Showing 132001 words to 135000 words out of 145230 words

Chapter 45 - Zakisan Koni Waye Complete

01 Nov 2025

275

bazata gane wurin ba, Salem takira ta shaida masa, tura mata number majed yayi yace in ta isa ta nemeshi.

Around 11 ta isa ta kira number da Salem ya turo.

Bayan kaman minti 40 majed yazo cikin wata white Prada, gaisawa sukayi, ya kalleta

"Pls I want to ask for your forgiveness kan Marin danayi maki..." Murmushi tayi

"Bakomai halina ya jamin after all ni na fara marinka so nima forgive me..."

"Godiya nake..." Ya ce mata Sannan ya shiga motan shi itama tashiga nata tabi bayanshi.

Around 1pm suka iso gidan, wangale ta tadda gate din, yaran unguwan sun shika gidan,

Murmushi tayi tare dayin horn yaran suka matsa gefe ta shiga da motanta, hinde ta hanga zaune gefen compound din da kayan tireda gabanta, tana ganin motan ta mike tana kallon motan cikin ranta kam tunani take masu gidan ne sukazo don su tada su. Ahankali ta dinga takawa tana karasowa wajen motan, Ameera na gama parking ta fito, Zainabu ce ta fito daga daki tana kallon Ameera, itama hinde wangala baki tayi tana kallon ta don Sam basu ganeta ba, Zainabu na Kara kallon ta sosai ta gane aikam da gudu ta tafi suka rungume juna, har lokacin hinde bata ganeta ba

"Innamu...Ameera ce..." Inji Zainabu, nan sauran yaran da hinde suka rungume ta suna shakan kamshin turarenta. Ameera kam lumshe idanuwa tayi don jindadi don tamkar family suke a wajenta, wurin kayan saidawan hinde ta kalla tana dariya tace

"Ashe kuna nan kuna kwasan dala...." Tafada tana dariya,

"Alhamdulillah... Ai Sai godiya..." Hinde ta amsa mata, daki suka shiga, ta zauna kasan carpet, suka fara hiran bayan saduwa, Tambayanta hinde tayi me zataci tace dan wake, aikam nan hinde ta hau girki Ameera da Zainabu na zaune gefe suna hira da Zainabu

"Babu mai gane kece.." Inji Zainabu, Dariya kawai Ameera tayi Sannan Zainabu tacigaba dacewa

"Ya kuka kara da Salem?..." Ta tambayi Ameera, nan Ameera ta kwace komai ta fada mata

"To Allah ya zaba maki mafi alkhairi.." Inji Zainabu,

"Hmmm ameen.. Ai shiyasa nazo...wallahi na rasa Wanda zai bani shawara..." Inji Ameera, Zainabu gyara zama tayi

"Meke faruwa kuma?..." Labarin sultan da Khalid ta fadawa Zainabu batare data boye mata komai ba, Zainabu shuru tayi tana sauraron ikon Allah

"Yanzu meye abinyi yi?..." Zainabu ta tambayeta

"Nama ban saniba...amma gaskiya inason in rabu da Khalid saboda dangatakar dake tsakanin shi da Salem Sannan kuma ya fada min shi manemin matane...."

"Hmmm...ai don wannan ba wani abu bane saboda da bai fada maki ba bazaki Sani ba....kuma..."

"Badai kina cewa in auri mazinaci ba..." Ameera ta tambayi Zainabu looking very surprised

"Ai gwara shi da ya fada maki... To shi sultan kinsan ayar da yake shekawa?...AI ki kalli maza kawai... Wani kaman ustaz amma in kikaji abinda sukayi kare baici...."

"Koma dai meye ba zan iya auran shiba....sultan kawai zan zaba..."

"To Allah yasa haka shi yafi alkhairi.. Amma kince tin kina yarinya kika san sultan... Meyasa baisoki ba sai yanzu da duk kyawun jikin ki ya fito?... Ni gaskiya gani nake Khalid yafi sonki fiye da sultan kuma anason mace ta auri Wanda yafi sonta ba Wanda tafi soba..." Ameera tsaya kallon Zainabu tayi

"Amma wallahi kin bani mamaki....mazinaci fah?...."

