Showing 162001 words to 163036 words out of 163036 words
dan na tsani gidan nan da komai na cikinsa. Wlhy idan na cigaba da zama komai zai iya faruwa”.
“Ki kwantar da hankalinki Mawaddat. A cikin wannan halin da kike ai wannan gidanne yafi cancanta da ki zauna fiye da ko ina. Karki ruɗar da kanki, domin yau ɗinki tanada banbanci da jiyanki. Aliyu mijinki ne, abinda ya faru tsakaninku kuma yanada banbanci da wanda zuciyarki ke kallo a baya. Bawan ALLAHn nan tun jiya hankalinsa a tashe yake da ganin halin da kika shiga, bana jin ko rintsawa yayi a daren jiya, dan ALLAH ki sakama ranki haƙuri ku fuskanci juna wataran zakiyi alfahari da hakan”.
Kuka Lulu ta sake fashewa da shi tana mai girgiza kanta, “Aunty dan baki san miya faru bane....”
“Ba sai na sani ba Mawaddat, ki adana wannan sirrinkine. Ni dai fatana ki kwantar da hankalinki ki saurari mijinki. Aliyu mutumin kirkine fiye da yanda kike zato ko tsammani. Ke da kanki zaki bama wani labarin hakan wata rana...”
“Aunty shi azzalumi ne, macuci ba mutumin kirki ba. Kuma wlhy saina ɗan ɗana masa fiye da abinda ya ɗanɗana min, ni zai yaudara ya sakama disere tablet acikin abu na sha ya min fyaɗe. Natsanesa aunty, bana son sake ganin fuskarsa a rayuwata. Kuma wlhy sai na shayar da shi mamaki, dama sai da Dada ta faɗamin amma na kasa fahimtarta. Yayi hakane saboda yasan gobe zamu rabu. Bazan yafe masa ba, kuma a yau ɗin nan komai ma ya ƙare, ya kuma saurari abinda zai biyo baya”.
A bazata suka tsinkayi deep voice ɗinsa cikin kunnuwansu dan basu san da shigowarsa ɗakin ba. “Ni ban saka miki komai kisha domin samun biyan buƙatata ba. Sannan aure nayi kamar kowane aure mai daraja da fatan mutuwa ta raba. Amma kiyi haƙuri ki bani dama na miki bayani maybe ki fahimceni kuma ki yarda” ya ƙare maganar yana ajiye tray ɗin hannunsa mai ɗauke da kofin shayi da plate da aka saka soyayyan ƙwai.
A zafafe Lulu dake masa wani irin kallo na tsantsar tsana tace, “Har abada babu yarda a tsakaninmu. Baka da abinda zaka fahimtar da ni Munafuki, azzalumi, maƙaryaci, mayaudar...”
“Mawaddat!!”.
Aunty Khadijah ta kira sunanta cikin daka tsawa. Yayinda Smart ya lumshe idanunsa har cikin rai kalmomin guda huɗu da suka fito da ga bakinta na ratsa shi. Ƙoƙarin matsawa yay gaban gadon da kofin shayi a hannunsa yayinda aunty Khadijah ke cigaba da mata faɗa. Bai gama tabbatar da takai maƙurar tsorata da shi ba sai da yay ƙoƙarin riƙota tai wata irin zabura, sai dai azaba da rashin isashen ƙarfi ya sata kasa yin kowane irin yunƙuri face sake fashewa da kuka ta furta, “NA TSANEKA ALIYU!!”.
“INA ƘAUNARKI MAWADDATAN'WARAHMAH”. ya amsa mata da tashi disashshiyar muryarsa yana tsayawa cak, kofin shayin ya ajiye a bed side drawer duk tausayinta sai ya sake mamaye masa zuciya. So yake tai haƙuri ta kwantar da hankalinta ya jera mata kalaman yabo da jinjinar ban girma, sai dai yasan bazasuyi tasiri ba a yanzu gareta, dan haka ya tattarasu ya adana a wani killataccen sashin adana manyan sirrikansa a zuciya.
Ganin Lulu na neman sake rikice musu aunty Khadijah tace yaje falo ya jirata. Kusan mintuna biyar da fitar tasa sai gata ta fito. Kallonsa tai cike da tausayawa. “Kayi haƙuri Aliyu ba laifinta ban itama. Wlhy gaba ɗaya a ruɗe take. Dan ma a hakan fa jiya an taimaka mata da wuri shiyyasa al'amarin yazo da sauƙi. Ni yanzu ina ganin mafita ɗaya ce, ka samo wadda zasu zauna tare, sannan dole kayi haƙuri na samu ko Maman Ra'is ce (Aunty Saliha) tazo ta ƙara lallashinta. Dan yanzu ni zanje asibiti ne inada theatre. Insha ALLAH komai zai dai-daita da zarar ta daina jin raɗaɗin a ranta. Sannan ka ɗanyi nesa da itan na ɗan lokaci koda yinin yau ne haka zuwa gobe”.
“In sha ALLAHU aunty Khadijah. Nagode sosai da ƙoƙarin ki kuma”.
Sosai aunty Khadijah taji daɗin yanda ya fahimta ɗin. Yayinda tausayin Lulu ke cigaba da ratsata itama harma da shi kansa Smart ɗin. Dan yarinyar tana cikin wani yanayi ne mai ban tausayi. Bayan wucewarta ɗaki ya nufa ya canja kayansa, koda ya fito sai yay tunanin bari ya ɗan leƙata kafin ya wuce, dan gidansu yake son zuwa ya ɗakko mata Maryam ko Asma'u. Kamar zai fice sai kuma dai ya nufi ɗakin nata, ya samu tana toilet, sai books guda buyu da ya gani a saman gadon da pen. Juyawa yay ya fita saboda so yake yaje ya dawo da sauri. Maganar aunty Khadijah na cewar zatai magana da Aunty Saliha tazo yasa shi bai rufe gidan ba, dan yasan sun fisu kusa da nan zata iya yiwuwa ta iso kafin shi ya dawo.. Da'ace bawa yasan gaibu ko abinda zai iya faruwa a bayansa da Smart bazai yi wannan fitar ba. Da bai bar ƙofar gidansa a buɗe ba. Da ya bari har aunty Saliha ta iso kafin ya tafi.......✍️
*_Tofa masu karatu. Mizai faru? Mike shirin faruwa? Amsoshin na a FURAR DANƘO book 2 in sha ALLAHU 👌_*
_Kumin afuwa wannan karon rubutun duk yazo a yanayi na shiririta sai dai godiyar ALLAH. Yau da gobe kenan dan na fiku son naga na kammala gaba ɗaya😭. Amma in sha ALLAH muna gab da hutawa baki ɗaya. Zamu koma part 2 ne dan in numbers na nisa rubutun gundurata yakeyi wlhy🤦. Amma insha ALLAHU zamu ƙarƙare akan lokaci._*
_Akwai ƙura fa ta gaske a book 2, dan duk wani abinda muke san sani na ƙunshe ne a cikinsa. Kudai kuyi addu'a ALLAH yasa mu koma pages goma goma mu kammala a kwana goma. Kun san fa ina matuƙar son goma😂😂._
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*