Showing 18001 words to 21000 words out of 117786 words

Chapter 7 - Me Zanyi Da Ita Book 1 Hausa Novel Complete

M SHAKUR   

22 Dec 2024

453

zasuyi da sassafe zasu bi flight d’in safe su tafi, haka ma hajiya mama tace bata son tashin hankali su taho kawai. Shatu kuwa ta’kudirce a ranta tsohuwa hajja ba zata kwana lafiya ba sai Ta gwammace kid’a da karatu.


Cikin dare shatu ta mi’ke daga gefen nahna da suka kwana tare a d’akinta, sad’af-sad’af ta fice. Murd’a ‘kofar hajja tayi a hankali ta shige ta mayar da ‘kofar ta rufe, dubanta ta kai kan hajja da ta saki baki tana barci tayi, har da yawun barci ta saki dariyar mugunta bayan ta kashe fitilar d’akin da fanka har da a.c . ‘Dif d’akin ya ba’kunci duhu ga windows dama duk a rufe, shatu ta shige ‘kar’kashin gadon hajja a hankali, kasancewar ba auki ne da ita ba zuruf ta shige . Muryarta ta kumbura ta fara fad’in “ke tsohuwa ke tsohuwar banza tashi maza ajalinki yazo....” Hajja da taji maganar daga sama a razane ta farka taji d’akin d’uf misalin dai duhun kabari da ake fad’a . “Kada ki sake kiyi mana ihu ba dai kince kin ‘konamu ba zuwa mu kayi ki ‘kara ‘konamu mun ja kunnenki ba kiji ba to yau a tsakiyar dajin aljannu zaki kwana kafin gari ya waye mu zu’ke jininki.......” Hajja jikinta ‘bari kawai yake murya a razane take fad’in “ Hajja kwananki ya’kare idan ban da shegiyar ‘karyata dama mai ya kaini cewa nayi fad’a da aljannu......😂😂🤣🤣🤣




Kai yau nayi typing da yawa so that ina jiran in ga ruwan comments.

*🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍



NAZEEFAH SABO NASHE


FREE📚
08033748387
-12



ELEGANT ONLINE WRITERS..........