"Sai maimaita mazinaci kike...inda bai fada maki ba zaki Sani?..โ€ฆ kuma ki tuna in har kika aureshi ya chanza halin shi saboda ke zaki samu lada babba..."

"In bai chanza ba fah....sai inyi yaya?..." Ameera ta tambayeta

"Zai chanza tunda har ya bude baki ya fada maki hakan....ni wallahi ya kwanta min..." Ameera tabe baki tayi ta kauda kanta gefe ,

"Kilan ma shine Wanda yazo nan wace garin tafiyan ki..." Inji Zainabu

"Wani yazo nan bayan tafiya ta?.."

"Eh mana....wani farin mutum mai saje... Dukda ban san Salem ba nasan bazai fi wannan mutum daya zo nan kyau ba..." Ameera shuru tayi don kwatancen Zainabu ya nuna cewa Khalid ne,

"Yanzu dan Allah ki bani shawaran abinyi..." Ameera Tafadawa Zainabu, Zainabu kallon ta tayi

"Nidai anawa tunanin... Ki zabi Khalid... Ba don kun dace ba...amma don tseratar da rayuwan shi...." Ameera gallawa Zainabu harara tayi tana cewa

"Amma in kece bazaki zabeshi..." Bata idaba Zainabu tayi Dariya Sannan tace

"Wallahi kinji rantsuwan Dan muslimi?...in nice shi zan zaba...kin San saboda me?..." Kai kawai Ameera ta girgiza mata Sannan tacigaba dacewa

"Saboda ya fada min gaskiya game kanshi....wallahi mazan talakawa iskanci sukeyi balle su da ga kudi ga kyau...don haka shawara ya rage naki..." Ameera dai shuru tayi tafara tunani,

"Hmmm...kilan shima sultan ya taba... Shi dayake da budurwa baturiya?... Su da basu dauki zina bakin komai ba...Hmmm" Tafada cikin ranta,

"Amma ki kara fadawa innamu muji nata shawaran.." Inji Zainabu.



Bayan taci Dan wake ta fadawa hinde komai,

"Gaskiya bazance ki zabi kowaba acikin su... Kawai abinda zakiyi shine intahara...kiyi shi adaren yau...Sai muga abinda zai biyo baya..." Inji hinde

"To shikenan...". Tafada tana nufan boot din motanta , budewa tayi tafara fiddo kayan da taimakon Zainabu.

Adaren ranar tayi aduointa ta kwanta bayan sun sha hira da su hinde, mafarkin datayi ya bata mamaki, don Khalid tagani da pure white jallabiya yana fada mata how much he loves her,exactly maganganun daya fada mata shekaranjiya ya dinga maimaitawa shima sultan was wearing a white cloth but not as pure as na Khalid.

The following day ta fadawa hinde mafarkin datayi.

" zabi ya rage naki..." Tafada mata.

Around ten ta kama hanyan Kano, tana shan kwanan street dinsu ta hangi wani hadadden mota tsaye wajen gate dinsu, tana karasowa wajen taga Khalid ya fito daga cikin motan, da sauri tayi parking gefe daya ta fito, gani tayi yayi mugun rama kaman ba shiba, idanuwanshi sun chanza kala, karasa wurin shi tayi shima ya nufota

"Baby why are you doing this to me?..." Ya tambayeta muryan shi na rawa

"I will marry you..." Shine abinda ta furta mashi, da sauri yace

"Are you for real or am dreaming..." Da sauri tace

"For real..."

"Thank you so much... I promise to make you happy till the end of my life... Thank you for choosing me even after you know my dirty secret..."

๐Ÿ’™โค๐Ÿ’œ๐Ÿ’š๐Ÿ’›

ZAKISAN KONI WAYE

๐Ÿ’›๐Ÿ’š๐Ÿ’™โค๐Ÿ’œ

ยฎzuwairat(ummu Maryam)

7โƒฃ9โƒฃ

Murmushi tayi tana kallon shi

"Nima Nagode..."

"No ni keda godiya..." Yafada yana kallon eyeball dinta, kaman ya dauketa ya gudu yakeji, gani yake kaman anyi mashi albishir da gidan aljanna

"Baby zan tafi Adamawa in fadawa his excellency da first lady na samu matan aure..." Murmushi tayi

"Kashigo ciki in baka ruwa..." Da sauri ya girgiza mata kai

"I have to be on my way..." ya fada yana backwards zuwa wurin motanshi, kiss ya busa mata itama ta busa mashi Sannan ya shiga mota ya bar wajen da gudu, itama mota tashiga tayi horn aka bude mata tashiga tayi parking tayi cikin falo da gudu, da gudu ta hau upstairs har dakin mom, tana shiga ta fada jikin mom ta rungume ta

"Habibty ya hanya?".

