kansa. Su biyun duka ya kalla saboda jin abinda Ahmad ya faɗa, da son jin amsar da Aunty Bilkisu zata bada. Cikin damuwa ta ce, “Zazzaɓi ne da ciwon kai mai zafi. Gata can cikin bargo tanata rawar sanyi ma”.
Smart ya ɗan lumshe ido ya buɗe, sai kuma ya ɗauki turare ya ɗan fesa da faɗin, “Inaga hayaniyar nan ce....”
“Hakama Ammah tace, shiyyasa ma tace a kiraka”. Aunty Bilkisu ta katsesa da sauri. Ɗan Basket ɗin da yake ajiye magunguna ya ɗauka, sai kuma ya dubi Ahmad da faɗin, “Ina zuwa”. Kai ya jinjina masa da mata addu'ar samun lafiya. Su kuma suka fice. Cikin gidan da sauƙin mutane dan duk ana waje wajen dj, sai ƴan tsofaffin ne da suka gaji sukai zamansu. Aunty Amarya ce ta taresu tun a farkon shigowa tace su biyota. Binta sukai sashenta, falon babu kowa sai yara da aka kwantar, kuma duk yaranta ne, dan ita danginta ma duk sun wace sai ƙanwarta budurwa da zata kwana tana kuma tare da su Maryam. Kai tsaye bedroom ɗin ta suka shiga, Lulu da aka maido nan tana kwance a gado cikin bargon da Aunty Amarya ta lulluɓa mata. Aunty Bilkisu tace “Yauwa nan aka maidota ashe?”. Amsa Aunty Amarya ta bata da “Eh nan ɗin yafi ƙarancin hayaniyane”. Sai kuma ta kalli Smart da ya zubama gadon idanu kawai batare daya ƙarasa ba. Katseshi tai da faɗin, “Hydar ƙaraso, Bara a samo ruwa tasha magani, sai dai banajin ma tunda aka kawota gidan nan taci wani abu. Ko a ɗan samo mata abinci? Ko tea haka ko”.
A hankali ya ce, “Ko tea ɗin dai zaifi”.
Babu jimawa Aunty Amarya ta dawo da tea da ruwa. Tana ajiyewa suka fice ita da aunty Bilkisu, sai lokacin ya ƙarasa gaban gadon. Da ga tsaye ya kai hannu kan bargon ya ɗan yaye kaɗan idanunsa suka sauka akan ƙyaƙyƙyawar fuskarta. Kamar ko yaushe yau ma babu kwalliya, sai wani irin sirrintaccen ƙyawu data ƙara fiye da yanda ya santa. A karo na biyu bayan ranar dinner daya riƙe mata hannu ya taɓa jikinta yanzu ma. Saukar hannunsa mai sanyin danshin ruwan wankan daya fito ya sata buɗe idanu kamar a ɗan zabure. Cikin sa'a kuwa suka faɗa cikin nasa saboda shima kallonta yake. Sake waro idanun tai da ƙyau, sai kuma ta kai hannu ta buge masa nasa hannun da har yanzu ke akan goshin nata tana hararar sa. Cikin ƙarfin hali ta ce, “Kai kuma waya gayyatoka nan?”. Yanda tai maganar da son yin masifa sai dai babu ƙarfi yaso bashi dariya, amma sai ya danne abarsa baiyi ba, sai ma kaiwa zaune da yay a bakin gadon har jikinsu na gogar juna sai dai ita a bargo take, kanta ya ɗan kifo yana raba hannayensa gefe-da-gefenta ta kasance a tsakkiya. Idanunta data sake rufewa ta buɗe da sauri jin saukar numfashinsa saman fuskarta duk da akwai ƴar tazara a tsakaninsu, ta sake watsa masa harara ta ce, “Kai kuma wai miye haka? Kake yi”.
Karan farko cikin ɗan lumshe idanunsa da buɗewa a lokaci guda ya motsa lips ɗinsa dan shima dai ciwon kansan nan na tare da shi a yau ma yini guda. Dan ma yanata addu'a da shan addu'oi wajen Malam sannan Abba yay masa kamu ɗazun da magrib shine ma ya ɗan samu barci sai yanzu ya tashi yay ɗan wanka zaiyi sallar isha'i da shafa'i da wutri aunty Bilkisu taje. “Zan dai yi Madam. Amma first ina son sanin mike damunki?”. Yay maganar cikin tausasa harshe sosai.
“Meya ruwanka malam nifa bana son shishshigi ka sani”. Itama ta faɗa cikin tsiwa da takurar yanayin kusancin nasu.