Shatu tayi saurin matse dariyar da take son kamata, ta sake jijjiga ‘kasan gadon , cikin murya mai amo sosai tace “ Baki ga komai ba tsohuwa sai kin bud’e ido kin ganki a gaban sarkin aljannu yana bada umarnin a shanye jininki a yar da gawarki a daji namun daji su cinye ba dai ba kya jin magana ba mun ce ki fita daga harkar hadizatu kin ‘ki hahhhhhahhhha yau zamu sha jini ku ‘karaso maza ku d’auketa kada ku sauketa sai a dajin sarki ‘kuraizu hahhhhhahhha.” Ta sake tuntsirewa da shegiyar dariya hajja kuwa tuni ta sume tun bayan da Ta ‘kwallara wata ‘kara da duk gidan ya amsa bayan taji an jijjiga gadon da ‘karfi. Imran ne ya fara fitowa kafin su mommah suma su fito kowa yana Duban d’akin hajja inda ‘karar take fitowa. Imran baiyi wata wata ba ya bud’e d’akin da sauri ya ‘karasa gun hajja da ya gani a san’kame akan gado, ya fara jijjigata sai dai ba alamar numfashi a tare da ita, idanunsa ne ya sauka akan tsinkakken abin hannun shatu da sauri ya zaro ido bayan ya d’au abin hannun yana dudduba inda zai ganota, bai ga alama ba ya zira abin hannun a aljihunsa. Momma kuwa da sauri ta ‘karaso tana dubata a gigice take sosai hakan yasa murya na rawa take cewa “ Imran kira doctor she is unconscious “ Imran ya mi’ke yayi saurin shiga toilet nan ma bai ga shatu ba, ruwa ya d’ebo ya zubawa hajja a jikinta ,da sauri ta kawo ajiyar zuciya ihu take tana fad’in kada ku tafi dani bijahil kudrati na daina shiga sabgar dijama innalillahi.” Kowa d’akin tsit yayi yana kallonta, Imran ya kamata “ Tashi Hajja ba wani aljannu da izinin ubangiji koma akwai zan binciko su” Hajja ta mi’ke jikinta sai ‘bari yake fad’i take “muje d’akinka imran tunda manga baya nan a can zan kwana ni da d’akinnan har abada anan matattarar aljannun gidannan suke.” Ammar da yake gefe ya tuntsire da dariya sannan yace “ Hajja rannan fa cewa kika yi kunyi fad’a dasu har kin ‘konasu to yau me yasa kika kasa.” Shiru tayi tana dube-dube “ kai Ammar ka iya bakinka yanzu d’akin nan taf yake da jinnu kafin kaima su dawo kanka muje lmrana” jikinta rawa yake sosai Imran ya fita da ita daga d’akin.
‘Dakin mommah ya nufa da ita da sauri taja tunga ta tsaya “ ina zaka kaini Imran?” Fuska a had’e yace d’akin mommah mana wani abu ne?” Hajja taja baya kafin tace “ma’ana so kake naje d’akin su samu nayi su dagargazani d’akinka zaka kaini dama manga na nan ne sai ba kwana a d’akinsa gobe kuwa jirgin asuba zan bi zuwa garinmu ba zan sake kwana a gidan manga baseries kuyi min bukin na tikitin jirgi.” Ammar yace “kice ba zaki zo bikin bros ba?” Kallonsa tayi sai kuma tayi ‘kwafa ta dam’ki hannun Imran “muje d’akinnaka” Imran ya’bata fuska Kafin yace “ Ni fa hajja ba’a shigar min d’aki ni kad’ai nake amfani dashi for goodness sake ya zanyi dake idan kin so shiga toilet ki dai canja shawara idan ba zaki shiga d’akin mommah ba sai dai a kaiki d’akin amarya” “To kaini can d’in ita ‘yar banza ma ko fitowa ba tayi ba duk wannan budirin da ake.” Shi dai baiyi magana ba ya jata ya kaita part d’in amarya . Yace “sai ki buga mata ni zan tafi na kwanta” ya juya da sauri ta cakumoshi ganin labulai na motsi, tsaki yayi sai kuma ya hau dukan’kofar amarya tana fitowa ya bar hajja yayi saurin fita so yake yaje ya rutsa yarinyar can.


Ko da ya shiga d’akin ganinta yayi kwance akan gadon hajja tana ta tuntsira dariya, ko kad’an bata damu ba da taga ‘kofar d’akin a rufe da key bata da hanyar fita ta san kuma dole goben asirinta zai tonu. Tsit tayi bayan ganinsa a tsaye kamar wanda aka turo fuskarsa a had’e kamar hadarin kaji. Gadon ya’karasa ya janyo jelar gashinta sai gashi ta mi’ke tsaye tsam, fuskarta babu alamar tsoro ko kad’an. Ji yayi kamar ya mammaketa ya ja bakinta ya murd’e duk da taji zafi bata nuna masa ba sai ma ‘bata fuska da tayi “kece aljannar da ke tsorata Hajja kenan to yau asirinki ya tonu kuma sai na gayawa kowa abinda kika aikata har dahda so kike ki kashe masa uwa kenan?” Turo baki tayi tana masa kallon ‘kasa-‘kasa, ba tare da tayi magana ba, ya sake janta ta durgo daga kan gadon sai gata a gabansa, kallon mamaki yake mata ganin yarda sam ba tsoro ko kad’an a tare da ita ya rasa irin yarinyar nan ko dai da gaske tana da ala’ka da jinnu tunda ance rayuwar daji tayi. “Wato ke baki tsorata ma da laifin da kikayi ba, ji yarda kike kallona da idanu kamar na mayu d’auke idonki a kaina before i nock your head, yau a toilet za kiyi spending darenki wuce Muje.” Ta’be baki tayi an gaya masa tana tsoron kwana a toilet ne balle wannan toilet d’in nasu na ‘yan gayu ita tsoronta d’aya kada ya gayawa wannan Almasifatun Babannasu da ko idonsa bata son gani razana ta suke. Ya turata toilet d’in har zai kashe fitila da yake switch d’in a waje yake sai ya fasa ya rufe toilet d’in da key ya fice daga bed room yana mamakin taurin zuciyar shatu.



