Showing 27001 words to 30000 words out of 163036 words

Chapter 10 - Furar Danko Book 1 Hausa Novel Complete

19 Dec 2024

432

idon Lulu ta ɗauka drinks da ruwa ta fita. Har yanzu yana zaune a motar ko buɗewa bai yiba, sai dai ya sauke gilashin tare da kwantar da kujerar yanda zaiji daɗi.
       Ita kanta yarinyar sai da taji wani iri datai tozali da shi. Dan Uncle Smart ƙyaƙyƙyawan mutum ne kuma nutsatstse ɗan gaye ga masifar tsafta, irin mutanen nan ne masu shegen tsaftar shiya da a wajen wasu suke ɗaukar harma tai yawa, duk da baida kuɗi bai kuma tashi cikin dukiya ba ALLAH ya bashi lafiyayyen fata mai ɗaukar idon mai kallonsa ga kamala da cikar haiba. Rashin yawan walwalarsa da shiru-shiru na zame masa adon kwarjini ga duk wanda zai dubesa ko zama da shi. Cikin ɗan daburcewar harshe ta gaishesa. Hannu kawai ya ɗan ɗaga mata dan tunda yay mata kallo ɗaya ya ɗauke kansa. Cikin ɗan in'ina ta ce, “Dama Aunty tace a kawo maka wannan”.
      Kamar zai share sai kuma yay magana cikin deep voice ɗin nan nashi mai rikita marasa jin magana musamman ƙannensa, mai kuma saka ƴammata da yawa mutuwa a kansa, “Waye aunty?”. Cikin motsa lips ɗinsa a hankali.
      (Masha ALLAH kaji wani dakakkiyar murya mai ratsa zuciya) ta faɗa a zuciya. A zahiri kam tai saurin faɗin, “Madam ɗinmu ƙawar aunty Lulu ƙamshi, Aunty Nadiy.....”
      “Ba buƙata”.
Ya katseta cikin ɗauke kansa da lumshe idanu yamayi sama da gilashin gaba ɗaya. Tsaye tai sororo kamar kayan ado, sai kuma tabar wajen jiki a sanyaye. A cikin shago har an fara kwance ma Lulu kalbar kanta da wanke mata ƙafafu, yayinda suke hira da Nadeeya ƙasa-ƙasa. Sai dai hankalin Nadeeyar gaba ɗaya na kan ƙofa ne. Da mamaki tabi yarinyarta data dawo da abinda ta fita a hannu. Sai dai batace komai ba gudun kar Lulu ta ganota. Kusan mintuna biyar da barin yarinyar wajen ya buɗe idanunsa. Haka kawai zuciyarsa ke masa kaikawo akan ledar fruit ɗin nan. Duk da wani gefe na kwaɓarsa ya kasa hana kansa dubawa. Ɗakkota yay, ɗaya bayan ɗaya ya fara fidda fruit ɗin da aka loda a sama. Kamar yanda zuciyarsa ke raya masa acan ƙasa wasu abubuwa ne daban, fiddosu yay baki ɗayansu ya maida fruit ɗin ciki tare da ajiye ledar a inda ya ɗauka. Wani irin dokawa ƙirjinsa keyi da sauri-sauri ganin mugayen ƙwayoyin dake a ƙasan, kasancewar shi ba ma'abocin shaye-shayen bane babu abinda ya fahimta a tare da su, sai dai yasan dole ƙwayoyin zasu zama na shaye-shayen ne. Sake naɗesu yay da ƙyau ya adana acan ƙasa inda ƙafafunsa suke, da ga haka ya sake buɗe motar ya fiddo ƙafafunsa dan yasha iska.
        Awani kusan huɗu Lulu ta kwashe a wajen gyaran jikin nan. Dan sai wajen 3 ta fito. Kallo ɗaya da yay mata sai da gabansa ya faɗi, yay saurin ɗaukewa yana jan siririn tsaki. Oho ita bama ta lura da shi ba. Dan yana da ga can gefe a bench na wani mai sai da ƙwa-ƙwa da aya da dabino dake ɗan jikin symbol ɗin shigowa harabar plaza ɗin. Tana da ga tsaye tana hararar motar da tunanin ko yana ciki amma shiru, a fusace ta fara knocking glass ɗin nan ma babu alamar za'a buɗe.
        Ashar ta mulmulo cikin ƙufula da faɗin, “Mi wannan illiterate ɗin ke nufi da nine wai? Barin wajen yay ko mi?”.
        “Kai haba shi ya fara wannan ganganci kamar bai san wacece Lulu ƙamshi ba ne”. Nadiya ta faɗa cikin ƙara fasa mata kai.
     “Ai da alama har yanzu ban sanar da shi ɗin ba. Guy ɗin nan fa mara mutuncine da kike ganinsa. Na barshi ne ban koreshi ba tun a ranar farko saboda sai na gama wulaƙanta rayuwarsa sannan da nuna masa banbancin da ƙasa da sama ke da shi”.
          Cikin ƴar dariya Nadiya ta sake faɗin, “Ai wannan karon drivern naki ne sam bai kama da driver ba wlhy. Irin wannan haɗuwa haka, da gani kuma akwai girman kai fa, koda yake ya kai yayi ne dan ya haɗu ba kary.....”
      “Mtsowww kema shashasha ta biyu da har kika zauna masa kallo haka. Ina wani abin haɗuwa mutum na warin talauci da jahilci. Ƙaton banzar bana zaton (A) kota kai girman garinsu ya sani”.
     Cikin dariya Nadeeya ta ce, “Kai Lulu harda sherinki, wannan ɗan ƙwalisar ne za'ace bai san miye A ba?. Da gani yayi karatu wlhy danni kamar ma na taɓa sanin fuskarsa a cikin ƴan ƙwallon Kano pillars sai dai nasan da wuya ace wancan ne”.
           Tsaki Lulu ta sake ja cikin gatse ta ce, “Sai dai ƴan ƙwallon kwashe gotta ɗin anguwarsu. Dalla malama ni kin isheni”.
      Nadeeya zata sake magana ya iso wajen, dan duk da ba jin mi suke faɗa yake ba da ga inda yake haka kawai zuciyarsa ke raya masa maganarsa suke, maganar kuma da bazata wuce zagi ya sha ba a wajen ƴar balaja'un tsagerar yarinyar nan. Wani banzan kallo Lulu ta watsa masa. Sai dai batace komai ba. Shima ɗin bai nuna yasan tana yi ba ya buɗe mata motar batare daya jira shigarta ba shi ya shige nasa mazauni.........✍️



