Showing 30001 words to 33000 words out of 163036 words
Yousuf ne yazo, ya ce kizo” da ga haka yay wucewarsa.
Tana son Uncle Yousuf matuƙa, tana kuma girmamashi saboda wasu dalilai nata na kanta. Dan haka tace ma Nadiya tana zuwa ta yanke wayar. Da mamaki mai nuna ɓacin rai take duban Smart da ke zaune a ƙayataccen falon nasu kusa da Uncle Yousuf. “Mi wannan abun yazo yimana nan Uncle You?”. Ta faɗa tana nuna Smart da ke zaune babu alamar ɗari-ɗarin nan irin na ma'aikaci da iyayen gidansa a tare da shi. “Ni na kirawoshi” Uncle Yousuf ya bata amsa cikin ɗaure fuska. “Uncle nifa bana buƙatar sake ganinsa” ta faɗa itama a harzuƙe.
“Da yay miki mi?”.
Baki ta tura gaba cikin kumbura fuska ta ce, “Wlhy na tsanesa, har ni wannan mutumin zai zaga. Korar ma da nai masa yanzu ba'ita kenan ba Uncle, ya jira hukuncin da zai biyo bayanta. Har ni zaima banza ina masa magana, sannan ya biyoni da baƙaƙen maganganu a gaban su maigadi, har shi waye? Mi yake jin kansa? Ɗan u......”
Hannu Uncle Yousuf ya ɗaga mata, “Ya isa haka. Mawaddat wai yaushe zakiyi hankali ne dan ALLAH. Yanzu abinda kike yi ko su Suhaib ƙannenki zasu aikata ne? Ke kullum cikin korar mutane. Yanzu dai ina son ki nutsu ki kwantar min da hankalinki, dan shiyyasa ma na dawo da shi gidan a yanzu dan na haɗu da shi a hanya ne. Ban kawo Aliyu gidan nan dan ki koresa ba, zan ƙara jaddada miki a yanzu shi ɗin zai dinga kaiki duk inda kike so dan saboda ke kaɗai ma na ɗaukesa aiki. Zai zo ƙarfe bakwai da rabi saboda takwas kike fita aiki, zai dawo da ke ƙarfe biyar da rabi kamar yanda kike dawowa shike nan ya tashi sai kuma washe gari period na gama magana.”
“Amma Uncle....”
Hannu ya ɗaga mata alamar baya buƙatar ta sake cewa komai, rai ɓace tabar wajen kamar zata fashe dan haushi. Da ga haka ya juya ga Smart da ke zaunensa a yanda ta shigo ta samesa batare da yabi takanta ba. “Wannan shine lokacin zuwanka aiki da tashin ka. Amma weekend zaka iya zuwa da ga goma zuwa huɗu sai ka tashi. Zan baka duka tsare-tsaren fitarta a rubuce, sai kuma idan zuwa wani waje ya kamata kasan aikinsu yana sakasu ɗan yinan-yinan koba shiri. Dan ALLAH ka ƙara hakuri, al'amarin Mawaddat sai addu'a, ga yanayin da take ciki na ƙara kangarar da ita. Kai tsakaninku ma akwai cigaba, dan naga alamar tana shakkar ka sosai”.
Karan farko ya saki ɗan murmushi da shafa kansa. “Alhaji wane tsoro kullum ana zageni da kirana illiterate ko villager. Kawai dai zanyi haƙuri domin mutuncinku da ceto rayuwarta, dan koba komai nima inada ƙanne mata, ina son kuma ALLAH ya karemin su a duk inda suka shiga.”
“Gaskiya ne wannan Aliyu. Ina godiya matuƙa a gareka da sake baka haƙurin di. Yanda ALLAH ya haɗa wannan zuminci a tsakaninmu ALLAH yasa muci moriyarsa har a gidan aljanna. Amma ina son naji wannan kalamai da aka faɗama yarinyata haka har suka harmutsa min ita, duk da nasan abu kaɗan ma fusata Mawaddat yake”.
Murmushi Smart ya sake yi a karo na biyu da faɗin, “A Alhaji ai ba'ayi haka ba. Tunda ya wuce a barsa kawai sai na gaba idan ALLAH yasa za'ayi a gabanka, duk da ina tsoron kuma karta kwaɗa min mari dan yau ma dai da ƙyar na sha shiyyasa ma na gudu”.
