Showing 126001 words to 129000 words out of 163036 words
ma bazai yi haka a yau ba zan dawo gida idan kwanakin da akai yarjejeniyar sun cika ya sakenin, zan iya ɗaukar komai amma banda kan aiki na, domin shine rayuwata, shine farin ciki na, shine mafarkina, shine babban burina tun kafin nasan kaina, shi waye da rana tsaka zai datse hakan da tunanin nuna gadara ko ƙarfin ikon abinda bashi da ikon!”.
“Mawaddat aure kona kwana ɗaya ne sunansa aure, da auren nan baida kimar da za'a kirasa ko kwallonsa da wannan martabar da muhimman mutane basu taru cikin shigar kamala domin ɗaurashi ba. Da wasu mutane basu ajiye muhimman ayyukansu ba domin halartarsa. Ki kwantar da hankalinki komai ya tafi cikin tsarin da muke fatansa, Aliyu kuma zanyi magana da shi duk da nasan shima ba son hanaki aikinki yake gaba ɗaya ba tunda ya sanar miki next week zakiyu resuming be a good girl mana sweetheart, maybe ma yana tsokanarki ne dan yaga yaya zakiyi. Dan haka ina son ki zama jaruma mana kamar yanda ya sanki.....”
“Amma Uncle fitan yanada muhimmanci fa yau. Kasan inada case ɗin yarinya da ke aibiti, tun juya kuma ya kamata naje na shigar da case ɗin court”.
“Kar ki damu indai wannan ne yanzu zan fita ni zanje da maman yarinyar mu shigar da ƙaran, ke kuma sai ki cigaba da shirinki matsayinki na lawyer ɗin nata hakan yay miki ko?”.
A hankali ta ce, “Eh”.
“Yauwa ɗiyar albarka na. Ki daure kinji, kar Aliyu ya samu na tsokanarki, bamma so ki bari yaga hawayen nan, maza ki sharesu ki zauna kurum kamar ba'ai komai ba Kinga kinyi winning”.
Ta gamsu da zancen nasa ɗari bisa ɗari, dan dolene itama ta mannama velleger ɗin can haukan da sai ya gagara barci a yau. Da ga haka ta miƙe bayan sunyi sallama da Uncle Yousuf da ke dariya daga can ta nufi bedroom. Fuskarta taje ta wanko da canja kayanta zuwa wando da riga marasa nauyi na zaman gida, ta sake dawowa falon ɗauke da laptop ɗinta. Dai-dai nan ya fito shima, alamunsa sun nuna yay wanka dan sanye yake cikin ƙananun kaya da sukai matuƙar amsarsa sai ƙamshinsa mai sanyi da ke tashi. Zaune ya kai idonsa a kanta sai dai fuskarsa babu walwala, duk da taji motsin nasa ko sau ɗaya bata nuna alamar hakan ba balle ta ɗago, lap-top ɗinta kawai take ƙoƙarin kunnawa. Shi kuma sai ya tsira mata idanun nan nasa na macizai da take kira, ƙin ɗagowar tata bai hanata jin kaifin idanun nasa a kanta ba, amma ta dake ta cigaba da abinda take yi.
“Break fast fa?”.
Ya faɗa a dake still dai idanun nasa a kanta. idan kujerar da ya ke zaune ta motsa to itama ta motsa. Cije lips ɗinsa yay yana wani sake ƙanƙance idanunsa a kanta. Kusan minti ɗaya yana kallon nata kafin ya miƙe tsam zuwa inda ta ke, lap-top ɗin ya ɗauke da ga jikinta ya ajiye gefe, karon farko ta ɗago ta kallesa da idanunta da suka kaɗa saboda kukan da tayi, fuskarta na nuna matuƙa ranta a ɓace. Nunawa yay kamar baiga kallon da take masan ba, kafin ta furta abinda ke bakin nata ya kwasheta gaba ɗayanta a cikin hannunsa yayi sama da ita kamar wata ƴar baby, (🤣dama abu ba abu ba sai masifa).