_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥



*_ALLAH ya gafartama iyayenku😭🙏_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲




  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗



           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻


𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣7️⃣



........Sai da ta zagesa ciki-ciki da kalmar illiterate sannan ta shiga motar Nadeeya ta rufe da faɗin, “Sai mun haɗu anjima. Dan yau dole ne a warware gajiya Lulu ƙamshinmu ta samu lafiya. Barama na nemo Ɗan-takife ya haɗa mana kayan aiki yau network na gasken-gaske zamu hau”.
    Yatsu biyu ta ɗaga mata tana murmushi, shi kuma yaja motar batare da bari ta faɗi abinda tai niyyar faɗa ba. Dama tun a kallo ɗaya da yayma Nadeeya ya fahimci itama tana shaye-shayen. Dan ita har jikinta ma ya fara nuna kansa saboda har taba tana sha. Masifar da batai masaba a farko ita ta fara zazzaga masa yanzu akan dan mi yasa zaija mota bata bashi iznini ba. Ko sau ɗaya bai nuna yasan ma tanai ba balle ya tanka. Hakan kuma na ƙara fusatata da cimata rai akan al'amarin sa, dan a duniya ta tsani tayi ma mutum abu ya mata shiru, amma shi kulatama bayayi balle ya bata haƙuri kamar yanda sauran masu aiki ƙarƙashinsu ke mata. Suna isa gida tun bai gama tsayawa ba ta fice a motar, cikin gargaɗi ta ce, “Sai nayi maganin wannan zafin kan naka baƙauye kawai”.
      Da kallo kawai ya ɗan bita, sai kuma ya janye idanunsa yana ambaton auziyya saboda yanda skert ɗin yay mata ɗam illahirin surarta na juya kansu. Bayan ya kashe motar ya ɗan ja kusan mintuna biyu zaune shiru abubuwa da yawa na masa kai kawo, ajiyar zuciya ya sauke a hankali yana mai cigaba da ambaton ALLAH tare da buɗe idanunsa dake lumshe har kalarsu ta canja. Ledar nan daya cire a fruit ɗinta ya ɗauka ya fito a motar, kai tsaye ya nufi wajen su maigadi. Suna cikin gaisawa Nazeer autan gidan ya fito. Sai da ya gaishesu dan sukam Mommy tsaye take akan tarbiyyarsu, bata yarda sun raina kowane ma'aikaci ba a gidan duk da wani lokacin su Hussaina kan so ɗaukar hallayar Lulu suce zasu taka ma'aikatan a bayan idonta. Duk kuma randa ALLAH yasa kunnenta yaji ko idonta yaji bata musu da wasa, shiyyasa ma suke shakkar aikatawar. Cikin ladabi Suhaib daya maida hankalinsa garesa ya ce, “Uncle Smart Aunty Lu ce tace na ɗauka leda a mota. Ta kuma ce wai karkaje ko ina yau har sai idan itace tace”.
        Karan farko da al'amarinta ya so fara bashi dariya. Amma sai bai nuna ba ko'a fuska. Miƙewa kawai yay yaje ya Bama yaron ledar data aiko a ɗauka. Wadda ganin bai biyota da ita bane yasa ta fara masifa, da farko ma catai Suhaib ɗin ya kira mata shi, Mommy ce ta hana tace ya amso kayan kawai. Duk rashin mutuncinta tana jin shakkar Mommyn, dan haka ta cema Suhaib ɗin to ya faɗa masa yau kar yabar gidan nan sai da izinin ta. Kai kawai Mommy ta girgiza, a zuciyarta tana tausayin hallayar Mawaddat ɗin, dan tsaurin idonta da izza na bata tsoro. Koba komai ɗiya mace take, komai daɗewa ƙarƙashin ikon wani zata koma. Wanin ma da bata san shi kuma tashi kalar tsagerancin ba.
  