Dariya sosai Uncle Yousuf yake kwasa da faɗin, “A lallai ka tsira da ƙyar, dan a ma'aikatan gidan nan ɗai-ɗai ne basu sha marin Lulu ƙamshi ba kam”.
“To kaji ko Alhaji. Bara nayi nan kafin ta sake fusatowa ma, nasan yanzu bai zama lallai na sha ba”.
Dariya Uncle Yousuf ɗin ya sake kwashewa da shi, shi kuma ya fice yana ɗan murmushinsa mai sanyi, har ga ALLAH yana ganin mutunci da kimar Uncle Yousuf, yaji kuma zai iya haƙuri da yarinyar kodan shi ɗin. Mutum ne da yasan daraja da kimar mutane, duk yanda kake baya wulaƙantaka ko nuna maka ɗagawar shi ɗin wani ne. Ya iske har lokacin su maigadi na gulmar Lulu, ganinsa baisa kuma sun daina ba sai ma kwarzantashi da suka shigayi akan abinda yaymata. Komai baice musu ba sai kansa da ya ɗan girgiza kawai ya ciro wayarsa ya fara sana'ar tasa, ba kuma wani abu yake a ciki ba face game ɗin ball.
Bayan kamar awa ɗaya Uncle Yousuf ya fito zai wuce gida, Lulu ce tai masa rakkiya har wajen motarsa, aiko ta dinga antayama Smart da bai san tanayi ba harara. Dariya Uncle Yousuf ya dingayi ƙasa-ƙasa, dan sarai ya lura da ita, sai dai baice komai ba yayma su maigadi alheri kamar yanda ya saba. Godiya da addu'a suka shiga kwararo masa. Murmushi ya dinga musu kawai, dan harga ALLAH yana jin matuƙar daɗin addu'oi nan nasu. Duban Lulu da keta faman yamutse fuska yay, cikin tsokana ya ce, “To Daughter kin bani aron drivern naki ko na tafi da shi”.
Fuska ta sake kwaɓewa da faɗin, ni nama bar maka Uncle You, Dan bana buƙatarsa sai shegen girman kan tsiya”.
Dariya yayi, yana mai kiran Smart dake zaune kansa ke ƙasa. “Shiga muje” kawai yace masa. Bai musa ba ya raɓa ta gaban Lulu dake faman binsa da kallon banza, ciki-ciki ta furta, “An samu motocin banza sai hawa ake”.
“Ko ke kika zama mota hawa zanyi”. Ya faɗa shima a ƙasa-ƙasa lokacin da yake shigewa cikin motar.
“Kai ɗin banza! Shashasha!”
Ta faɗa a zafafe har tana zaburowa. Wani shegen murmushi ya sakar mata a karon farko yana ɗan ƙara gimtse fuskarsa kamar bashi ya furta ba ya shige motar abinsa. Wayyo ba'a taɓa Lulu ba ma ya aka ƙare balle. Dariya sosai Uncle Yousuf yake yi, dan ya fahimci akwai abinda ya faru duk da Smart ɗin ya fuske abinsa kamar bai aikata komai ba. Har yaja motar suka fice bata bar masifar ba.
“Na kula dai kai kake fara kunna min yarinya ka noƙe”. Uncle Yousuf dake dariyarsa har yanzu ya faɗa dai-dai yana harba motar saman lafiyayyen titin anguwar. Kaɗan Smart ya shafo kansa yana ɗan murmushi batare da yace komai ba. Sai da sukai ɗan nisa ya zaro ledar da ya cire a cikin kayan fruit ɗin Lulu. Buɗeta yay, tarin ƙwayoyi kala-kala suka bayyana. Motar neman ƙwacema Uncle Yousuf ɗin tayi, da sauri ya gangara gefen titi cikin rawar harshe ya furta, “Wannan fa Aliyu?”.
Cikin damuwa da ɓacin rai shima ya bashi amsa da, “Fitar da mukai ɗazun abinda muka fara tsayawa akai order kenan a wajen wasu masu fruits kafin mu ƙarasa inda tace zataje”.