“Bana son wulaƙanci malam miye haka? Dalla sauke ni”. Ta faɗa cikin matsanancin ɓacin rai tana kai masa ƙananun duka a ƙirji, amma ko gezau kansa tsaye ya nufi hanyar kitchen da ita, saman cabinet ya direta, ya juya ya sakama ƙofar key. Dai-dai ita kuma tana dirowa da ga inda ya ɗauratan ta iso ga ƙofar. Wani shegen kallo ta watsa masa da faɗin, “Matsa min”.
“Idan kinyi abinda nace kenan”.
Ya faɗa cikin halin ko'in kula yana saka key ɗin cikin aljihun wandonsa da jingina da ƙofar yana mai harɗe ƙafafunsa waje guda. Ƙarshen ɓacin rai Lulu ta gama kaiwa, dan haka cikin kaushin murya ta ce, “Kasan na iya fiye da abinda kake tunanin ka'iya na rashin mutunci ko. Aliyu! Ka buɗe ƙofar nan ka bani hanya na wuce kafin na saka dana sanin sani na”.
Jikin ƙofar ya bari da ɗan taɓe baki batare da yace komai ba ya nufi frizzier ɗin da ke kitchen ɗin ya buɗe, sai da ya ƙarema kayan ciki kallo sannan ya rufe ya nufi store. Daga sama har ƙasa yake bin store ɗin da aka tsatstsage da kayan abinci kala da iri da kallo shima, har da su doya da airish da ruwa da kayan miya da akaima ajiya irin wadda bazasuyi saurin lalacewa ba. Shi sai abin ma ya so bashi mamaki da dariya, to su da suka jibge waɗan nan kayan matar gidan ta iya abinci ne?....
Shigowar Lulu a fusace ya saka tunaninsa yankewa, ya juyo gaba ɗayansa yana dubanta, huci take sosai idanunta sun juye gaba ɗaya har wani tara ƙwallan masifa sukeyi. Gashi yanda yaga sun ɗan kumburo tun ɗazun ya fahimci kuka tayi, yaji ba daɗi a ransa, dan sam baya son ganin wani ya shiga damuwa a dalilinsa, sai dai dolene yay abinda yayin dan ya fahimtar da ita da da yanzu ba ɗaya bane, yanzu komai sai da izini... Da sauri ya dubeta jin tana ƙoƙarin saka hannu a aljihunsa alamar son zaro key. Hannun nata ya riƙe yana ɗan waro idanu waje, duk yanda taso fisgewa bai sakar mata ba sai da ya zare key ɗin da ga aljihun nasa, sai kawai ya maƙalashi jikin belt ɗinsa ta inda yasan bazata ce zata ɗauka ɗin ba yana sakin wani shegen murmushin mugunta. Da sauri ta ɗauke kanta da ga dubansa gaba ɗaya tana jin kamar ta fasa ihu, a zuciyarta kuwa tace (ɗan iska).
“Yanzu mi zaki dafa mana? Dan yunwa nake ji nikam ga shi nace su Ammah kar su ƙara aiko abinci injiki.”
Harara ta watsa masa cikin gatsali ta ce, “Ashe zaka mutu da yunwa kuwa a gidan nan”.
“Zadai mu mutu, dan kema dai duk tsiya dole ki nema ai. A yanzu ma haka idan kina son fita da ga kitchen ɗin nan ki nema mana abinci, inba hakaba ALLAH anan zamu yini”. Ya ƙare maganar yana fitowa da ga store ɗin. Ɗaya da ga cikin kujeru huɗun da aka sakama table a tsakkiya yaja ya zauna. Hankalinsa kwance ya jawo wayar ya fara buga game ɗin ball, ya kuma ƙure ƙarar yanda ta cika kitchen ɗin da hayaniya. Lulu data gagara fitowa a store kanta ta dafe, sai faman haɗiyar rai take zuciyarta na ƙuna. Ta rasa yaushe ne guy ɗin nan yay mata irin wannan rainin har haka, bata taɓa haɗuwa da mutumin da ke latsata a yanda yake so da gadararsa irinsa ba, ya bala'i bala'in shigar mata hanci da yawa. Gadararsa da son nuna shi ɗin wani ne da iya taurin kai na cimata zuciya. Fitowa tai a bisa shawarar da zuciyarta ta bata, ta cije lips ɗinta tana jin kamar idan ta ƙarasa garesa ta shaƙesa kawai, amma sai ta ture tunanin gefe. Kujerar dake kallon wadda yake zaune ta dafa cikin ɗan sassauta zafinta dan ta fahimci ihun da take masan kamar tunzurashi yake da jin daɗin latsata. “Aliyu kafa san aiki nakeyi ka ɗakkoni ka kawo nan, kai miyasa baka bambance lokacin shiririta dana serious?”.