" alhamdulillah... "

"Ya su hinde?..".

" suna lafiya.. Sunce in gaisheki..." Tafada sounding very excited

"Habibty.. Why do you seem happy... Ko da akwai abinda kikeson fadamin..." Tafada tana kallon how light up fuskan Ameera yake,

"Mommy.. I have choosen Khalid... Shi zan aura..." Tafada kanta kasa, tsaya kallon ta tayi

Mom dago fuskan ta tayi tari rike cikin palm din ta Sannan tace

"Yanzu habibty kinfi son Khalid kan sultan?..." Ahankali ta dagawa mom kai

"To Allah yasa haka shi yafi alkhairi..." Dasauri tace

"Ameen.." Kwantawa tayi kan gadon mom har dad ya dawo, wajen shi taje ta fada mashi abinda ta fadawa mom,

"Waye babanshi?.." Dad ya tambayi Ameera,

"Governor na Adamawa..." Ta amsa mashi, dadi dad yaji cikin ranshi,

"Zan zama in-law na governor..." Ya fada cikin ranshi, kunsan mai hali baya barin halinshi especially in ya zame maka jiki,

"Ki fada mashi ya turo..." Inji dad, da sauri mom ta kalleshi

"Ai ya kamata ayi bincike ko?.." Gaban Ameera faduwa yayi tana tsoron kar a binciko Khalid

"Wane irin bincike kuma?...waye baisan governor na Adamawa da mutunci da sanin ya kamata ba?..."

"AI bashi zata auraba danshi zata aura...."

"AI ba sai..." Dad bai idaba mom ta katseshi dacewa

"Zaka farako?...haka kayi lokacin aurenta da Salem... Kuma..." Da sauri dad ya daga hannun shi

"Shikenan... Ayi binciken....karki jamin sharri..." Itadai Ameera zama tayi tana sauraron su

"Tashi kije kici abinci..." Mom ta fada mata, mikewa tayi ta koma dakinta, kayan cikinta ta cire ta kwanta Sannan tayi dailing number sultan, nan ta fada mashi she have something to tell him.

Bayan sallan magrub yazo, hakuri ta fara bashi

"Pls can you hit the nail at the head?.." Ya fada mata dukda ya gane abinda ke faruwa, nan ta fada mashi ta fidda miji, murmushin karfin hali yayi Sannan yace

"Haba jewel...saboda wannan kiketa kame2 kaman kinyi abun kunya?... In baki mantaba I told you duk yanda Allah yayi daidai ne....so na dauki kaddara...." Yafada cikin sanyin murya, she never expect to hear that from him,

"Thanks for your understanding..." Tafada ahankali, baice kala ba ya mike

Ya fuskance ta, yana kallon beautiful and innocent face dinta, ahankali ya jawota jikinshi ya rungume ta, da sauri ta zame tana waige2 don ta tabbatar babu Wanda ya ganta, murmushi kawai yayi Sannan ya shiga motanshi ya tafi. Ameera komawa ciki tayi tana shakan free air don ji take kaman ta sauke mountains daga kanta.

Khalid kam yana tuki yana waya da Salem, nan ya shaida mashi Ameera ta amince zata aureshi.

Yana isa gidan su ya shaidawa first lady ya samu Matan aure, murna wurin ta baa magana Cos babu abinda take so kaman first son dinta yayi aure

Tunda Salem yayi aure take aduan Allah yasa shima yayi cos there are bird of the same feathers so there flug together. Dad dinshi ya fadawa shima wise man din cewa yayi

"Sao yanzu ka gandama kenan..." Khalid Dariya kawai yayi,

"Sai ayi bincike kan family dinsu kafin muje ayi maganan aure..." Inji his excellency,

_One week later_

Duk binciken daya kamata su dad sunyi kuma babu Wanda bai shaidan halin Khalid ba, asalima cewa akayi yafi sauran brothers dinshi mutunci, ( hmmm daman bincike baisa agane dukkan halin mutum.. Sai ka zauna dashi)

Abangaren Khalid kam suma anyi bincike amma sun gano yarinyan ta taba aure,

"Yanzu son yarinyan data taba aure zaka aura as a first wife?.." Shine tambayan da mom dinshi tayi mashi, ahankali Khalid yace

"Mom..ita nakeso....kuma duk karyan mutane ne...bata taba aureba...."