Sosai jikin Uncle Yousuf ke rawa, dan har ga ALLAH shikam bawai bai yarda da maganar Doctor Khalifa bane, kawai dai rashin ganin al'amarin a zahirinsa ya sa bai kai masa ƙololuwa a rai ba, shiyyasa ma ya ɗora Smart ɗin dan ya samu tabbaci. Kamar wanda ya shiga ɗimuwa ya sake furta, “Aliyu Hydar! Ka tabbata a jikinta ka samu waɗan nan ƙwayoyin?”.
Cikin salon dakewar nan tasa da rashin son magana ya ɗan ɗage kafaɗunsa da faɗin, “Yaah! A gabana ma aka saya”.
“Dolene na saka a kama yaron nan dake sayar mata, bara ma na kira CP....”
Da sauri Smart ya dakatar da shi. “Niko a nawa shawaran Alhaji kamar kama yaron ba shine mafita ba tun a yanzu. Domin inaji a jikina ba dashi kaɗai take huɗɗa ba. Dan ka saka an kamashi kamar ka fargar da itane ta sake sabon salo ita da abokan mu'amalarta. Kaga kenan ba hanyar da zamu rabata da al'amarin muka ɗakko ba kenan, dan yanzu aka fara wasan kamar”.
Sosai maganarsa ta shigi Uncle Yousuf ɗin, dan haka ya ɗan dakata da ga ƙoƙarin kiran cp da yake shirin farawa, sai dai idanunsa sun kaɗa jazur harda ƴar guntuwar ƙwalla a cikinsu. Shiru babu wanda ya sake magana a motar har kusan mintuna huɗu, kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa.. Shine ya kashe shirun nasu da furzar da iska mai zafi. “Alhaji ni zan wuce, dan yamma nayi gashi ina son na isa gida da wuri”.
Cikin damuwa ya gyaɗa masa kai batare da ya iya furta komai ba har sai da ya fita yana ƙoƙarin rufe ƙofar motar ya kira shi a hankali. Ɗan duƙowa yay yana amsawa, Uncle Yousuf ya miƙa masa kuɗi masu yawa. Kansa ya girgiza da faɗin, “Kayi haƙuri Alhaji, tun farko na faɗa maka kada irin haka ya dinga shiga tsakaninmu. Hakkina kawai nake buƙata a kowane ƙarshen wata kamar yanda mukai alkawari. Na barka lafiya”.
Ajiyar zuciya mai ƙarfi Uncle Yousuf ya sauke ta re da sakin ɗan murmushi yana mai binsa da kallo. Tabbas a girme yasan zai iya bama Aliyun shekara bakwai. Amma dattako da kamunkan yaron na sakashi jin ya cika masa ido tamkar wani babba garesa. Wata irin kima da kwarjini yake masa a zuciya da cikin udanu. Yana matuƙar son ganin mutumin da yasan ciwon kansa a rayuwa da riƙe mutuncinsa. Ya yarda ya nema halak ɗinsa koda za'a kallesa a mai riƙe da sana'a mai ƙasƙanci, amma bai yarda ya ƙasƙantar da kansa ba wajen a bashi ya amsa balle zuciyarsa ta mutu. Insha ALLAHU zai taimaki rayuwarsa.........✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenku😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣9️⃣
........Smart kam tuni ya shanye titin layin zuwa babban titi, da ƙyar ya samu napep. Tafiyar da bata wuce mintuna talatin ba ta kawosa anguwarsu. Kasancewar da sauran hasken gari koda ya shiga sai ya ɗan watsa ruwa tare da zuwa ya gaida Abba da su Ammah, sai dai ya iske Ammah ma ta fita ita da aunty Amarya Barkan ƙanwar Aunty Amaryar da ta haihu a can Gadon ƙaya tun la'asar, sai su Maryam kawai da suka dawo islamiyya. Dan haka bai zauna ba suna gama gaishesa ya fito ya koma ɗakinsa. Ba wasu abokai ne da shi ba shi dama sai Ahmad kuma ba anguwar yake ba. Dan Mutum ne mai ƙarancin kwaramniya. Idan kaga abokinsa da har zasu iya zaman doguwar hira to sai dai abokan karatunsa, amma na cikin anguwa sai gaisuwar mutunci kawai, duk da dai a da anyi abotar yarinta, sai dai kasancewar sa mara sakewa da mutane suke masa kallon mai girman kai duk suka janye jikinsu da shi, shi kuma bai nuna ya damu ba. Abokan