Batare da ya ɗago ya kalleta ba hankalinsa ma akan game ɗin sa ya ce, “Yima mijinki girki ne ba serious ba?”.
“Kai kasan mijin ma, Ka bani key na wuce, idan abincin kake so ai kasan gidan abinci, dan in har abinda zan girka zakaci ka siyama kanka wahala dan ban iya ba ma sai kabi wani sarkin”.
“Hummm ashe kuwa in dai ba zakiyi abinda nake so ba kuma ya dace ga matar aure to aikin ma zai gagareki yi ne, duk da a farko banda wannan niyyar. Dan haka kina da zaɓi kenan, yin yanda nake so kuma na tsara a gidana, ki samu yanda kike so kema. Ko ƙin yi, kema ki ƙi samu. Abinci kuma duk yanda kika iya kiyi zanci a hakan ko baiyi ba”.
Luuuu tai da idanunta kamar zata lumshe su sai kuma ta buɗe, komai ma ya gundireta, tama rasa yaya zatai da mutumin nan mai shegen taurin kai da gadara. Wai miyasa ma ta amince ne da wannan tsarin da shi? Miyasa bata bada damar a nema wani ba?. Tsaki taja mai ƙarfi da kai hannu ta dafe kanta, sai kuma ta janye tana mai watsa masa hararar zaka banbance tsakanin aya da tsakkuwa ta bar wajen. Da kallo ya ɗan bita ganin ta nufi hanyar store, tana shiga yay mata gwalo da sakin murmushi nan nasa da take kira na mugunta yana kashe ido ɗaya a hankali ya ce, “2-0 Madam”........✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣1️⃣
........Tana fitowa ɗauke da dankali ya fuske kamar bashi ba ya cigaba da game ɗin yana satar kallonta ta gefen ido. Ganin ta fara firar dankalin ya sashi ajiye wayar tasa a table ɗin ya miƙe, gefenta ya tsaya kaɗan, ya ɗauka wuƙar data ajiye saman chopped board ya fara yanka wanda ta fere, bata kulashi ba, ba kuma tayi magana ba ta cigaba da ferewa tana ajiye masa. Shima sai baiyi magana ba ya cigaba da yankawa, idan ya ɗan tara sai ya zuba a cikin ruwan data ajiye a bowl. A haka har suka kammala, kasancewar ta rigashi gamawa ita ta fara barin wajen ta ɗakko preyn fan ta dawo inda yaken ta zuba ruwan sabulu kaɗan ta wankesa da soso ta ɗaureye duk yana satar kallonta. Komawa tai gaban gas ta kunna ta ɗora sannan ta zuba man data ɗakko. Dai-dai nan ya kammala, sai ya wanke mata dankalin ya sake masa ruwa ya tace sannan ya juyo yana miƙa mata robar. Sai da ta hararesa ta amsa, shi dai ya gimtse dariyarsa da ƙyar ya juya yana ɗauraye wuƙa da sauran abinda sukai amfanin. Lulu kam koda albasanta ya soyu ta zuba dankalin sai ta nufi frizzier, kifi tai ƙoƙarin cira sai dai sanyin da ya ratsa mata hannu ya sata faɗin, “Ouchh!!”. Juyawa yay yana kallonta, ganin yanda take yarfe hannun ya sashi nufarta, hannun ya riƙo ya saka cikin nashi ya rumtse ɗumin nasan ya ratsata, sai kuma ya jawota gaban fanfo ya kunna ruwa ya ɗauraye mata hannun, sannan ya jawo ƙaramin towel ya saka mata hannun ciki. Komawa yay ya ciro kifin har biyu masu ɗan girma ya dawo ya wanke su sannan ya dubeta, ɗauke kanta tai da ga kallon gefen ido da take masa. Shiko da ba lura yay ba ya ce mata “Yankawa zakiyi?”.
