Showing 141001 words to 144000 words out of 145230 words
ciki saida Salem ya sanar dashi
"Angel ina tunanin Salem..."
"Pls Ku shirya..." Ta fada cikin sanyin murya,
"Baby baya picking calls dina....har yanzu fushi yake dani...wallahi it is disturbing me..." Kara rungume shi tayi tana cewa
"Kaje wurin shi mana...ka bashi hakuri cos kai ka bata mashi rai..." Inji Ameera dake Kara kankame mijin ta kaman Zaa kwace matashi.
"Sai kinji sauki...I can't leave you now... " yafada yana shafa cikinta.
Abangaren su Salem kam har yanzu Tawakaltu na wurin Umma amma babu abinda hakan ke hana Salem don duk kwana biyu yake zuwa yola, Umma Sai mamakin shi take don da Sai yayi wata baizo gida ba amma yanzu every two days Sai yazo.
Yanzu cikinta ya kai wata shida going to seven duk fuskan ta ya chanza ka pimples, duk sanda Salem yazo yaje inda take Sai ya durkusa kasa yace
"Hajiya inawuni?..." Hakan yana bawa tawa haushi sosai, at times Sai ya kura mata ido ya tuntsure da Dariya, ta shika tayi fam ga takuran ciki ga na Salem.
Suna zaune kan dinning table dukkan su har Abba suna cin lunch, Salem ya daga kai ya kalli tawa ya tuntsure da Dariya, kallon shi tayi ta galla mashi harara ya daga mata gira,
"Zakuje gidan abokinka ko?..." Inji umma, Da sauri Salem ya kalleta,
"Umma wane abokina?..." Ya tambayeta don sam ya manta da su Khalid, hararanshi tayi
"Kana nufin bakasan Khalid ya dawoba?..." Da sauri ya saki murmushi
"Oho...nasani mana...bansan shi kike magana ba..."
"Aboki nawa gareka?..."
"Shi kadai...." Inji Salem, Abba kam baice kala ba cos shi yana daga cikin policy nashi baya magana while eating.
Bayan sun gama lunch ya tafi part dinshi yayi kwanciyan shi, har 4:30 bai nuna alaman zaije wurin Khalid ba donshi har yau bai bar jin zafin abinda Khalid yayi mashi ba, Umma ce ta shigo part dinshi, zama tayi shima ya mike zaune
"Habibi ka fada min gaskiyan abinda ke faruwa tsakanin ka da Khalid..." Da sauri ya saki murmushi
"Babu komai.."
"Da komai mana...Khalid da ya tsaya ya taya ka komai lokacin bikinka bakazo nashina dukda nasan haka nan kaki zu...Sannan yanzu na fada maka ka kai matarka amma nuna alaman kana son zuwa ba...son what is happening..."
"Umma ba komai.... Daman cewa nayi bari rana ta sauka Sai muje tunda na kirashi ya fada min inda gidan yake..."
"To kuyi sauri kuje... Baason mai ciki kan titi da magrub..." Tafada tana barin dakin.
Tawakaltu ya kira ya fada mata ta shirya zasu fita
Bata yi wasting time ba tayi wanka ta aka jallabiya ko kwalliya batayiba don ta kanta take, shima Salem wanka yayi ya shirya tare da sukaje dakin Umma sukayi mata sallama Umma tace
"Ku gaida su..."
Cikin mota suka shiga driver ya jasu sukafita,
"Ka kaini gidana..." Salem ya umarceshi, Tawakaltu kallon shi tayi
"Umma tace gidan sir Khalid zamu..."
"Baby I can't go to Khalids house...remember he denied my presence at his wedding..." Yafada yana jin haushi har cikin ranshi
"Amma ai yana kiranka...kai ne baka picking... Ni dai gaskiya ka kaini gidan..." Tafada tana harde hannuwanta kan kirjinta,
"No...muje gidana ..."
"Wallahi kasa driver ya kaini ko kuma in fadawa Umma " tafada kaman zatayi kuka.
Tsayawa yayi yana kallon ta, aikam kuka tafarayi tana cewa
"Kasa akaini..." Rarrashin ta yayi don ko kadan bayason kukanta, fadawa driver inda zasu yayi don yasan gidan.
Wurin bashi da wani nisa sosai don haka babu bata lokaci suka isa gidan, Salem kallon Tawakaltu yayi
"Princess ki shiga ki fito..."
"Bazaka shigaba?..."