karatun kuwa akan jima ma ba'a haɗu ba sai ta waya ko wani taro mai muhimmanci ya haɗa. Shiru ya kwanta kamar mai barci, da gani kasan duniyar tunani ya faɗa, dan babu abinda yake sai furzar da huci akai-akai da ga bakinsa, hakan kamar ɗabi'a ce data zame masa jiki in dai yana cikin damuwa.. Abubuwa ne masu yawa ke ci masa rai, ciki harda batun bauɗaɗɗiyar yarinyar can, shi mutum ne da baya shiga sabgar da ba tashi ba koda kuwa a cikin gidansu ne sai idan yaso, amma sai yake ji zuciyarsa na ingizashi akan taimakon ubangidan nasa da yarinyar, badan komai ba sai dan ƙannensa mata da bazai taɓa fatan su tsinta kansu a irin wannan rayuwar ba. Yasan idan har ya tsamota da ga wannan musifar yayi jihadi, sai dai bai san ta ina zai farama taro wannan al'amari nata ba. Karan farko yaja sirrin tsaki, sai kuma ya tashi zaune yana ɗan furzar da huci tare da kai hannunsa saman goshinsa yana ɗan murzawa. Ganin yaƙi samun nutsuwar hutawar da yake buƙata ya sashi tashi ya fito a ɗakin, nan ƙofar gidansu ya zauna yana ɗan gaisawa da mutane masu wucewa har akai kiran sallar magrib. Bai fito da ga massalacin ba sai da akai isha'i, yana kwaɗayin shiga gidan suyi hira da Ammah dan wannan ɗan lokacin kawai yake da damar haka gareta, amma zuciyarsa nata masa tuni akan Lulu da abinda yaji suna magana ita da ƙawarta zasuyi a daren na yau da sunan wai murnar samun lafiyarta. duk yanda yaso yaƙar zuciyarsa abin ya gagara, saboda yana ji a ransa ba alkairi za'a shuka ba wajen, dan haka ya fito da ga layinsu ya samu Napep zuwa hotoro gra. bai damu da kuɗin da suka tsuga masa ba. Ɗan nesa da gidan ya sauka, amma ya tsayar da mai napep ɗin, ya samu jikin wata bishiyar dabino kusa da katangarsu ya tsaya, ya kai mintuna talatin da wani abu a wajen yaji motsin an buɗe gate ɗin gidan, ido ya zuba na son ganin wanda zai fito. Ilai kuwa Lulu ce, dan a kanta idanunsa suka sauka saboda haske dake tako ina a street ɗin, gashi ta sauke glass ɗin motar sosai har kana iya hango kalar kayan da take sanye da su. Tayi ƙyau matuƙa ga uban ƙamshinta na isowa har inda yake tsaye saboda yanda ta gumbuɗashi kamar ba mace ba. A ɗan kasancewarsu na kwanaki ya fahimci sam bata tausayawa ƙamshi, haka kawai sai yaji tanan ɓangaren ta ɗan samu sassauci a garesa, duk da tana saka nata ƙamshi ne ba bisa ƙa'idar da ya kamata ace mace ta saka ba. Da sauri ya ƙarasa ga mai napep da ke zaman jiransa. “Kabi wannan motar Please, amma karka bari ta fahimci muna biye da ita”. Ya faɗa yana nuna ma mai napep ɗin motar Lulu da ke tafiya a hankali kamar bata son tuƙin yau. Yanda take tafiyar ya bama mai napep ɗin damar binta cikin hikima har zuwa wata sabuwar anguwa, dai-dai wani gida da alamu suka nuna shima ba'a daɗe da kammalashi ba ta tsaya, da ga inda suke yana hangen yanda ta kai waya a kunnenta alamar kira take ko an kirata, tana ajiye wayar ana buɗe gate ɗin gidan. Da sauri ya fita tare da miƙama mai napep kuɗi yana faɗin, “Abokina nagode ko”. Bai jira amsarsa ba ya nufi gidan, kasancewar akwai ƙarancin haske a anguwar dan kamar ma basu da wuta sai ƙarar gen... Ɗin gidan data shiga yake jiyowa ya samu damar bin motar tata ta gefe suka shiga tare batare da mai-gadin ya lura ba. Motoci ne kusan bakwai a gidan duk an parker a babban compound ɗin kamar wasu masu biki, tun kafin ta fito a motar ƙawayen nata suka baibayeta da ihun faɗin, “Sai Lu ɗin mu!!!, sai ƙamshin mu!!!”.