      Koda Suhaib ya kai mata ledar fruit ɗin sama-sama kawai ta cire ta ajiye musu ta shige da sauran ɗakinta. Babu wanda yayi magana sai binta da sukai da kallo kawai. Duk da tana buƙatar wanka hankalinta ba'a can yake ba. Kayan shaye-shayenta kawai take buƙatar ɗan ɗorawa, dan kwana biyun nan da bata sha ba jinta take kamar mara laka a jiki, kuma kamar ana mata susa a brain. Tsaf ta gama zazzage kayan fruit ɗin a ƙasa batare data damu da yanda aka gyara ɗakin ƙal-ƙal ba. Duk da ba wani a cinkushe suke ba haka ta shiga tonawa da mamakin rashin ganin waccan ledar. Da gaske dai babu alamar ledar, dan haka ta miƙe zumbur, bataima kowa magana a falon ba ta fice. Har yanzu yana zaune a wajen su maigadi da sauran masu aikin gidan. Hira suke suna kwasar dariya shiko yana zaune shiru sai waya da yake dannawa, wani lokacin yakan ɗanyi murmushi da hirar tasu musamman idan sun sakosa a ciki. Cikin jan tsaki a zuciyarta ta ce, (Baƙauyen banza sai jin kan tsiya ko ubanwa zaima) dai-dai wajen motar da suka dawo ɗin ta dogare tana faɗin, “Kai!!”. Dukansu juyawa sukai suna kallonta. Shikam ko motsi ma baiyiba balle ya nuna yasan da zuwanta.  
      Baƙin ciki, takaici kamar zasu kashe Lulu. Cikin takaici da izza tace, “Wai kai banzan nan bada kai nake ba”. Yanzun ma shiru bai ɗago ba. Sai dai mai-wanki ya zunguresa da faɗin, “Aliyu da kaifa take inaga”.
          Nan ma shiru yay yaƙi nuna yaji. Dan haka ta nufo wajen a fusace. “Wai kai mika ɗauki kanka? Waye ubanka a ƙasar nan?!!”.
     Idanunsa ya ɗan rufe sai kuma ya buɗesu a hankali. Karan farko ya ɗagosu a buɗe gaba ɗaya ya zuba mata su. Wani irin motsawa zuciyarta tayi, dan wani irin kwarjini da shakkarsa ce ta daki ƙirjinta har zuciyarta na sukur-sukur a cikin jiki. Cikin ƙarfin hali ta watsa masa harara da faɗin, “Dalla malam daina kallona da wannan shegunayen idanun naka uwa na macizai”.
      Bai janye idanun ba, haka kuma bai tanka mata ba dai, sai ma sake tsatstsareta yay da idanun duk da masifar da hakan ke haifar masa shi kansa. Neman daburcewa take, dan tama kasa cigaba da masifar da ke ta mata tuƙuƙi a zuciya. Fahimtar hakan da yay ya sashi motsa laɓɓansa karo na farko da nufin yin magana. Cikin deep voice ɗin nan tasa dake fita da dakewar da nutsuwar fitar da lafazi ya furta, “Duk macen data cika mace mai suturtawace akan kanta koda ga muharramanta ne, hakan kansa ko bata kira daraja gareta ba, darajar kanzo ta risina mata a gaban wanda ya fita ma balle wanda ke a ƙarƙashin ikonta. Wannan gata da musulunci yayma mace har a lafazinta ana so ta zama mai ƙyautatawa akan harshe”. Yana gama faɗa ya miƙe tare da miƙa ma mai-wanki dake kusa da shi key ɗin motar. “Mu kwana lafiya” ya faɗa cikin miƙa masu hannu ɗaya bayan ɗaya sannan ya nufi hanyar gate batare da ya sake ko kallon inda take tsaye ba.
       Babu abinda ta fahimta a kalamansa, sai dai abin mamaki ta kasa koda motsa yatsanta garesa balle maida masa murtani ko yin masifa kamar yanda ta saba har ya fice gidan abin sai kace wani siddabaru.