Ƙaramar harara ta sakar masa da tura baki gaba sannan tace e.
“Kai dai Aliyu kana shan harara wlhy abin tausayi”. Ya faɗa yana yanka kifin. Hararar tasa ta sake yi da matsawa gaban dankalinta ta da ke cikin mai......
Kusan a tare sukai aikin, sai dai itace ke girkin shi kuma yana taimaka mata da yanka miƙo, duk da dai ba itace ke cewa yayi ɗin ba. Ya shiga matuƙar mamakin ganin yanda take girkin dama yanda tayisan, dan harga ALLAH bai kawo ta iya abinci ba. (Sai dai abinda Smart bai sani ba girki yana cikin hubby ɗin Lulu, tana son girki kuma ta iya kalolin girki na zamani sai dai fa sai ta gadamar yi take yin, tamafi sakin jiki tayi idan taje gidan Dada (kakarta matar Alhaji Garko) amma idan kaga tai girki a gidansu ko gidan Uncle Yousuf lallai ƴan arziƙinne a kanta ko taso yima Daddy wani bazata ko Uncle Yousuf ɗin). Abinda tai ɗin ya sashi jin daɗi bai ji ƙyashin tayata suka gyara kitchen ɗin ba duk da ma ba wani ya ɓaci bane dan Lulu akwai iya ƙwaf-ƙwaf ɗin aiki komai aka taɓa ana wankesa ne da zarar an gama da shi, inda ko ruwa ya taɓa za'a goge, tana hakanne kuma saboda yanayin tsaftarta, hakan kuma sai ya sake bama Smart nutsuwa kasancewarsa mutum mai shegen tsantseni da tsantsami. Dining takai komai ta ajiye tai wucewarta bedroom batare da ajiye plate ko kofin da za'ayi amfani ba. Baiyi magana ba saboda kiran Uncle Yousuf da ke shigo masa. Kiran ya amsa ya koma falo ya zauna. Har ya kammala wayar bata fito ba, dan haka ya miƙe yabi bayanta. Samunta yay kwance a kan gado rufda ciki sai dai ta canja kayan jikinta zuwa wasu, a hankali ya sauke ajiyar zuciya tare da yin gyaran murya. Kamar bazata kulashi ba sai kuma ta buɗe idanun kaɗan a kansa. Cikin ido suka kalla juna, ta janye nata da wani yin gaba da lips kamar mai son yin zinɗe, ta ce, “Wlhy in ma da wani abun kazo bazanyi ba na gaji”.
Dariya taso bashi dan yanda tai maganar da iyakar gaskiyarta, amma sai ya dake da ƙyar ya ce, “Ni na isa na sake saka Madam aiki ai tsaurin idon nawa ma sai yayi yawa. Sannu nazo yi miki, da kuma ban haƙiri da bikon kizo kici abinci. Har dama tausa idan kina so ƙyauya”.
Cikin taɓe baki da harararsa akan zancensa na ƙarshe ta ce, “Kai ne handin burum kaje kaita ci”.
“To Aliyu Hydar ka ƙara samun cigaba kenan, da ga illiterate velleger ka koma Maye, yau kuma handin burum, ɗan Ammah baban Ammah mijin Mawadda....”
Filon da take kwance ta fisga kafin ma ya kai ƙarshen sunanta da taji ya kamo ta wulla masa. Da sauri ya cafe yana zaro idanu, ya ce, “Madam ina rabaki da halin jifar nan kar wataran ki ɓazge min hanci kamar yanda Iffah tai ma Uwa fa tom”.