Fuskarta ƙawace da wani shegen murmushi ta fito. Wani shegen gown ne a jikin nata ta lafe mata kamar babyn roba. Da sauri ya kauda idanunsa yana mai jan sirrin tsaki da taune lips ɗinsa da ƙarfi. Bai sake kallon inda suke ba har suka shige ƙofar da yake ƙyautata zaton ta cikin gidan ce. Huci mai zafin gaske ya furzar tare da gyara tsaiwarsa. A ɓangaren su Lulu kam suna can cikin ƙaton falon gidan da ya sha kayan alatu. Abinda zai baka mamaki bawai iyakar su kaɗai bane ƴammatan ashe, akwai dattijan maza a shekaru bawai a cikar kamala ba har su huɗu, tun shigowar su Lulu kusan su duka suka zubo mata idanu fuska a washe, yayinda ita kuma nata murmushin ya ɗauke ta wani yamutse fuska tana kallon Nadiya, sai kuma ta juya ta fito a fusace. Da sauri Nadiya tabi bayanta tana faɗin, “Please Lu ki saurare ni.”
“Anƙi a saurareki ɗin, Nadiya kin san dai na tsani irin wannan ko...?”
“Na sani, amma bamu da wani zaɓi ne wlhy Lu.., dan ALLAH ki fahimce ni, kin san dai bazanyi abinda zai ɓata miki rai da gangan ba....”
“In ba kinyi da gangan ɗin ba miya kawo waɗan nan tsoffin banzar nan? Ni ban hanaki huɗɗa da su ba, amma ki sani duk randa suka zubar da ke bayan gama lalata miki ƙuruciya kiyi kukanki ke kaɗai kar ki tunkareni. Amma ki daina sakamin su a sabgogin rayuwata”.
Ɗan murmushi Nadiya tayi cikin rashin ɗaukar zancen na Lulu da muhimmanci ta ce, “Naji, ni dai yanzu kiyi haƙuri mu koma ciki dan ALLAH. Dan wannan fa zaman naki ne, dan ke akayisa, mun riga mun gama tara mutane, su Shony fa tun daga ktn suka taho a yammacin nan domin wannan shagali kawai. Abinda yasa ki ka ga su Alh. Baita anan ma saboda su Shony ne, dan sun riga sun kirasu cewar zasu shigo Kano, amma wlhy badan ke bane ba”.
A hankali ta furzar da iska, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya. “Shike nan amma ki kiyaye gaba, dan in har kika sake sakamin sabgar waɗan nan mutanen a tawa wlhy sai mun rabu. Suma su Shonyn idan suna buƙatar haɗuwa da su ne suje can su haɗu bai shafeni ba”.
“Naji na yarda baza'a sake ba. Suma kuma zan musu bayani yanda zasu gane Muje to dan ALLAH suna jiranmu”.
“Bani details ɗin mai kayan nan na tura masa kuɗinsa karna shiga wata sabgar. Sannan wannan gidan na waye uwar kwashe-kwashe kika kawo mu kuma?”.
Gidan Nadiya ta kalla tana ƴar dariya tare da faɗin, “Gidan wanda ya sayar mana da kayan ne, wlhy Guy ɗin akwai kirki gashi so handsome kuma, ya bamu shawara ne muzo nan musha shagalinmu dan zaifi mana sirri kasancewar kinga dare ne, ke kuma ba cika son shiga clubs na nan Kano kikai ba kin ce ƴan hayaniya da ƴan iska sun cika yawa”.
Cikin rashin damuwa ta ɗage kafaɗa kawai, batare da ta sake tofa komai ba ta bar wajen. Binta Nadiya tai suka shige