Da asubar fari yazo ya bud’eta ba don komaiba sai don baya son ya shafawa mommah black paint dole zai bar hajjan a zuwan jinnun gaske ne. Tana barci a kwamin wanka ya sameta hankalinta kwance. Tsayawa yayi yana kallon al’ajabi yarda take barci peacefully a cikin toilet idan shine ai an kasheshi baya jin zai kwana da lafiya. Ya daddage ya d’aka mata duka, ta d’anyi saurin bud’e idonta tana ganin shine ta saki murmushin mugunta don tayi targeting sai ta rama wallahi nan kwana kusa kuwa. Ta zuro’kafafunta ta fita. Shi kuma yabi bayanta. Sai da yaga ta shiga d’akinsu sannan yaja ‘kofar part d’in hajja ya fice masallachi.


Ana idar da sallahr asuba Hajja ta fito main parlour ta zauna, ko tunanin d’aukan kayan ta bata yi ba. Imran yana shigowa daga masallachi yayi arba da ita dariya taso ‘kwace masa sai dai da yake ba ma’abocin dariyar bane sai ya gimtse “ wai meye haka hajja tafiya ba shiri” ya fad’a yana jingina da bango. “ mi’kewa hajja tayi tana gyara sandarta kafin ta sake gyara glass d’in idonta ta kafeshi da ido kafin tace “ko ubanka manga bai isa yace sai na sake kwana a gidannanba aljannu na neman kassarani maza-maza muje ka kaini tashar jirgi.”Ransa a ‘bace ya juya sai kuma yace”ai dai kya yi sallama da mutanen gidan.” Ya shige sashen mommah Hajja tayi saurin bin bayansa “muje ka wani bar ni anan nifa tsoron gidannan nake ji” shatu da take la’be a window ta tuntsire da dariya da sauri hajja ta dam’ki hannun sa “kaji ko wallahi har yau suna gidannan ko baka ji abinda naji ba” hararar shatu yayi tayi saurin sakin labilan. Nahna da take zaune tana azkar ta kalli shatu “ ke lafiyarki kuwa?” Shatu taso bata da labari sai kuma ta gintse tace “zo kiga tsohuwar nan anty nahna zo kiga yarda take rawar d’ari duk tabi ta ma’kal’kale yah Imran” Nanah tace “Allah ya shiryeki shatu ko dai ke kike tsorata ta?” Da sauri shatu ta girgiza kai. Suna kallo su mommah suka rakata su kayi mata sallama.



Kashegari kuwa budurwar Imran ce ta bayyana a gidan tazo hutu a cewarsu wajen uwarta daga abuja fara ‘kal da ita har yellow take sai dai a tsaye take tsam kamar sanda shatu da take jikin window inda ta saba la’be, tana ta kallon yarda Imran yake rawar ‘kafa da budurwarsa ta kuwa ta’kar’kare tace “Muciya da zani” kasancewar parlourn ba hayaniya ba wanda bai ji furucinta ba sai da maganar ta fito tayi saurin toshe bakinta tana kallon Imran da suka yi four eyes da ita ransa a matu’kar ‘bace.....”




To fah! Shatu danger

*🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍



NAZEEFAH SABO NASHE


FREE📚
08033748387
-13


Da sauri shatu ta ruga part d’in mommah, shima Imran yayi saurin mara mata baya, yau kam ba mai hanashi cin kwal uban shatu, a bayan mommah ya ganta tana ta dariya ‘kasa-Kasa, kamar mayunwacin zaki haka ya bita zai cafkota, mommah tayi saurin ri’keta tana furta “kai lafiya uban mai tayi maka?” Cikin ‘bacin rai yace mommah please ki rabu dani in jibgi yarinyar nan, habibteey fa take tsokana wai muciya da zani” dariya ce taso kufcewa mommah tayi saurin rufe baki wanda hakan ya sake ‘kular da Imran yayi kukan kura ya kamota mari lafiyayye ya sauke mata. Da sauri mommah ta janye ta ranta a matu’kar ‘bace “ wai meye haka ne Imran kasheta zaka yi akan wata habibty to wai ma da tace mata muciya da zani sunanta ne? Ko kuwa an canja mata suna ne ta koma muciya ina ce dai ba sunan mutum bane muciya?” Ransa a ‘bace yake sake kallon mommah kafin yayi ‘kwafa wallahi da ita take kuma zaki gane baki da wayo” Mommah ta’kunshe dariyarta ita da nahna da shigowarta kenan tace “a’a Imran kaso kanka sai dai kuma idan tsarguwa kayi ni ban ga abin damuwa ba indai ba habibteeyn taka tayi kama da muciyar da zani bace” Hafsa da Nahna suka tuntsire da dariya. Tsaki Imran yayi ya juya ya fice zuciyarsa cike da sake tsanar shatu.