Wasu ta sake fisga tana tashi zaune ta cigaba da jefa masa su, tun yana karewa har ya fita yana dariya dan ya kula dai fushin ake saukewa a haka. Ƙwafa tayi itama da ballama ƙofar harara kamar itace tai mata laifin.....
Shi da kansa ya ɗebo plates ɗin da spoons bayan ya wanke su, ya zauna a ransa yana faɗin (Bari muci girkin ƴar madara muji). Da tea ya fara, lokacin da ya kai dankali da source ɗin ƙwai bakinsa sai da ya lumshe idanunsa. Wannan fa shi ake kira kama da wane bata wane, UBANGIJI mai rahama. UBANGIJI mai jin ƙai da baya haɗama bawa zafi biyu, idan ya jarabceka ta nan sai ya sauƙaƙa maka ta can dan kaji sanyi. A duk inda kaga mutum da halayya mara ƙyau kar ka yanke masa hukunci da ɗari bisa ɗari ɗin munanan ayyukansa, UBANGIJI shine kaɗai yasan abinda ke cikin zuciya da sirrikan ɓoye ga bayinsa. Ita dai a zahirinta duk wanda ya ganta suna ɗaya zai bata, amma a baɗininta sai UBANGIJIN da ya halicceta ya san kayarsa, sai ko wanda ya ƙaddara ya santan kamar dai shi mijinta a yanzun...
Yana gab da kammalawa ta fito, sai dai yitai kamar bata gansa ba ta zauna a falo ta ɗauka laptop ɗin ta ta cigaba da aikinta na ɗazun batare da kallon ko inda yake ba ko sau ɗaya. Shi ko dai sai satar kallonta yake time to time. Koda ya kammala sai ya ɗibo farfesun kifin cikin dauriya dan baya son kifi shi sam da tea ya nufota, ƙaramin coffee table ya jawo gabanta ya ajiye, ƙamshin kifin ne daya dakar mata hanci ya sata ɗagowa, harararsa tai ƙoƙarin yi yay saurin faɗin, “Ni dai tausaya min da hararar nan gidan ma zan bar miki karki lashe ni Ammah ko yaye ni batai ba”.
Hararar tasa dai tai ta ɗauke kai, sai kuma ta sake ɗagowa ta dubesa, karan farko ta saki murmushin da ke bayyana beauty point ɗinta da farare haƙoranta, ga wanda ya santa a kallo ɗaya zai fahimci na mugunta ne, saboda bata murmushi sai ta so, wanda kuma bai santa ba zai ɗauka yinsa matsayin birkita kwanyar duk wanda ya kalletan ne. Girarta a sama ta ce, “Waye zai fitan? Ka manta yau a gidan nan babu shiga babu fita? Ai duk yanda ka dama haka kowa zai sha wlhy. Ta miƙe ta nufi hanyar bedrooms. Da kallo kawai ya bita na mamakinta ne ko na son ƙarin bayani akan maganar tata ne oho masa. Yana a wajen harta da dawo da keys a hannu, a kallo ɗaya ya gane na ƙofar falon ne da ƙofar kitchen ta baya. Sai da takai zaune sannan ta tura su cikin rigarta a gaban idonsa ta gyara tana ɗaukar tea ɗin da ya ajiye mata ta kai baki.
“Idan ma wasa kike ki daina. Uncle Yousuf fa ke jirana tare da Yaya Abdull-Hameed”.
“Oh really?”.
Ta faɗa cike da rainin wayo. Hannu ya kai ya dafe kansa, sai kuma ya kai zaune a kusa da ita cikin lallashi ya ce. “Mawaddat Please seriously wlhy jirana akeyi, babu jimawar nan yay kirana kuma important ne zuwa 12”.
Batama ko kallesa ba balle ta tanka masa, sai ma kifinta data fara ci a hankali tana wani lumshe idanu taba banza ajiyarsa. Rasama mi zaiyi yay, cikin son ta fahimta yay ƙoƙarin kamo hanunta ta balla masa harara. “Karka kuskura hannunka ya kai jikina. Ka kuma kiyayi yin hakan inba haka ba kasha mamakin sanin ainahin Mawaddat Isma'il Ibrahim