“Inafa na sani, sai dai yanzu da kika faɗa zan kiyaye. Amma yanzu dai ni ba faɗa nazo muyi ba, tashi kici abinci kisha magani”.
“Nace maka ina buƙata ne?”.
“Basai kina buƙata ba ai”. Ya bata amsa yana ɗaura hannunsa saman bargon zai yaye. Tattaro bargon tai ta da sauri ta tattaro cikin hannunta zata fisge daga nashi. Hakan yasa ya ja shima, itama ta ja, ya ƙara ja, itama ta fisga cikin sake fusata duk da bata da wani ƙarfin kirki a jikinta. Ga bakin masifar sai motsi yake alamar magana take son yi amma bata fita. Da ɗan ƙarfi yaja kasancewar ƙyaleta kawai yake dama, aiko ya ɗage bargon. Gaba ɗaya ta tattaro da hannunsa da bargon ta fisgo cikin takaici sai kawai ya biyo su shima ya faɗa mata a jiki fuskokinsu kan na juna kowa na shaƙar numfashin ɗan uwansa, lips ɗinsa a kan nata. Sosai zukatansu suka hau dokawa da sauri-sauri a tare, sai dai kowanne da dalilinsa. Lulu da wani shuɗaɗɗen al'amari mai matuƙar zafafa zuciya da ƙonata ya fara son hasko mata a memory tasa dukan sauran ƙarfinta ta turesa jikinta na rawa. Hakan bai sakashi yin ko gezau ba, sai dai shima ya matsar da fuskarsa da ga kan nata, sai kuma ya ɗagata jininsa na wani yamutsawa. Zaune ta tashi tana ƙoƙarin sauka a gadon kamar wadda ke neman rasa nutsuwarta dan jikinta rawa yake, yay saurin dakatar da ita cikin sassarfar harshe shima. “Ina kuma zaki je?”. Ganin tana cigaba da janye bargon zata saukan ya riƙota da sauri. Harara ta watsa masa da idanunta da suka kaɗa sosai. Ga jikin nata rawa yake da gasken fa. Magana take son yi amma ta kasa, sai idanunta dake cikowa da ƙwalla. Mamaki sosai hakan ya bashi, amma sai ya sake yinƙurin riƙota.
Hannunta ta fisge, sai kuma ta dafe kanta wasu hawaye masu zafi na sake wanke mata fuska. Idanu ya zuba mata ganin yanda jikinta ke ƙara ƙarfin rawa, hakan ya matuƙar sake ɗaure masa kai da zuciya, dan yanayine bawai mai nuna ƙin da take masa ba matsayin wanda bata so ko tafi ƙarfin aurensa, ba kuma kuya bace. Al'amarin nata kamar dai like wadda ta tuna wani mummunan al'amari mai firgitarwa da ciwo a zuciyarta da yay kamanceceniya da yanayin da suke ciki. Kanta ta sake girgizawa da sake yinƙurawa zata ƙarasa sauka ya miƙe da sauri ya zagaya gabanta. Cikin nuna kulawa da son maidota a nutsuwarta ya ce, “Kinga Please relax, ko mima zuciyarki ke son ayyana miki ba haka bane ba, koma ki kwanta kinga baki da lafiya”.
“Idanunta da sukai masifar kaɗawa da ja ta ɗago ta zuba masa. Sai kuma taja da baya da ga kusa da shi har yanzu dai da alamar bata samu nutsuwar da yake buƙatar ba. Shima sai ya matsa ɗin da kallon ƙofa ya kuma sake maido idanunsa kanta. “Kin gane bana son wani ya fahimci akwai wani abu a tsakaninmu saɓanin abinda suke kallo a bayyane. Ki daure zuciyarki na roƙeki koma mi kike tunani ki ajiyeshi gefe”.
Yaraf ta koma saman gadon ta zauna, hannunta dafe da kanta muryarta na fita da rawa da ɗan kaushi ta ce, “Ka kira min wata a cikinsu bazan iya zama da ga ni sai kai a ɗakin nan ba in har dole sai jikinka ya taɓa nawa”.
“Wancan ma mistake ne, bakuma za'a sake ba, Kinga ga tea kisha sai kisha maganin ki kwanta”.