"No..." Ya amsa mata atakaice, fita tayi driver ya fito yayi knocking a gidan, maigadi ya bude ta shiga, daya daga cikin gidan Wanda yayi kama da daakwai mutane tayi knocking, shuru baa bude ba, tafi minti biyar tana danna door bell.
Alokacin Ameera na kwance jikin Khalid don evening fever take, yana jin ana knocking amma bayason tashi, dole Ameera tasashi mikewa.
Tawakaltu har ta juya ya bude kofan, mamaki ne kwance kan fuskan shi,
"Aa...Ashe kece...come in..." Yafada yana komawa gefe, murmushi tayi ta shiga, gaisawa sukayi,
"Ya akayi kika gane nan?..." Ya tambayeta
"Tare muke dashi..." Da sauri Khalid yace.
"Yana INA?..."
"Yana waje..."
"To bari in shigo dashi kafin in kirawo Aisha...daman bata da lafiya ..." Yafada yana fita daga falon.
"Allah yasa ka shawo kanshi..." Inji tawa cikin ranta.
Khalid na fita chan waje ha hangi wata dunkulellen mota yasan Sai Salem, wurin motan ya nufa, Salem na ganishi ya daure fuska irin yana fushin nan. Khalid bude motan yayi
"Haba guy...fushin ne har yanzu shine bazaka shigo cikin gidana ba?..." Inji Khalid, Salem kallon shi yayi yaga yanda ya chanza
"Ni da baa son tarayya dani?...me zanyi cikin gidan ka..." Khalid shiga yayi cikin motan ya fara bashi hakuri, daman Salem yayi missing dinshi,
"Yanzu ko shigo ciki..." Inji Khalid, babu musu Salem ya fito, suka shiga cikin gidan.
Tawakaltu dadi taji sosai data ga Salem tare da Khalid, zama yayi gefen tawa shi kuma Khalid ya shiga inda Ameera ke kwance daga ita Sai pant and bra,Ahankali ya tabata ya bude ido daman ba bacci takeba,
"Baby...munyi visitors..." Ahankali tace.
"Su waye?...".
" Salem da matanshi... " da sauri ta mike zaune tana cewa
"Da gaske sir Salem da Tawakaltu sun zo?..."
"Yes..." Ahankali ta mike, jallabiya Khalid ya dauko mata tare da Vail, saka mata kayan yayi Sannan ta yafa Vail suka fito hannun shi rike da nata, suna fitowa Salem ya kalleta, itama ta chanza sosai amma alhamdulillah bai ji komai ba, rungume juna sukayi da Tawakaltu, gaisawa sukayi da Salem Sannan kowacce ta koma gefan mijinta, Khalid Dora kan Ameera yayi kan kafadanshi don yanajin tana nishi2 kasa2 Wanda shi kadai ke jin hakan. Hira sukayi sosai kaman ba friends dake fushi da junansu few minutes back ba.
Pls manage..
๐๐โค๐๐
ZAKISAN KONI WAYE
๐๐โค๐๐
ยฎzuwairat( ummu Maryam)
8โฃ3โฃ
*My Sadnaf,Allah ya barmin ke ya kara basera, you are* *awesome and free of jealousy..Allah ya kara tsaremin ke daga sharrin masu sharri. The whole page is yours.*๐๐๐
Ameera Sai kara lafewa take jikin Khalid don sam bata jin dadin zaman, Salem da Khalid Sai hira suke ita kuma Tawakaltu hankalin ta na kan film da ake nunawa cikin MBC 2, suna cikin hira Ameera ta zame ta dora kanta kan cinyan Khalid tare dayin pillow da hannun ta, Khalid kallon ta yayi tare dayi mata magana cikin kunnenta, kai kawa ta gyada mashi,Salem kallon su yayi
"Guy bata da lafiya ne?..." Ya tambayeta yana kallon yanda Ameera ta lumshe idanuwa kaman mai bacci, murmushi Khalid yayi Sannan yace
"We're pregnant..." Idanuwa Salem ya kwalo yana cewa
"Woww...congrats..." Yafada Sannan ya kalli Ameera
"Sis congrats..." Ameera murmushi kawai tayi, Kara kallon Khalid yayi
"Mun dai girme ku..." Yafada cikin zolaya, Dariya Khalid yayi yana shafa kan Ameera