"AI ba hanaka zanyi ba tunda ba haramun bane...am happy zakayi aure" Tafada cikin jin dadi.

Bayan sati daya uncles din Khalid da wasu manyan mutane sukaje gidan su Ameera Neman aurenta, kuma da kayan saka rana sukazo, Dad dadi sosai yaji don yasan yanzu yarshi zatayi aure, anci ansha Sannan aka sa sati 8 that's two months.

Tunda daga ranan aka dauko mai koyawa Ameera abinci da sauran aikace2 gida. Ana sauran 7 weeks Khalid ya shigo Kano, ba karamin kyau yayiba, itama tayi kyau sosai saboda gyaran jikin da anty Sadiya ta fara yi mata, kasa daina kallon ta yayi, kanta kasa Sai wasa take da fingers,

"Babyna haduwanki bai faduwa..." Yafada yana murmushi, itama murmushi tayi,

"Do you have any special events in mind?.." Ya tambayeta, ahankali ta girgiza mashi kai

"So ki yarda in sa ashirya all the events?.." Ya sake tambayan ta, ahankali ta daga mashi kai, kallon ta yayi

"Baby wannan kunyan fah?...tunda nazo baki daga kai kika kalleni ba...what have I done wrong.." Ya tambayeta kaman zaiyi kuka

"Nothing..."

"Then pls look at me..." Yafada cikin whisper, daga kanta tayi suka hada ido, ido daya ya kashe mata, tayi murmushi tare da dauke kanta,

"Angel INA kikeso mu zauna?... I have two duplexes in abuja....two in yola Sai one a banana island lagos..." Ameera shuru tayi bata ce komai ba don babu abinda take tunawa kaman ya kusa ganin nakedness dinta,

"Angel say something.."

"Duk inda kakeso..." Ta fada mashi

"Ko in sayi gida nan Kano?..." Kallon tayi ta saki murmushi, Dariya yayi

"Baki idaba yarinya... You want to be close to mommy..." Ya fada yana dariya, Itama Dariya tayi don ya gano ta,

"Ai bance mu zauna nan bako..." Ta fada cikin shagwaba, Dariya ya karayi yana cewa

"sayi gida nan mu dinga sauka in Mun zo Kano..." Daga kai tayi ta harareshi

"Ga gidanmu?..." Baice komai ba ya sa hannu cikin aljihunshi ya dauko wani small jewelry box, ya bude, wani white ring ne mai dauke da diamond stone samanshi, hannun ta ya kama ya sa mata Sannan ya Kara dauko wani envelope ya saka cikin palm dinta, kallon zoben tayi ta saki murmushi cos ba karamin kyau yayi wa hannun ta ba. Sun dade suna hira batare data bude envelope dinba, sallama yayi mata ya kuma shaida mata yanzu saidai su dinga waya cos he will be very busy saboda wedding arrangements.

Tana komawa sama taga credit card ne da pin number kiranshi tayi ta tambayeshi ATM din na meye ya shaida mata ta zari any amount da take bukata for her friends anko.

Duk yanmatan dake yiwa Ameera habaici saida suka dawo suka bata hakuri don ta dama dasu, batayi masu wulakanci ba aka shiga harkoki dasu, zeenat kam bataji dadi abinda Ameera tayiwa sultan ba amma she takes everything in good faith.

Ba karamin gyara Ameera take shaba don abubuwan is to much, jikin ta ya kara kyau fiye da yanda kuke tunani, kullum cikin waya suke da Khalid.

Ana sauran sati four biki aka kawo lefenta, fadin kyau da yawan kayan is a waste of time and strength just imagine lefen yayan governor, kuma civilised one don mom din Khalid wise woman ce ta gidan karshe, akwati 18 aka kawo 12 lv sai 6 gucci traveling bag da mota daya sai kujeran makka 3, mom kam abun tsoro ya bata dad baki har kunne saboda jin dadi, duk Wanda ya zo ganin lefen Sai ya koma da baki bude, aranan Ameera da Khalid suna waya take shaida mashi kayan sunyi yawa, cewa yayi bai ma gansuba Kuma ta dauka duk yawan kayan can never be compired to her beauty.