     “Aunty wani abu za'a ɗakko a motar?”.
    Mai-wanki ya dawo da ita hayyacinta. Kamar wadda aka farkar a barci a zabure ta ce, “Ubanka zaka ɗakko min wawa kawai” ta juya zata bar wajen. Sai kuma ta dawo ta shiga nuna maigadi da yatsa. “Idan har kabar wancan ɗan iskan ya shigo gidannan a gobe a bakin aikinka kaima. Shima kuma ba ƙyalesa nayi ba, sai naga waye ubansa a garin nan, mi kuma yake taƙama da shi? Dan wlhy sai na wulaƙanta rayuwarsa ta yanda ko sunana yaji sai ya saki fitsari a wandonsa”.
      (Ko kuma ke ki saki ba) mai-wanki ya faɗa ƙasa-ƙasa yana danne dariya. A zahiri kam kawunansu a ƙasa babu wanda ya motsa harta isa motar da suka dawo ta buɗe, ko'ina sai da ta leƙa amma babu alamar abinda take nema. Rai ɓace ta nufi komawa dan a zuciyarta ta fara bata *_Ƙwaro_* bai saka mata abubuwan nan bane. Dai-dai tana shigewa motar Uncle Yousuf nayin horn. Da sauri maigadi ya tashi ya buɗe gate ɗin. Fitowar Uncle Yousuf ɗin a motar shi da Smart ya sakasu sakin ajiyar zuciya a tare, a hankali mai-wanki ya saki dariyar da yake ta riƙewa tun ɗazun ganin Uncle Yousuf ya dawo da Uncle Smart ɗin tun ba'aje ko'ina ba. Hakan yasa mai bayin fulawoyi tayasa shima. Sai da sukai mai isarsu sannan mai-wanki ya ce, “Yau fa gamai maganin fitsararriyar nan. Ga kuma Alhaji ƙarami ya dawo da shi tun minti biyar basu cika ba, maga yaya wasan zai kaya. Dan wlhy ya mugun burgeni guy ɗin nan. Ga shi da alama ta tsorata da shi. Ai ban taɓa tunanin anan kusa za'a samu mai maganin masifaffiyar matar nan ba, sai gashi kuwa a cikin waɗanda tafi rainawa da cima zarafi wato mu ma'aikata, dan kawai muna neman guminmu a ƙarƙashin dukiyar gidansu sai take jin mune ƙasar takawarta a duniya”.
        Nisawa maigadi dake kaiwa zaune yayi yana sakin wani ɗan murmushin manya. “Ai ni tun randa yaron nan ya fara zuwa nasan ba kanwar lasa bane ba, dan a cikin idanunsa zaka fahimci shima taƙadarin kansa ne”.
     “Shine dai-dai da ita ai. Wulaƙancin yarinyar nan wanene bamu gani ba. Sau biyu fa tana marina”. Mai-wanki ya faɗa cikin ƙunar rai alamar har yanzu yana jin raɗaɗin marin a zuciyarsa, sai dai babu yanda zai yi...
      Kafaɗarsa mai bayin fulawoyi ya dafa shima cikin ƙunar rai dan ya taɓa shan marin Lulun, “Ai ga mai rama mana nan yazo da ikon ALLAH. Fatanmu dai ALLAH yasa Alhaji Yousuf ya tsaya kan hanata korarsan da tace”.
   “Ai insha ALLAHU bazata taɓa samun wannan damar ba ma. Dan randa ta dawo ashe shi aka aika ɗakkota tai masa halin nata yay tahowarsa ya barta acan, kamar dai yau ɗin nan da ya manna mata hauka, amma Alhaji Yousuf ɗin yaje ya dawo da shi aiki matsayin ma drivern ta, kaga ko da ace dane ai tun ranar zata koresa bayan taci masa zarafi kamar yanda takema na baya ko, kuma ya koru ɗin kenan. Nima a wajen Mubeen naji yana labartama yayansu Husain ta waya jiya”.
        “Ai Alhaji ƙarami yana birgeni wlhy”. Cewar maigadi. Haka suka cigaba da gulmar Lulu da a gabanta to tari basu iyawa bare satar kallonta..........✍️