"Ba komai... AI baifi five months ba..." Tawa kam batasan abinda suke cewa ba don ko kadan hankalinta bai wajen, suna nan zaune aka kawo dinner daga government house, Khalid amsa yayi ya ajiye kan dinning, alokacin ana kiran sallan magrub
"Guy bari in kai Angel inyi mata alwallah Sai mu tafi masjid...." Inji Khalid, Khalid Dariya yayi yana cewa
"To mai angel...." Inji Salem, dukkan su Dariya sukayi, Khalid mikewa yayi ya dauki ameera sukayi hanyan bedroom din da suka fito, tawa kallonsu tayi ta saki murmushi tare da kallon Salem, shima kallon tayi
"Ya akayine?...ko kema so kike in dauke ki...Hajiya..." Bai idaba ta dauki pillow ta wurgamashi, dariya
Yana cewa
"Hajiya me nayi maki?..." Ya tambayeta yana kare fuskan shi da wani pillow yana dariya,
"Wallahi ka bar kirana Hajiya?..." Ta fada kaman zatayi kuka, Dariya yayi yana cewa
"Kwantar da hankalin ki....makka zaki haihu...innamu..." Yafada yana dariya sosai, buga kafa tafarayi tana cewa
"Ka dura min ciki kazo kana zolayata ko?..." Dariya Salem ya dingayi sosai
"Wai na dura mata ciki...wa yace ki budemin kafa?..." Pillow ta kara dauka ta buga mashi ya kauce yana dariya.
Khalid nashiga yayi wa Ameera alwallah Sannan shima yayi alwallah, har lokacin jikin ta zafi sosai
"Baby ko in kara maidaki hospital in su Salem sun tafi?..naga har yanzu bai saukaba..." Ahankali ta girgiza mashi kai
"Ai...mom tace in bar zuwa hospital wai ko naje babu abinda zasuyi min
..." Ta fada gwanin ban tausayi, kiss yayi mata ya shimfida mata praying mat, Sannan yace
"Baby Bari muje masjid..." Kai ta gyada mashi tare dacewa
"Ka fadawa sis Tawakaltu ta shigo nan tayi sallah..."
"Ok..." Ya amsa mata Sannan ya fita, yana zuwa yaga Tawakaltu sai jifawa Salem pillow take shikuma yana kaucewa yana dariya, shima Khalid murmushi yayi ya karasa inda suke yana cewa
"Wanda kukayi a gida bai isheku ba?..." Inji Khalid, Salem yana dariya yace.
"Wai don nace mata hajiya shine take fushi...."
"Sis rabu dashi...ki shiga ciki kiyi sallah... Kaikuma ga shiga chan kayi alwallah mu tafi..." Ahankali tawa ta mike tana hararan Salem, gwalo Salem yayi mata
"Zamuje gidane.." Tafada mashi Ahankali Dariya Salem yayi yana cewa
"In muje gida ki hana ni...." Da sauri ta shige shikuma Khalid ya saki dariyar rainin hankali yana cewa
"Ka San dadin abun yanzu ko....gashi ko kunyata bakaji..." Hararanshi yayi
"Da inji kunyarka gara... Inji kunyar dan akuya..."
Yafada yana mikewa, inda Khalid ya nuna mashi ya shiga ya dauro alwallah suka tafi masjid.
Tawakaltu na shiga ta hangi Ameera tana sallah, saida ta salkame ta nuna mata hanyar bathroom, itama shiga tayi ta dauro alwallah ta tada sallah, Ameera komawa tayi gefe ta hada kai da gwaiwa cos ita kadai ta san abinda takeji. Bayan Tawakaltu ta idar da sallah ta kalleta
"Sannu sis..kina jin jiki..." Tafada tana kallon ta, Ahankali Ameera ta daga kai
"Yauwa...pls dama kema haka abun yayi maki?..." Ta tambayi tawa cikin sanyin murya
"Gaskiya bai yimin haka ba...kawai ni dacin baki da kasala ke damuna... Ke mai zafi kika ciyo..." Tafada cikin zolaya. Murmushin karfin hali Ameera tayi
"Wallahi sis...har na gaji...in haka ciki yake gaskiya duk Dan da baiji maganan uwarshi ba ya shiga uku...."
"Hmmm haka ne...Dan bai San wahalan da uwa take sha kanshi ba amma ya girma ya nuna ya fi uwar wayau da hankali..." Ahankali Ameera ta girgiza kai
"Allah ka kiyashemu da yaran da basu jin maganan iyayensu..."