Abangaren Salem kam duk ya damu ba don komai ba sai yanda Khalid yaki amsan komai daga hannun shi, duk abinda ya bashi Sai ya ki amsa yana cewa bayason rai Ameera ya baci, ko yanzu suna zaune da tawa tawa suna kallo shi kuma yana waya da Khalid,

"Guy gaskiya abubuwan da kakeyi is touching me... Ya zakayi min haka...we grow up together... Amma zakayi aure ka ki amince wa da komai daga gareni..." Inji Salem daga chan bangaren Khalid yace

"Just understand....banason abinda zaisa Ameera bacin rai...remember she almost dump me because of you..." Gyara zama Salem yayi Sannan yace

"Yanzu guy mace zata rabamu da kai kenan?..."

"Haba wake maganan rabuwa...it's just for the main time..." Inji Khalid,

"Ba komai...we will be coming back next week..." Inji Salem yana rike hannun tawa, da sauri Khalid yace

"I beg you in the precious names of Allah... Don't come back now... Wait until five weeks for now..." Ido Salem ya zaro

"Hope this is not what am thinking?..."

"Yes it is... In ka dawo su first lady da first love zasuyi mamakin rashin ganin ka a wedding dina...so pls just wait till after my wedding..."

"Yanzu Khalid are you saying I should not be present at your wedding?.." Ya tambayeshi afusace, ahankali Khalid yace

"am sorry but yes...." Salem bai Kara cewa komai na ya katse wayanshi tare da mikewa daga inda yake zaune kusa da Tawakaltu, da sauri ta bi bayan shi,

"What's wrong?..." Ta tambayeshi,

"Nothing..." Ya fada mata atakaice, rike mashi hannun tayi ya fixge

"I said nothing!...." Ya daka mata tsawa, da sauri ta ja baya, tana kallon shi, gaba yayi tabi bayan shi Ahankali, afusace ya juyo ya kalleta fuskan shi Sam babu walwala

"See just go back...right now am upset and I don't want to be disturbed..." Kuka tafarayi tana cewa

"So am disturbing you?...to shikenan... Let me keep my distance..." Tafada tana juyawa Ahankali tare da dafa maranta, Salem tsaya kallon ta yayi har ta zaunasai yaji bai kyauta ba cos ba ita tayi mashi laifi ba amma he's taking it on her, komawa yayi wajenta,

"Princess am sorry... Kawai rainane a bace...kiyi hakuri kinji?"... Kai ta daga mashi, hannu yasa ya goge mata hawayenta tare da jawota jikinshi.

Ahankali lokacin ke tafiya inda Khalid ya kawowa Ameera list na events da zasuyi for a whole week, kuma ko wanne rana nada dress code, ana sauran two weeks Ameera ta rabawa friends dinta iv. Yanmatan kam shirye suke don sunji abun nayine.

Gyaran da anty Sadiya takewa Ameera yafi na wancan lokacin cos ta samu enough time and money, Sannan lefen da aka kawo ya Kara nunawa cewa ba anyhow mutum zata aura ba haka yasa kullum da abinda take bata, Sannan yanzu ba laifi Ameera ta iya at least not less than 15 variety of food

Duk Wanda yaga pre wedding pics dinsu Sai yace Ameera da Khalid sis and bro ne saboda yanayin hasken su da pointed noise,guys Sai zolayan Khalid suke suna cewa ya fi abokinshi iya zabe, cikin ranshi kam saidai yace bakusan shi ya fara aurenta ba.

Yau sauran ten days saurin aure, da yamma around 5pm wani moving van ya shigo gidan, mom fitowa tayi tana kallon katon van din Sai mamaki van din take don sai gobe kayan Ameera suke isowa, driver ya fito daga cikin van tare da yaranshi, kallon mom dake ta mamaki yayi Sannan yace

"Sakone daga sultan..." Baki mom ta bude da aka fara sauke kayan, complete set ne na kujera da da gado, exactly irin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login