Bai ganta ba a parlourn hakan ya nuna masa ta shiga sashen mahaifiyarta don haka direct d’akinsa ya nufa yana danna waya nemanta yake, sai dai sai rejecting calls dinsa take.


Ita kuwa tana can zaune fuska a tur’bune tana kallon mahaifiyarta “amma anty wannan yarinyar wacece? A gaban mutane fa ta disgani wai muciya da zani yanzu idan tasa Imran ya ankare da halittata fa ya fasa aurena” zainabu ta girgiza kai “bai isa ba bashi da wannan right d’in baby don na riga Na d’inke zuciyarsa a jikin taki tsaf ba zai ta’ba kallon wata mace bayan ke ba da sunan so” murmushi ta saki “wallahi na yarda da lamarinki anty gashi nan ma yanzu sai kirana yake tun d’azun na tabbata ya kasa sukuni ne”zainabu ta girgiza kai “ba zaki gane irin yarda na tsani Dijah bane saboda ita fa manga ya’ki aurena har an saka rana ta da yana had’uwa da ita yace ya fasa aurena bayan na tabbata ba yin kansa bane tsubbun su na fulani ne ya kamashi” Shaheeda ta girgiza kai “kullum fa anty sai kin bani labarinnan ko hadda ne yaci ace by now nayi haddarsa ni yanzu damuwata ayi a saka ranar nan na kama shi a hannuna ina son Imran to the extent.” Zainab ta dafa ta “shaheedah na sani na san kina son Imran amma fa bana so ki sashi sosai a zuciyarki don bana son lokacin da aikina zai kammala ki kawo min cikas bance kada ki so shiba a’a nafi so ma ki so shi sosai ko bakomai ba ko don dukiyarsa yaci a soshi, duk da kema na san don hakan kike sonsa da bashi da ko sisi ko shine aljannu don kyau ba zaki aureshi ba,aurenki da Imran ba fashi don nima shine burina, sai dai ina da wata manufa mai ‘karfi akan haka kuma kada ki sake ki bijire min a lokacin da bu’kata ta tazo” shaheeda murmushi tayi kafin ta janye jikinta ta mi’ke tsaye ta furta “Allah ya nuna mana lokacin bari inje in gaishe da inlaw ta kada tace bani da kunya.” Zainabu ta had’e a rai a zuciyarta tana tunanin lokacin da zata cimma burinta da ya jima a zuciyarta.


Murya can ‘kasa tayi sallama a ‘kofar parlourn idanunta akan shatu tana jin tsanarta a ranta. Momma ta amsa mata sallamar fuskarta ba yabo ba fallasa su kuwa su nahna ba wanda ma ya kalleta. Sum-sun har ‘kasa ta dur’kusa ta gaida mommah. Amsa mata mommah tayi fuskarta fal fara’a tace “Ya gida ya mutanene gidannaku?” Kanta a ‘kasa tace “lafiya lau” hafsa ta bita da wani kallo a zuciyarta tace munafuka. Shatu kuwa ‘kara ‘kare mata kallo take tana son ganin wani aibu a fuskarta sai dai bata gani d’in ba fuskarta ba yabo ba fallasa tana da kyau dai-dai nata sai dai daga ganin goshinta kasan bata da gashi tsam ta mi’ke “mommah bari na kawo mata ruwa” momma ta gyad’a kai “kin kyauta kuwa mah girl hakan yayi”