_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥



*_ALLAH ya gafartama iyayenku😭🙏_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲




  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗



           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻


𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣8️⃣



.........A ɓangaren Lulu kam sosai ta haukacema ƙwaro ta waya da masifa shiko ya dinga rantsuwar ya saka mata. Har abokinsa da yay komai a gabansa ya bama wayar ya zame masa sheda amma taƙi yarda. Sai ma katse kiran tai da tabbatar masa sai ya san ita ya cuta wlhy... Gado ta faɗa zuciyarta na mata wani irin tafasa, babu abinda ke mata kai kawo a rai irin maganganun drivern ta, haka kawai zuciyarta ke ingizata akan son sanin ma'anarsu. Wayarta data yasar gefe ta jawo. Nadeeya ta kira, ana ɗagawa daga can Nadiya ta fara da faɗin, “Bastie dama fa yanzu zan kiraki, dan gama wayata da Gajere kenan yace za'a samu kaya a wajen ogansa kona mil. ake s.....”
       “Kinga ni ba wannan ba...”
    Ta faɗa cikin katse Nadeeyar.
“Oh to ina saurarenki, na jiki kamarma cikin ɓacin rai, miya faru kuma? Badai driver ɗin ba kuma?”.
      “Komai ma ya faru, har ma abinda banyi zaton faruwarsa ba ya faru. Wani Hausa nake son ki fassara min”.
   “Tofa! Wane Hausa kuma?”.
Batasan ta haddace abinda ya faɗa matan ba sai da ta zayyanosu tsaf a yanda ya faɗesu babu ko gargada. _“Duk macen data cika mace mai suturtawace akan kanta har akan muharramanta, hakan kansa ko bata kira daraja gareta ba, darajar kanzo ta risina mata a gaban wanda ya fita ma balle wanda ke a ƙarƙashin ikonta. Wannan gata da musulunci yayma mace har a lafazinta ana so ta zama mai ƙyautatawa akan harshe”._
     “Woow Madam irin wannan kalamai haka kamar wata mai tsara baitikan waƙe, dan ALLAH waya shiryasu haka....”
    “Mtsoww malam dilla fassararsu nake buƙata nace”.
    “Oh sorry, tab wlhy fa kalaman sunyi tsauri, ni kaina ban san yanda zan fassarasu ki gane ba dan hausan ba gama isata yay ba. Amma ina zuwa bari na tambaya”.
         Tana ƙoƙarin ajiye wayar cikin jan tsaki Suhaib na mata knocking. “Uwar miye?”. Ta faɗa cikin masifa. Cikin tunzura baki Suhaib da ke da ga ƙofa dan bai shiga ba ma ya ce, “Uncle

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login