Tabbas yanda yake mata magana a nutse ya taimaka ma ƙwaƙwalwarta wajen dawo da ita hayyacinta kan cewar bafa abinda ke mata kai-kawon bane ba. Sannan kuma tunda take da shi bai taɓa aikata mata makamancin hakan ba, lallai ta yarda mistake ɗinne kamar yanda ya faɗa. Hakane, ƙwarai hakanne mistake ne. Zuciyata ta shiga sake tabbatar mata. Sai ta fara sauke numfashi a hankali a hankali jikinta na ƙara samun ƴar nutsuwa. Gadon ta koma ta zauna ta jingina da fuskar gadon bayan taja bargon ta rufa, sai ya koma shima ya zauna a baki-baki da ƴar tazara a tsakaninsu yana sauke ƙaramar ajiyar zuciya ya miƙa mata kofin shayin da har ya ɗan fara hucewa..........✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣8️⃣
........Kai ta girgiza masa alamar bazata sha ba. Sai ya ce mata “Please ko kaɗanne! Kinga magani zaki sha”.
Yanda yay maganar da ɗan dafe kansa shima ya sata amsa dan har yanzu dai tafi buƙatar ya fitan ko zata fi samun daidaito yanda ya kamata. Kwankwaɗar shayin tai kamar ruwa kawai duk da akwai ɗan sauran zafin. Tasha kusan rabi ta miƙa masa kofin, amsa yay baice mata komai ba ganin ta ɗan sha. Ba tsoron magani take ba, dan haka ta amsa tasha shima salin alin, sai kuma ta zame ta kwanta tare da lulluɓe duk jikinta har kanta ta juya masa baya. Idanu kawai ya zubama bargon da take ciki, har yama rasa mizai hasaso game da abinda ya farun yanzu. Rashin makama ya sashi miƙewa da Basket ɗin magungunan, ya ɗan tsaya a kanta yay addu'ar da ake son yima mara lafiya da kuma ta barci ya tofa mata dan yasan idan yace zai tofa mata a hannu ta shafa bazasu wanye lafiya ba. Dan haka yay yanda zata fisheshi sannan ya fice.
Su Aunty Bilkisu na falon zaune da alama dakon fitowarsa suke, bai zauna ba ya ce, “Tasha maganin ta kwanta nima zanje na kwanta sai da safe”.
“ALLAH ya tashe mu lafiya”.
Suka faɗa a tare, yana ida ficewa yake amsawa da Amin. Koda ya koma ɗakin nasa ya samu Ahmad na wanka, dan haka ya zauna jiransa sai da ya fito ya shiga ya sake alwala ya fito. Sallar isha'i ya rama da yin shafa'i da wutri yay karatun Alkur'ani kaɗan dan wancan kiɗan na waje damunsa yake yi. Bai dai ce komai ba yay kwanciyarsa bayan sun ɗanyi magana da Ahmad dake tambayarsa yaya jikin Lulun. Ya amsa masa da cewar da sauƙi zazzaɓi ne. Daga haka ɗakin yay shiru, Ahmad na kallo a MBC Action shi ko yay luf tamkar mai barci, sai dai idanunsa biyu abinda Lulun taine ɗazun ke masa kaikawo a rai. Tabbas akwai abinda ya firgitata a dalilin abinda ya faru a tsakaninsu. Yana kuma tunanin kamar hakan ya tuna mata da wani abu ne da ya shuɗe a rayuwarta ko kuma.... Sai kuma ya ɗan furzar da iska kaɗan, hakanne yasa Ahmad jiyowa ya kallesa.
“Kai wai dama ba barci kake ba?”
Idanunsa ya ɗan buɗe ya kalla Ahmad ɗin. Shi kuma sai ya saki ƴar dariya da faɗin, “Oh dama likimo kayi, to kodai mun tauyeka ne da rashin baka amaryarka? Ai bata ɓaci ba yanzu ma sai a kawo maka ita nan ko kuma ku tashi ku wuce karma ku mana abin kunya an.....”
Bumm!! Yaji saukar filo akan bakinsa. Filon Ahmad ya riƙe yana murza bakin, sai kuma ya kalla Smart dake harararsa ya bushe da dariya. “Kufa dama masu shiru-shirun nan wlhy abin tsoro ne wajen ƙulafucin mace. To maida wuƙar yau ne kawai gobe i war haka kuna can manne.....”
Sake jawo wani filon Smart yay zai jefa masa yay saurin ɗaga hannu sama alamar surrender yana faɗin, “Yi haƙuri nayi shiru Zakin zaki. Haka kawai kamun dogon baki na kasa samun mai aurena nima”.
Ƙwafa Smart yayi ya ajiye filon, sai kawai yaja bargo ya lulluɓa yana juya masa baya ma. Dariya Ahmad ɗin ya cigaba da yi masa ta shaƙiyancin a kaikaice. Shi dai bai sake kulashi ba dan sosai abinda Lulu tai yanzu yay masa tsaye a rai yaƙi wucewa.....