Shigowar Imran yayi daidai da kawo mata ruwan da tayi. Yana ganinta yayi saurin had’e rai. Ita kuwa shatu bata ma san yana yi ba ta isa gabanta ta ajiye mata ruwan ta kuma ‘ki yarda ta kalleta ta hau zuba ruwan, da azama Imran ya ri’ke hannunta. “Kwashe ruwan nan ki tashi daga nan kafin nayi ball dake wa yace miki ita ‘kazamace da zata sha ruwanki.” Kallonsa shatu tayi kallon da bata ta’ba yi masa sai taji zuciyarta ta buga bata ta’ba ganin zahirin kyansa ba sai yau da suka yi so close dashi, taushin hannunsa a cikin nata yasa ta zubawa hannayensu ido. Kamar a mintsineshi da sauri ya janye hannunsa, itama shatu hakan ya fargar da ita ta janye idonta da sauri ta mi’ke jikinta a sanyaye tayi hanyar d’akinta. Mommah kuwa ranta ne ya’baci tunaninta haushi shatu taji daji saboda furucin da Imran yayi a Kanta.mi’kewa tayi ita ma ta bi bayan shatunta. A kwance ta ganta akan gadon. Ta zauna a bakin gadon taja ‘kafarta “ Tashi shatun mommah tashi maza kije ku tafi da nahna za tayi miki shopping d’in school.” Da sauri ta mi’ke tana murmushi “mommah yaushe zan fara zuwa?” Mommah tana murmushi tana duban shatu ta lura shatu sam bata da ri’ko shi yasa kullum take cikin walwala ko tunani da wuya ka kama ta tanayi always zuciyarta fresh take as babies hearts. Tana kallonta ta fice da d’an saurinta. Ko da suka fita parlourn tuni suka tarar Imran ya fice da gimbiyar tasa.


Da sassafe shatu tayi shirin school ta fito kenan ta tarar da masu aiki a kitchen hannunsu duk hand gloves da alama uban ‘kyankyamin su ke yiwa girki. Da fara’a ta shiga tana kallon Daniel tace “ shugaban yan girki abincin waye wannan?”cikin gwarancin hausarsa yace “Babyn mommah kayi kyau wow!” Harara ta zuba masa “tambayar da nayi maka kenan?” Daniel yana dariya ta shagala da kallonta yace abincin oga Imran ne” murmushi ta saki tana dubansa ta juya ta shiga store cikin abinda bai fi second biyar ta fito a guje “daniel zo ka fita da ‘bera” daniel ya zaro ido “‘bera kace mai kyau you mean rat?” Tsaki taja “kayi sauri ka tsaya kana surutu sai ya shige wani wajen” yana shiga ta rufo ‘kofar da key “idan ka cireshi ka gaya min sai na bud’e.” Ta bud’e peppe soup ta tara yawu a bakinta ta tottofa ta mayar ta rufe tana dariya, sannan ta ciro wata leda a jakarta ta tsiyaya ruwan cikin shayin dariya take sosai “yau zamu ga ‘karsheb tsafta zaka sha yawuna ka sha kuma ruwan hammata ta.” Da sauri ta bud’e daniel jin Imran na’kwala masa kira.” Kaga ‘Beran?” Ta wurga masa tambayar bayan ta lura yana kallonta “ban ganta ba” ficewa tayi tana cewa “ta gudu kenan bagware wai ban gan taba sai kace ‘beran macece?”



Not edited.....

*🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍



NAZEEFAH SABO NASHE


FREE📚
08033748387
-14



Tun da ta ganshi a parlourn hakan yasa ta zama don taga ko zaici abincin,shi kuwa yana dinning a zaune ya had’a tea ba tare da ya dubeta ba da alama sauri yake don haka da azama ya d’aga cup d’in tea d’in ya kur’ba ya kuma bud’e bowl d’in peppe soup d’in ta zuba a plate ya kai baki yana kur’ba dad’in peppe soup d’in ya ratsa har kwanyarsa ya lumshe ido yana sake zu’ka. Dariyar da shatu ta saka ce yasa shi saurin bud’e idonsa sai kuma ya had’e ransa yana dubanta tana ta she’ka dariya har da tuntsirawa,jikinsa ne ya bashi tabbas akwai dalilin dariyar tata don haka da sauri ya ture plate yace”ke zo nan” tana ‘kunshe baki ta fara

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login