"Ameen..." Tawa ta amsa mata, hiransu suka cigaba dayi har su Salem suka dawo daga masjid. Salem zama yayi inda ya tashi shi kuma Khalid yayi arranging dinning table da abincin da aka kawo daga gidansu
"Guy kayiwa Tawakaltu magana tafiya zamuyi..." Inji Salem,
"Muyi dinner tare mana..." Inji Khalid
"No...zamu tafi..." Yafada yana kallon agogon hannun shi. Khalid bai kara cewa komai ba ya shiga ciki ya kira Tawakaltu, ahankali Ameera ta mike tana cewa Tawakaltu
"Dan Allah sis ki dinga zuwa dubani tunda kince kina yola har ki haihu..."
"To...in mai house ya amince...".
Dukkan su fitowa sukayi, Salem na ganinsu ya mike, Tawakaltu ta karasa wurin shi ya rike mata hannu, shi kuma Khalid ya zagaye hannun shi ga kugun Ameera suka rakasu har bakin mota Sannan Khalid ya dauketa in a bridal style suka koma ciki.
Daga wannan ranar Friendship dinsu ya dawo, duk ranar da Salem ya shigo yola Sai sunje gidan Khalid don har kusan wata biyu Ameera bata samu saukiba.
Tsakanin Ameera da Tawakaltu shakuwa ce sosai don har su Salem cewa suke kar a munafurcesu, don kullum suna cikin waya da junasu in har basu tare.
Sultan kam ba karamin soyewa suke da Habeeba ba, duk family sun San da soyayyar su, dukda sauran shekara daya ta gama daga Oxford university sultan yaki wai dole suyi aure before then kuma yayi alkawarin zai barta tayi aiki a duk kasan da take so.
Yanzu Tawakaltu na jira taga ta yanda labor zai fara don lokacin ta yayi kawai tana jiran time, babu yanda Salem baiyiba don Umma ta barsu su tafi abroad haihuwa amma taki tana cewa mai sa a sauka lafiya chan shine a nan din haka bazaa sata zaryan kasan wajeba. Dole Salem ya hakura ya kira wata kwararriyar doc daga london, matar ta San aikinta sosai don har su pregnancy exercise take sa ta. Tawakaltu kam abun duniya ya isheta don ji take kaman ta cire cikin ta yarda don tunda ta shiga watanta takejin nauyin cikin, yanzu Salem ya bar zolayan ta don kiris take jira ta fara kuka, tun jiya Salem ya dawo yola kuma baida niyyan tafiya da Umma ta tambayeshi cewa yayi yana nan har Sai Tawakaltu ta haihu, kai Umma ta girgiza tana mamakin rashin kunyan Salem Sai kuma ta tuna cewa ba yaro bane shi.
Kullum Tawakaltu cikin yiwa Umma adua take don ba karamin kulawa take bata ba, duk abinda take so shi zata ci balle cikinta ba mai selecting abinci bane. Sannan kullum tana bata maganin masu ciki tana sha ga wasu mami ta aiko mata.
Daman da akwai home hospital a gidansu Salem don haka abubuwan da ake bukata wurin haihu aka saya aka sanya wurin yanda koda haihuwan ta zo basai sun tafi waje haihuwa ba. Salem kullum cikin online shopping yake dukda sunyi shopping a kasar waje amma gani yake kayan basu isaba.
Yau tana zaune kasan carpet bayan sallan ishai doc Vicky tana dan ne mata kafafunta, Salem ne ya bude kofa ya shigo, kallon shi tayi ta kauda kanta kaman bata ganshi ba cos yanda take jin haushin shi Allah kadai ya sani, din gani take shi yasata cikin wannan conditions kuma shi kullum cikin gayunshi yake, gaisawa sukayi da doc Vicky t fita ya karaso kusa daita
"Babyna ya kike?.." Ya tambayeta yana zama nan kasan inda take,
"Lafiya..." Ta amsa mashi atakaice, murmushi yayi
"Princess nayi wani laifi ne?../" bata kalleshi ba tace
"Wayace kayi laifi?..."
"Naga tunjiya kaman kina fushi dani...jiya ma kin bani hakkina kikayi...." Galla mashi harara tayi
"Kai kullum hakkinka...ni baka tausaya min?...baka ganin yanda nake?....ni wallahi ta kaina nake...ji nake inama ina iya baka ajiyan wannan cikin... Am tired.." Ta karashe maganan kaman zatayi kuka, hannun ta ya kama yayi mata kiss
"Sorry.. Kin kusa hutawa insha Allah... Daman aski inyazo gaban goshi yafi zafi....sannu kinji..." Bata amsa ba ta kara kallon shi ta galla mashi harara again,
"Ni banason wannan sannun...." Dariya yayi
"Me kike so?..."