*_WASHE GARI_*
Washe gari safiyar litinin kusan kowa ya tashi da ƙyar musamman ma ƴammatan nan da sukasha rawa da su Abdull da suma suka cashe kam basu tashi ba sai wajen sha ɗaya da ƙyar. Baƙi fa nata haramar tafiya musamman ma na nesa dangin Abba. Dan haka buɗar kai ma da wuri za'ayi. Alhmdllh amarya Lulu ma ta tashi garas babu zazzaɓin, sai dai damuwar son shan kayayyakinta da ke ƙara tsikararta. Tare suka kwana da su Amrah a ɗakin aunty Amarya. Koda aka kammala haɗa break fast Asma'u ce takai musu. Yanda ta gaishe da Lulu cike da girmamawa da kiranta aunty yay matuƙar mata tasiri a zuciya, sai taji ƙaunar Asma'un ya shigeta, gata ƙyaƙyƙyawa, kamanninta kuma sosai a bayyane suke da Smart. Tun jiya sun jone da su Afrah dan zasu iya zama sa'anni, sai dai Asma'u ta fisu nutsuwa a bayyane, su kuma sun fita wayewa. Dan haka ta basu hannu suka gaisa kowanne nama ɗan uwansa murmushi, a take kuma hira ta ɓalle a tsakaninsu sai Lulu ta zama ƴar kallo. Asma'u na tare da su har sai da Amal tazo tai kiranta sannan tai musu sallama da cewar zata dawo idan tayi sallar walha.
“Wannan kuma ina kuka samota?”
Cewar Lulu bayan fitar Asma'u. Kai tsaye Amrah ta bata amsa da “Aunty Lu ƙanwar Uncle Smart ce fa, tace mana itace auta a ɗakinsu. ALLAH yarinyar tana da daɗin zama bakiga yanda suka dinga karramamu jiya ba, mutanen gidan nan nada kirki”.
Shiru kawai Lulu tai tana kallon Amrah ɗin har na wasu sakkani, sai kuma ta ɗauke idanun nata sakamakon kiran wayar Afrah da akayi. Mommy ce, tana ɗagawa tace a Bama Lulu. Amsa tai cike da ɗokin jin Mommy, ta gaisheta da faɗin, “Good morning Mommy”.
Daga can Mommy ta amsa mata da kulawa da kuma tambayarta yanda suka kwana a baƙon guri da bin ba'asin babu dai wata matsala ko?. Samun kanta tai da amsawa Mommy ɗin da “Eh babu wata damuwa Mommy.”
“To Alhmdllh haka akeso. Sai ku zama cikin shiri gasu Auntynku nan tahowa buɗar kai, zasu kuma maidaki gidanki In sha ALLAH”.
Duk da bawani ta damu da zuwa can ɗin ba ko ɗaukar hakan da muhimmanci ta amsawa da Mommy ɗin da to. Da ga haka ta miƙawa su Amrah wayar ta ƙarasa shirinta dan tayi wanka harma ta saka kaya.....
Ƙarfe kusan sha biyu dangin Lulu suka iso gidan su Smart da shatara ta arziƙi na kayan gara dana rabo. Acewarsu waɗan nan iya na nan gidan su Smart ɗin ne nashi kayan garar ankai can gidansu. Koda Abba da aka kira yazo kai tsaye yace musu baza'a amsa ba kayan sunyi yawa. Haƙuri su Aunty Saliha sukaita bashi amma fir yaƙi, ya daice an amshi kayan rabo suyi kamar yanda al'ada ta tanadar amma kayan abinci kam a'a sunyi yawa. Wanda aka kaima Smart ɗin sun wadatar. Dole aka haƙura da sauke kayan daga motar da aka ciko da su sai iya na rabon kawai. Duk abinda ake Lulu taji, hakan kuma ya matuƙar bata mamaki, sai dai batace komai ba. Anyi rabo na bajinta daya tsayama su Umma arai, dan a kaf aurarrakin ƴaƴansu maza ko rabin hakan ba'ayi ba, hatta ƙannen Smart da ke ɗakunansu har ƴaƴan Aunty Amarya sai da aka basu abu, daga haka akai ɗan abinda al'ada ta tanadar ciki harda kai Lulu gaban surukinta Abba da tsirarun ƴan uwansa datai ƙyau cikin lass pitch color da yay matuƙar mata ƙyau skert da riga da mayafinsa, ga kayan sarƙa ta ɗora sai ɗaukar ido take duk da kwalliyar kaɗan ta yarda su Amrah sukai mata. Fuskarta a lulluɓe take, ta gaishesu kamar yanda aunty Saliha ta sanar mata tayi tunkan su fito daga ɗakin aunty Amarya. Abba yay