"Nima ban saniba...kawai am tired...."
"Bari in hada maki ruwan wanka...." Ya fada yana mikewa,
Bathroom ya shiga ya hada mata ruwan wanka yadawo ya dauketa suka shiga ciki, kayanta ya cire mata yafara kokarin cire nashi, kallon shi tayi
"Me zakayi?..."
"Wanka zamuyi tare...."
"Aa...ka tafi part dinka kayi wankan..." Murmushi yayi din ta gane manufarsa, bai saurareta ba ya cire kayan zo kusa daita
"Babyna...let's do it ...kilan kafin tomorrow kin haihu and I will be lonely for a while...." Yafada yana kissing wuyanta, kallon big belly dinta tayi tana mamakin yanda baya gajiya da abu daya har ya fara koya mata hakin shi, ahankali ta dan zame tana cewa
"Ni marata ke yimin ciwo..." Tsayawa kallon ta yayi
"Tun yaushe yake yi maki ciwo?..." Ya tambayeta sounding very caring
"Dazun... "
"Kin fadawa Vicky?..." Girgiza kai tayi
"AI ba sosai yakemin ciwoba...yazo kadan ya koma ya dawo.. " yanda take maganan in I don't care tune yasa Salem ya tsaya kallon ta
"Amma baby an fada maki kome ke damunki ki dinga fada mata... Kilan you are having a contractions..." Murmushi tayi tana cewa
"In haka ake contractions da kullum zan dinga haihuwa..." Tafada tana dariya, wanka sukayi tare da hot romance suka fito, kara tambayan ta yayi ko tana jin zafin mararta ta amsa mashi da No
Cikin wardrobe ya shiga ya dauko mata kayan bacci ta saka ta hau gado, lokacin kuma ta farajin ciwon maran, amma bata fada mashi yayi bata good night ya tafi ya kwanta, itama kwanciya tayi.
Har ten maran na kara ciwo ahankali amma bata dauki ciwon serious ba saboda daman in zatayi period tana irin wannan ciwon.
Fitsari tajeyi taga wani abu kaman mucus mai hade da jini, da sauri ta fito ta tada Vicky da ke kwance gefen gadon ta fada mata abinda ta gani, safa ta dauko ta umarceta data kwanta ba musu ta kwanta, dubata tayi ta fada mata she's in labor, tawa mamaki take wai ashe daman haka haihuwa keda sauki?, nace you must be joking,
Around 4am abun ya zama gaskiya don banda yarfe hannuwa babu abinda take har lokacin baa sanar dasu Umma da Salem ba, kuka tafarayi tana yarfe hannuwa da zafin ya bari Sai ta goge hawayenta, chan Sai ta fara kuka, Vicky sai danne mata waist take, karfe biyar taji contractions din ya zama unbelievable
"Wayyo ki kira salem...mutuwa zanyi...." Ta dinka maimaitawa Vicky da turanci, Vicky kiran number Umma tayi sai na Salem ta sanar dasu halin da ake ciki, tawa durkusawa tayi gaban gado ta dora kanta ta fara bacci, ko minti biyu bata yiba ta farka ta fara kuka sosai, lokaci daya Salem da Umma suka shigo, tawa Sai zufa take kaman babu ac a dakin, duk hankalin Salem ya tashi, Umma sannu ta dingayi mata amma babu bakin amsawa Sai kuka,
"Please a kaita wurin haihuwn..." Inji Umma,
"Stand..." Vicky ta umarceta ahankali, da sauri tawa ta girgiza kanta tana cewa
"Ban Iya tsayawa...." Tafada cikin kuka
"Wayyo bayana...Mara ta
.." Ta dinga maimaitawa,
"Baby sorry..." Inji Salem dake magana kaman shi ke labour, Salem ne ya daga ta tsaye Sai ihu take, duk yanda Umma ke hana ihu Sai tace
"Wayyo Ku barni inyi kona ji sauki....Dan Allah Ku kiramin mami..." Da kyar suka isa mini hospital Ta shiga tana tafiya da kyar don data daga kafa daya Sai tayi minti biyar bata daga dayanba,